𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum, mallam mijina ya kasance mazinaci kuma ni na tabbatar da hakan kamar yadda sharia ta tanadar, kuma har magani mun karɓa a asibiti sakamakon cututtukan dake samuwa sakamakon haka, na yi hakuri ganin bai rageni da komai ba. na yi tayi masa addu'a shekaru da dama amma ba wani canji, kuma yanzu baya ma kusanta ta. Mallam zai iya neman saki? Meye abinyi a shari'ance?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikis Salaam
Warahmatallahi Wabarkatahu:
Abin da ya kamata shi ne ki
sanar da magabatan ku. Domin kuwa wannan bayanin da kika yi, ba Ƙaramin abu bane. Allah Subhanahu Wa
Ta'ala ya hana yin aure a tsakanin Mazinacin miji da kuma Mace mumina wacce ita
ba ta Zina. Acikin suratun Nuur ayah ta 3 yana cewa;
لَا
يَنْكِحُ إِلَّا زَانِيَةً أَوْ مُشْرِكَةً وَالزَّانِيَةُ لَا يَنْكِحُهَا إِلَّا
زَانٍ أَوْ مُشْرِكٌ ۚ وَحُرِّمَ ذَٰلِكَ عَلَى الْمُؤْمِنِينَ
Mazinãci bã ya aure fãce da
mazinãciya kõ mushirika, kuma mazinãciya bãbu mai auren ta fãce mazinãci kõ
mushiriki. Kuma an haramta wannan a kan mũminai. (suratun Nuur ayah ta 3)
Malaman tafseeri suna kafa
hujjah da wannan ayar cewar aure a tsakanin mazinata da muminai bai halatta ba.
Kuma akwai hatsari mai yawa a gare ki cikin zama da wannan bawan Allah. Domin
kuwa wata rana zai iya zuwa ya kwaso miki H.I.V AIDS ko kuma wata cutar mai
wahalar magani.
Kwanakin baya can da akwai
wadda ta taɓa min irin wannan tambayar Mijinta Zina
yake aikatawa a yanzu haka ya ɗauki H.I.V daman matansa
biyu ne toh ita H.I.V ɗin bai kama ta ba tukuna
amma ɗayan
Matarsa ta kamu, shi ne ta ke neman shawara ya zatayi da zaman Auren ta wai ya
halatta ta nema Saki?
Akwai wata kuma ciwon ya
Riga ya kama ta Amma bai gama yin Karfi a jikin ta ba wai ya zatayi?
Yakamata mata ku gane cewa
indai irin wannan ya faru da mijin ki toh kawai ki nema saki ku rabu matukar ke
ciwon bai kama ki ba idan ya kama ki ne toh yanzu duk ɗaya
kuke sai ki ci gaba da zama da shi a hakan har zuwa ta zo muku, Amma indai ke
ba ki kamu ba toh kiyi gaggawar rabuwa da shi kawai ko Yara nawa kuka Haifa da
shi ku rabu, domin a cikin ku babu wadda ya San waye zai Riga mutuwa, yanzu
idan kema kika kamu da Ciwon sai shi Mijin ya Riga ki mutuwa ko kuma sai ya
sake ki, don Allah ya zakiyi da rayuwar ki kuma ga shi ke karamar Yarinya ce ba
ki wuce wani ya Aure ki ba amma kina ɗauke
da Ciwo wai zai zo ya Aure ki?
Sabida haka matukar Mijin ki
yana harkan Zina a waje Kun yi magana ya ƙi ji
Kun yi Nasiha ya ƙi
ji, kin gayawa Waliyyin sa da Waliyyin ki ya ƙi,
kin gayawa duk wadda za su gaya masa magana ya ji ya ƙi sauraron su toh ko shi ne Ɗan autan Maza kiyi gaggawar rabuwa da
shi, shine yafi dacewa, tunda baya Jin maganar kowa sa'annan ya zaɓi ya
ci gaba Saɓawa Allah akan ya ji maganar kowa toh
kin ga ke a matsayin ki na wadda ba mazinaciya ba Wajibi ne gare ki nema saki
ya sake ki, ki rabu da shi ko Yaran ku sun kai 100 ne ki rabu da shi kawai,
Allah zai kawo miki wani wadda yafi sa wadda za kula da ke da Yaran ki idan
Kuma kin ce a'a ai kina son sa wallahi ba ki son rabuwa da shi ai Uban Yaran
ki, toh lallai kina cikin matsala da tashin hankali sa'annan ke kina goyon
bayan ma ya ci gaba da Saɓawa Allah ɗin
kenan.
Sa'annan kuma kowacce mace
burin ta shine Uban 'ya'yan ta ya zamto mai kyawun halaye Da tarbiyya yadda zai
zama abin alfahari a wajen 'Ya'yan sa. Amma ya kamata lallai ki zauna tare da
waliyyan auren ku ki bayyana musu halin da kike ciki sannan su kuma su tunkare
shi da maganar ki sanarwa manyansa na, sannan ayi masa nasiha, Wa'azi,
tunatarwa, Idan ya yarda ya tuba ya chanja halayen sa, toh shikenan sai ku ci
gaba zaman Auren ku.
Amma idan ya ƙi yarda, ko yayi tawaye, toh mafi
alkhairi a gare ki shine a raba auren kawai kada ki damu da maganar wasu Cewa
ai tunda ba ke kike aikatawa ba ina ruwan ki ai laifin shi ya shafa ke Ina
ruwanki ki bar shi yayi abun da yake so tunda ya ƙi,
toh kawai ki ce tunda ya ƙi ke
kuma ba za ki zauna da wadda baya Jin maganar iyayensa ko Manyan sa ko Waliyyin
sa tare da saɓawa Allah ba kawai ya Sake ki. Idan ba
haka ba, zai iya sanya ke ma ki kauce hanya idan ba Allah ne ya kiyaye ba.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.