Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Saurayin Da Yake Kama Maman Budurwarsa

TAMBAYA

Assalamu alaikum malam fatan an yini lafiya ya gida ya aiki, dan Allah malam ina da tambaya, ina da saurayi to sai yake min wasu abubuwa tun ba na so har ya kai nima ya saba min, idan ya zo gurina sai ya dinga kama min mama na ko ya dinga sanya gaban sa cikin gabana na yi masa faɗa yaƙi dainawa har ta kai ya yi min ba adadi, shin malam wannan mijin aure ne ko ba mijin aure ba? Na gode Allah saka da alheri kuma a ja hankalin ƴan uwa na Mata saboda dayawa suna aikata haka.

AMSA

Wa alaikum salam warahamatullahi wabarkatuhu lafiya lau alhamdulilah, to da farko dai ƴar uwa kin zubar da ƙimar ki kuma ki sani cewa ba ko wani na miji ba ne zai iya auren ki idan kika bashi kanki ya sanki a ya Mace ba ta hanyar aure ba koda ya aure ki ba zai ɗauke ki da daraja ba kullum yana cikin zargin ki da kuma tuhumar ki.

Duk namijin da ya miki haka to ba ke yake so ba da yana son ki ba zai so ya miki haka ba kuma ki sani kinyi babba kuskure da kika yardar masa.

Duk na miji da zai dinga miki maganar da ki yarda koda malami ne ko ustaz ya dinga jayo miki wasu ayoyin sa wanda zai rude ki ko ya ce zai miki fushi idan baki yarda ba to wallahi kar ki yarda kaf Alkur'ani babu inda aka hallata hakan kuma hukuncin ku kamar kun aika zina kuyi saurin tuba zuwa ga Allah.

Kuma ki sani duk na mijin da ya aure ki zai gane sn kwanta da ke.

Allah a cikin littafinsa mai tsarki yana cewa:" Kuma kada ku kusanci zina. Lalle ne ita ta kasance alfãsha ce kuma tã mũnãna ga zama hanya."

Suratul Isra'i aya ta 34 zuwa 35 safaha ta 285

Kuma mu sani alƙawari ne Allah ya yi duk wanda ya yi zina to zai auri Mace daidai dashi wadda ita ma haka take yi.

Kamar yadda Allah yake faɗa a cikin Alkur'ani mai girma:" " Mazinãci bã ya aure fãce da mazinãciya kõ mushirika, kuma mazinãciya bãbu mai aurenta fãce mazinãci kõ mushiriki. Kuma an haramta wannan a kan mũminai."

Suratul Noor aya ta 3 zuwa ta 4.

Wannan ayar ta zamo mana izina a gare mu domin duk wanda ya aika zina da ƴar wani ya sani fah ba Allah ya yi ma wayo ba shi ma Allah zai haɗa shi da daidai dashi.

Kuma mu sani duk wanda yake aikata munana kamar zina to shi ma Allah ya yanke masa hukumcinsa ga wanda zai rayu dashi tun nan duniya domin ba a yi ma Allah wayo a cikin Suratul Noor aya ta 26 zuwa ta 27

" Miyãgun mãtã dõmin miyagun maza suke, kuma miyãgun maza dõmin miyãgun mãtã suke kuma tsarkãkan mãtã dõmin tsarkãkan maza suke kuma tsarkãkan maza dõmin tsarkãkan mãtã suke...."

Duk wani wanda ya aika zina to ya tuba idan har ba a yi masa hukunci anan gidan duniya ba idan yaje Allah zai yi masa nasa.

Hukuncin abin da kuke yi kamar zina kuka yi

Abin da kuka yi tun da har yana sanya gaban sa cikin gaban ki to wannan kamar zina ce kuka aika ta kuma hukuncin wanda bai da aure shi ne bulala 100 kamar yadda ya zo cikin Alkur'ani mai girma:" Mazinãciya da mazinãci, to, ku yi bũlãla ga kõwane ɗaya daga gare su, bũlãla ɗari 100. Kuma kada tausayi ya kãma ku game da su a cikin addinin Allah idan kun kasance kunã yin ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira. Kuma wani yankin jama, a daga mũminai, su halarci azãbarsu."

Suratul Noor aya ta 2 zuwa ta 3

Wannan hukunci ne da Allah ya yanke shi idan har ana yin sa to za a yi musu wannan hukuncin su duka kuma a kora su daga garin saboda kar su lalata wasu.

Amma wanda suke da aure to jefe su za a yi har sai sun mutu idan aka musu rangwame kuma to Allah zai yanke musu nasu hukuncin.

Jan hankali na ga yan uwa🦻👂

Kada sha'awar ka tasa ka aikata zina da ƴar wani haka kema kada son ranki da rudin shaidan ya sa ki aikata wannan ɓarnar.

Kuma ki sani ke uwar wasu ce kuma za ki haifa haka kaima uba ne ga wasu dan haka kada ka yi nadama daga baya idan ka haifi ƴaƴa suka zamo suna da irin halin ka.

Allah ya kare mana imanin mu ya kuma tsare mu baki ɗaya.

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments