Citation: Abba Bala FAGGE & Maimuna Iyal SADA (2018). Wasu Hanyoyin Bunƙasar Wasu Garuruwan Hausa Jiya Da Yau. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. 6. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
WASU HANYOYIN BUNƘASAR WASU GARURUWAN HAUSA JIYA DA YAU
Abba Bala FAGGE
Da
Maimuna Iyal SADA
TSAKURE
Wannan maƙala mai taken “Wasu
Hanyoyin Bunƙasar Wasu Garuruwan Hausa Jiya da Yau”, kamar
yadda sunan ya nuna, bincike ne da ya yi magana a kan ƙasar Hausa da yanayinta da ma asalin Hausawa, da kuma irin yadda
wasu daga cikin garuruwan ƙasar suka kafu, suka bunƙasa ta hanyar wasu ginshiƙan abubuwa da suka haɗa da; noma da fatauci da yaƙe-yaƙe da nema ko yaɗa ilimi da sauransu. Har
wa yau, an kuma bayyana irin bunƙasar da ƙasar ta yi a yau sakamakon bin waɗancan hanyoyi na farko-farko da al’ummar suka yi.
1.1 Gabatarwa
Babu shakka, batu na bunƙasar garuruwan ƙasar Hausa, abu ne mai
faɗin gaske da ya ƙunshi abubuwa daban-daban, sai dai wannan bincike ya tsakuro irin
abin nan da akan ce, ‘a sa a baka…’, domin haskawa tare da fito da muhimman
abubuwa yadda za a fahimta. Don haka, wannan takarda za ta kalli ƙasar Hausa da yanayin ƙasar Hausa da kuma
tarihin Kano da Daura da kuma Damagaram a taƙaice. Sa’annan za a dubi
yanayin bunƙasar garuruwan ƙasar Hausa jiya da yau.
Amma da yake wannan takarda za ta yi ratse ne
wajen kawo tarihin kafuwar wasu garuruwa da yadda za a fahimci bunƙasar garuruwa ƙasar Hausa, don haka, za
a yi wa tarihin shigar shantun ƙadangare ne.
Ma’ana, ɗan lasawa kawai za a yi, domin a samu damar
fahimtar yadda garuruwan ƙasar Hausar suka ɓankasa ta hanyar kafuwarsu.
Ƙamusun Hausa (2006, sh. 58) ya bayyana ma’anar bunƙasa da “Gawurta ko Ƙasaita”. Haka kuma, ya kawo ma’anar garuruwa da “Wurin
da mutane suke zauna suka yi gidaje”, (CNHN, 2006, sh. 159) har
wa yau an kawo ma’anar ƙasa da “Wani yankin duniya wanda hakuma
guda ke mulki”, (CNHN, 2006, sh. 278).
1.2 Ƙasar Hausa
An ce gidan Hausawa na gado shi ne Arewacin
Nijeriya, da kudancin Jamhuriyar Nijar. “An tabbatar a cikin tarihi akwai wani
lokaci da mutane suka yi ta yin ƙaurace-ƙaurace daga yankin takin Chadi suna yin yamma. Babban dalilin yin
waɗannan ƙaurace-ƙaurace shi ne, ƙeƙashewar tafkin Chadi. Gulbin Kebbi shi ne maƙurar wannan ƙaura a sashin yamma. Tsakanin gulbin Kebbi da
tafkin Chadi akwai nisa ƙwari, kuma akwai makekiyar ƙasa.
A lokacin ƙaurace-ƙauracen waɗansu mutane sun ƙarasa har gulbin Kebbi, waɗansu kuwa, iyakarsu
tsaunukan ƙasar Borno. Mafiya yawan mutane, sun watsu ne a
wurare daban-daban cikin wannan makekiyar ƙasa. Haka kuma, mutanen
sun daɗe ƙwarai a wannan
makekiyar ƙasa, yadda har ma ba a san tun lokacin da suka
zo ba. Ba a san su sosai ba, sai ƙarshen ƙarni na sha biyar. Bugu da ƙari, mutanen ƙabilu ne daban-daban, Hausawa da Bolawa da Ngizim da Margi da Buduma da Ƙotoko, su ne manya daga
cikin ƙabilun. Daga manyan ƙabilun, Hausawa sun fi yawa sun fi warwatsuwa cikin wannan
makekiyar ƙasa.
Ƙasar Hausa tana da girma ƙwarai da gaske. A miƙe, daga Arewa zuwa kudu, ƙasar Hausa ta fara daga
Azbin har i zuwa kusurwar Arewa maso gabas ta tsaunukan ƙasar Jos. Daga nan sai ta kwasa ta yi yamma har i zuwa inda kogin
Kaduna ya yi wani dabban doro. Daga nan kuma sai ta buga ta yi arewa maso yamma
sai da ta dangana da wani ƙaton kwari na galbin Kebbi. Daga wannan wuri,
sai ta karkata ta nufi arewa maso gabas har Azben. Wannan zagaye shi ya nuna
iyakokin ƙasar Hausa a gabas da yamma da kudu da
arewa. Ƙasar da waɗannan iyakoki suka
iyakace ita ce ƙasar Hausa har i zuwa yau, wannan ƙasa, wato ƙasar Hausa, ita ce mazaunin Hausawa (Amfani:
2011, sh. 2).
1.2.1 Yanayin Ƙasar Hausa
Ƙasar Hausa, buɗaɗɗiyar ƙasa ce shimfiɗaɗɗiya mai albarka noma,
tsawonta da faɗinta. Ba ta da wasu matsolalin yanayin ƙasa, irin su girgizar ƙasa, ko zaizayarta ko
ambaliyar ruwa da dazuzzuka masu duhu ko manya-manyan duwatsu masu aman wuta,
ko koguna waɗanda suka yi mata shinge ko suka rarratsa ta, ta
yadda zirga-zirgar jama’a za ta yi wahala (Adamu, 2011, sh. 68).
Babu shakka, idan aka kalli waɗannan bayanai da aka tsakuro daga masana, dangane da ƙasar Hausa da yanayinta, za a tabbata da cewa, lallai ƙasar Hausa na da faɗin gaske, musamman idan
aka duba yadda ta kwakwaso wani yanki na jamhuriyar Nijir ta haɗa da wani yanki na Nijeriya.
1.3 Asalin Hausawa
Asalin Hausawa wani batu ne da yake nema ya
gagari-kwandila, bisa la’akari da yadda masana da manazarta Hausawa da
harshensu ke ta ƙarakaina wajen daddagewa don tabbatar da inda
Hausawa suka ɓullo. Kaɗan daga cikin masana da
manazarta ra’ayoyin asalin Hausawa sun haɗa da Malam Aminu Kano
da Ɗanmasanin Kano, a cikin Yusuf (2010, sh. 4) da
Adam (1997, sh. 20) da Adam, (2011, sh. 66) da sauran su.
Don haka batu na asalin Hausawa, idan aka bibiyi
masana mabambanta ra’ayi, aka kuma tattara hankali wuri guda, za a fahimci
cewa, kawai karafkiya ake ta yi ta fuskar tarihi, don har zuwa yanzu babu wani
abu guda ɗaya a matsayin alƙibla da aka kalla ko aka
tafi a kai dangane da asalin. Kenan kamar ƙowace al’umma da
asalinta, sai dai a yi ta lalube cikin dahu, don buƙatar neman dacewa. Ko kuma a tattara abin kacokan a ce asalin
Hausawa shi ne, ‘Tun ran gini tun ran zane’ (Fagge, 1999, sh. 15ƙ.
1.4 Garuruwan Ƙasar Hausa
A nan kamar yadda bayanai suka gabata, ƙasar Hausa ta haɗa da wani yanki na Najeriya (Arewa), da kuma na
Jamhuriyar Nijar (kudu maso gabas). Kenan yankin ƙasa biyu ne suka haɗu suka samar da
garuruwan. Waɗansu daga cikin garuruwan kuwa sun haɗa da:
|
(GƘH)
a Nijeriya (Arewa) |
(GƘH)
a Nijar (Kudu maso Gabas) |
|
Daura |
Damagaram |
|
Kano |
Maraɗi |
|
Zazzau |
Ƙwanni |
|
Katsina |
Tasawa |
|
Kebbi |
Mada-rumfa |
|
Yawuri |
da
sauransu |
|
Gobir |
|
|
da
sauransu |
(Adamu, 2007).
1.4.1 Kano
Idan ana so a naƙalci tarihin Kano, dole
ne sai an taɓo tarihi ƙasar Hausa. Shi kuwa
tarihin ƙasar Hausa sai an leƙa cikin tarihin Sudan. Shi kuwa tarihin Sudan sai an lelleƙa cikin tarihin daular Larabawa ta Banu Ummayyata da ta Banu
Abbasi. Har ila yau kuma, da binciken labarin wani tunzuri da ya sa jama’a suka
riƙa ƙauratowa daga tsakiyar ƙasar Asiya suka yo yamma. (Dokaji, 2002, sh. 1).
A ƙarshen ƙarni na tara (Ƙ-9) na masihiyya, waɗansu maharba waɗannan babu haƙiƙar daga inda suka fito sosai, amma dai daga wajen arewa suke, suka
zauna kan duwatsun da ke kewaye da sararin da ake kira Kano a yanzu. Irin
duwatsun nan su ne irin su Dala da Gwauron duste da Magwan da dutsen Fanisau.
Waɗannan mutane dai maharba
ne, wanda a nan suka riƙa yin farauta a wani kurmi wanda yake shi ne
tushen rafin Jakara, inda kasuwar Kurmi ta Kano ta samo suna. Da waɗannan maharba suka jarraba ɗan noma suka ga wurin ya
yi albarka, sai suka ci gaba suna ƙara saran dajin suna yin
gonaki. Albarkar wurin nan mai ban-mamaki sai ta jawo waɗansu mutane daga waɗansu wurare suna zuwa.
Da taron mutanen ya fara yawa, sai suka yi shugaba, wanda a bisa al’adar
mutanen, wannan lokacin mai nisa, yakan zama mutum ne da ke da fifikon ƙarfi game da tsafi.
Babu tahaƙiƙanin akan irin tsarin mulkin da waɗanan al’umma suka gina
shugabancinsu, amma duk da haka ana iya cewa, aikin shugaba a wannan lokaci bai
wuce tsare dakokin farauta da kuma kusaci da tsafin da mutanen ke bautawa ba
(Dokaji, 1958, sh. 5).
Shi kuwa Malam Aminu Kano, (1983, sh. 26) cewa
ya yi, “Birnin Kano gari ne da ya samo sunansa daga wani mutum wai shi
Kano. Wani lokaci kuma ana yi masa laƙabi da suna Dala”. Iyakacin bincike ya nuna cewa, a lalace an yi
shekara dubu da fara gina birnin Kano. Sannu sannu ya ƙasaita a kan sana’o’i huɗu da suka haɗa da; ƙira da rini da sassaƙa da kuma gini.
Daga nan, sai kasuwanni suka tashi. Cikin waɗannan kasuwanni sai aka
samu babbbarsu wadda ake kira ‘Kasuwar Kurmi’. A kusa da kusawar akwai wani
tafkin jakara inda ake kaman kifi, kuma ake bikin, al’ada na shekara-shekara.
Wajen rini kuma ta yi suna ainun, har ana yi wa Bakano kirari da; ‘Bakano
bakan riɗi, da rana kana karofi da daddare kana dandali’. Kuma shi birnin ana yi masa kirari da
cewa ‘Jalla babbar Hausa. Kano ko da me ka zo an fika, Kano ganin Dala
ba shiga birni ba, Kano tumbin giwa’. (Adamu, 2007).
Bugu da ƙari, Kano tana da ƙafofi guda goma sha biyu, kowace kofa tana da ƙyauren ƙarfe da ake rufewa in dare ya yi, kuma kowacce
tana da sarki da ɗan ɗakinsa, don kula da
shige da fice na mutane. Yana iya tsayar da kowa ya tambaye shi, in ya ga
alamar rashin gaskiya game da shi. Wani abin sha’awa kuma shi ne, kowa ya shigo
sai ya taɓa bangon ƙofar. Wannan shaida ce
ta duk wanda ya shigo birnin Kano ya tsira, kowane abu ne kuwa ya koro shi….”
(Adamu, 2007).
Da tafiya ta yi tafiya, har zuwa lokacin da aka
samu jaddada Musulunci, wato lokacin Shehu Usman Ɗanfodiyo. A lokacin ne Fulani suka riƙa tumɓuke sarakunan maguzawa suna kakkafa nasu mulkin
daga wannan lardi zuwa wancan, wannan ya taimaka ƙawai da gaske wajen sauya salon tafiyar ƙasar Hausa.
A ƙarƙashin mulkin Fulani, baya ga gidajen sarautar Bagauda da Rumfa da
kuma Kutumbi, akwai:
1. Sarkin Kano Sulaiman
2. Sarkin Kano Dabo
3. Sarkin Kano Usmanu
4. Sarkin Kano Abdullahi
5. Sarkin Kano Bello
6. Sarkin Kano Tukur
7. Sarkin Kano Alu
(Dokaji, 1958, sh. 33-65)
Sarakunan Fulani zamnin Turawa kuwa su ne:
8. Sarkin Kano Abbas
9. Sarkin Kano Usman
10. Sarkin Kano Bayero
11. Sarkin Kano Sanusi
12. Sarkin Kano Ado
(Dokaji, 1958, sh.
66-82)
Wannan tarihi na kafuwar Kano da aka
tsattsakuro, ko daga nan aka dakata, za a fahimci cewa yana ƙunshe da abubuwa da daman gaske, waɗanda kuma za su taimaka
wajen haskakawa don gano bakin zaren inda aka gaba dangane da bunƙasar ƙasar Hausa. Alal misali, a ciki an yi
maganar ƙaura da noma da sana’o’i. da sauransu.
1.4.2 Garin Daura
Daura wani gari ne mai tarihi kuma ɗaya daga cikin garuruwan ƙasar Hausa. Mutanen da
ke cikinsa Hausawa ne kuma kamar sauran ‘yan uwansu Hausawa babu wanda zai ce
ga daga inda suka fito. Ko da yake dai wani marubuci mai suna Isma’il Tsiga a
littafinsa Sarauniya Daurama ya ambaci cewa, wai “Asalin
mutanen da suka fara zama a Daura Falastinawa ne, waɗanda suke da kaka wai shi Najib. Haka kuma shi Najib ɗin yana da wani ɗa wai shi Abdulƙadir wanda ya baro gida Falastinu ya dawo Libayya da zama, daga
nan kuma ya sake ƙaura ya koma wani gari wai shi Tarabulus
(Tripoli). Bayan ya ɗan zauna kaɗan, sai kuma ya yi fushi ya nufo kudu, bai zame ko’ina ba sai da
ya iso tsohon Birni wato Daura, bayan ya sami ‘yar makwantar ruwa wadde ake
kira Kusugu...”.
Abin da dai masana tarihi suka fi ambata shi ne,
kasancewar mutane a tsohon Birni tun da daɗewa, kuma sun samu ci
gaban rayuwarsu da yadda ake yin sarauta. Ga kuma sana’o’i kamar su noma da
kiwo da farauta, sai dai kawai suna fuskantar matsala rashin ruwa, domin kuwa
an ce sukan haƙa rijiya gaba hamsin zuwa tamanin ko fiye kafin
a tarar da ruwa, wani zubin ma ba a samu sam-sam. Saboda haka, an ce an haƙa rjiyoyi fiye da dubu uku (3,000) a garin don neman ruwa a wancan
lokacin.
A bisa tsarin rayuwar wanan gari, mata ne ke yin
sarauta ba maza ba, kuma duk matar da ta ci sa’a ta yi sarauta ana kiran ta
“Magajiya” sannan an ce wai tun mace na da shekara goma ake ganewa idan za ta
yi sarauta. Saboda haka idan an gane da haka, to ba a ƙara barin ta ta fita ko ƙofa, sai dai a ajiye ta
cikin gida a yi mata wasu al’adu da ba za ta yi sha’awar namiji ba. Kuma
tana ƙara girma ana ƙara yi mata abubuwan al’adun ta yadda har idan ta balaga za ta yi
ta cuɗanya da maza amma ko kusa sha’awarta ba ta kai
gare su ba, don haka babu maganar aure kenan a kowace sarauniya sam-sam.
Kuma a tsarin mazauna wannan gari bisa al’ada
Sarauniya ba ta yin shari’a, sai dai akan naɗa Sarki wanda kan yanke
hukunci bisa izinin Magajiya. Amma a inda aka gane bai yi gaskiya ba, to sai a
cire shi a naɗa wani.
Idan muka lura sosai sai mu ga cewa mutane sun
daɗe zaune a tsohon Birni, har ma sun samu hanyar
ci gaban rayuwarsu ta yadda ake yin sarauta. Kuma ma abin ba a nan kawai ya
tsaya ba, domin kuwa tarihi ya nuna cewa an sami Sarauniyoyi tara waɗanda suka yi mulkin Daura kafin Sauraniya Daurama, ga jerin
sunayensu kamar haka:
1. Yakuno 6. Katsinta
2. Gafari 7. Yakaso
3. Wawaina 8. Gidirgidir
4. Yakanya 9. Wahazama
5. Indari 10. Daurama
Magajiya Daurama dai ita ce Sarauniya ta goma.
Kuma ta ƙarshe a tsarin Sarautar Mata a Daura, domin kuwa
daga kan ta maza suka karɓa har zuwa yau. (Adamu, 1997, sh. 29-30)
1.4.3 Garin Damagaram
Tarihin Damagaram ya fara ne, daga wani Shehun
Malami, wanda ya fito daga ƙabilar Dagirawa, kuma ya
yi zaman ɗalibta a Birnin Ngazargamu. Bayan da ya ƙoshi da karatu, sai ya nemi izini wajen Sarkin Borno mai Dunama,
don shi ma ya fara yin wa’azin addinin Musulunci a ƙasar tasa. Da ya zo ƙasarsa sai ya fara
wa’azi daga wannan gari zuwa wannan gari. Da haka ya samu mabiya a cikin ƙabilun Azbinawa da Dagirawa da Barebari da Hausawa.
Da wa'azinsa ya ɗaukaka mabiyansa suka yi yawa, sai suka taru suka nacfa shi
Sarkinsu. An yi wannan abu watakila a wajan hijira ta 1736, kuma garin da
malamin ya kafa na asali shi ne ‘Damagaran ta Kaya’. Saboda haka masarautar
Damagaran ta farko ita ce 'Damagaran ta Ƙaya'. Bayan da Malamin
ya rasu, sai 'ya'yansa da jikokinsa suka ci gaba da sarauta, to amma ba su iya
samun damar faɗaɗa mulkinsu ba, har sai
da wani jikan malamin mai suna Sulaiman ya hau gadon sarauta, a wajen hijira ta
1812 (December, 1971).
A lokacin da Sarkin
Damagaran Sulaiman na farko ya hau gadon sarauta a Damagaran ta Kaya daga
(1812-1822), sannan tuni jihadin Fulani na Shehu Usmanu ya yaɗu a duk ƙasashen Hausa. Tashin wannan yaki na jihadi ya
ba sarki Sulaiman damar faɗaɗa daular Damagaran, don
kuwa ya kawo wa Damagarawa ƙarin ƙarfi da arziki, Farkon abin da sarki Sulaiman ya yi shi ne, tara
yaki ya ci wani gari na Maguzawa da ake kira Zinder. Sulaiman ya ci zinder, ya
kashe shugaban ƙauyen mai suna ‘Zandarma’, kuma har'ila yau
ya ɗauko kujerar mulkinsa daga Damagaran ta Ƙaya ya maido ta Zinder, inda ya gina gidan sarautar Damagaran na
yanzu. A Damagaran ta Ƙaya kuma, sai sarki Sulaiman ya naɗa wani wansa wai shi Maida ‘Yakudiman Damagaran’ ya kai shi can
don tunawa da asali.
Sarkin Damagaran
Sulaiman ya zo Zinder a sa'a, da ma kuwa, garin yana gefen inda Fulani suke
yaki, kuma bugu da ƙari, Zinder Mahaɗa ce ta fataken da ke
kaiwa da komowa, ta ciniki tsakanin Kano da Tripoli. Cikin shekaru goma da
sarki Sulaiman ya yi yana sarautar Damagaran, ƙasar Damagaran ta bunƙasa saboda dalilai biyu.
i.Da yaƙin Fulani ya tashi, sai suka cinye ƙasar Katsina, da Kano da Daura. In ban da sarkin Kano duk
sarakunan waɗannan ƙasashe da suka gudu daga
yaƙin Fulani, ƙasar Damagaran suka je, inda Sulaiman ya ba su
gurin fakewa. Mabiyan waɗannan sarakuna na Ha6e, da kuma sauran talakawa
da ba su yarda da jihadin Fulani ba, duka Damagaran suka tafi, don kuwa can ne
aka karbe su. Wannan juyi ya jawo wa Damagaran ƙarin mutane, da kafa ƙauyuka sababbi. Da yake
Haɓe mutane ne masu zafin nama wajen noma da
sana'a, nan da nan sai gonaki suka ƙaru a ƙasar Damagaran, kuma masana'antu iri-iri na Hausawa, su rini da
jima da ƙira da sassaka da shauransu suma suka yaɗu.
ii.Da Fulani suka ci Katsina sai Maracfi taƙi bin su, saboda haka yaƙi ya ci gaba tsakanin
Maraɗawa da Fulanin Katsina da na Sakkwato. Waɗannan yake-yake sun kawo rashin kwanciyar hankali ga fataken da
suke kawo kayan ciniki daga Tripoli zuwa Katsina. Saboda haka, sai hanyar
ciniki wadde ake bi ta Tasawa zuwa Katsina sannan Kano, ta mutu. Daga nan sai
aka buɗe sabuwar hanya daga Tripoli zuwa Zinder zuwa
Kano. To fa a sakamakon wannan hali ne Zinder ta ƙasaita ta zama zangon fatake, kuma kasuwa ta biyu bayan Kano. Da
samun wannan nasara ne sarkin Damagaran Sulaimanu ya rasu a shekarar (1822).
Bayan rasuwar Sulaimanu sai 'ya'yansa guda biyu, waɗanda suka gaje shi, sarkin Damagaran Ibrahim (1822-1846-1854) da
kuma sarki Tanimu (1854-1884), suka ci gaba da wannan ruhi na faɗaɗa ƙasar Damagaran, har
suka ƙarasa daular nan ta Tsotse-bakin-ka wadda ita ma
Bamo take bi, kamar Damagaran. Har ila yau dai, su ne suka share fagen yaƙi da Kano don su ƙwace mata abin da Allah
ya ba ta na arziki.
Wasu daga
garuruwan sun ƙunshi wurare kamar haka:
1 Mirya 9 Muwa
2 Dakusa 10 Gidimoni
3 Wame 11 Dogo
4 Damagaran ta Ƙaya 12 Durum
5 Babban Tafki 13 Zarmu
6 Hamdara 14 Gafati
7 Tirmini 15 Albarakarim
8 Guma (Adamu, 2007, sh. 3-6).
1.5 Wasu Matakan Bunƙasar Wasu Garuruwan
Hausa
Masu iya magana kan ce,
‘hannu ɗaya ba ya ɗaukar jinka’,
don haka ma hankali ya yarda da, ‘karfe ɗaya ba ya amo’. Kenan,
idan batun bunƙasar ƙasa ko wani gari ake yi,
dole ne sai an samu dunƙulalliyar al'umma a ƙarƙashin kyakkyawan shugabanci da jajircewa da
kishi da taimakekeniya a tsakaninsu, domin samun ci gaba, kuma kowa yana da
irin rawar da zai iya takawa, har a cim ma gaci.
Game da wasu matakai na
bunƙasar wasu garuruwa na ƙasar Hausa akwai:
a. Nona
b. Sana’o’i
c. Fatauci
d. Neman Ilimi da Bayar da shi
e. Ƙaura
f. Yaƙe-yaƙe (da Jihadi)
g. Shigowar baƙin al’ummu
Waɗannan abubuwa su suka haɓaka garuruwan ƙasar Hausa, ta faɗaɗa har i zuwa wasu
yankuna na kusa da na nesa da ita. Bari mu kalli kowannensu a takince.
1.5.1 Noma
Noma abu ne mai asali da
tushe, wanda har masu hikima kan yi masa kirari da “na duƙe tsohon ciniki, kowa ya zo duniya kai ya taras”. A wannan gaɓa, ƙasar Hausa ta shahara ƙwarai da aniya. Don haka, “Allah ya albarkaci ƙasar Hausa da wadatar ƙasa ta noma da karɓar iri, tana kuma da bishiyoyi da ma’adanai iri daban-daban. Shi
ya sa ma wani Bature mai suna Dr. Barth ya bayyana cewa, ya ga abin mamaki a
lokacin da ya taho daga Tasawa ya biyo ta Katsina ya nufo Kano a cikin shekarar
(1850) ya kuma ƙara da cewa, “noma shi ne jigon tattalin
arzikin ƙasar Hausa...”(Adamu, 1997, sh. 14). Kenan noma a ƙasar Hausa, tamkar jinin jikin al’ummar wannan yanki ne, wanda
kuma ya bunƙasa su, ya ɗaukaka darajarsu a idon
duniya har aka san su, (a wancan lokaci).
1.5.2 Sana'o'i:
Ƙo a tarihi an tabbatar da cewa, al'ummar ƙasar Hausa ba ragwaye ba ne, jajirtattu ne wajen neman na kai.
Alal misali, a cikin garurawan ƙasar Hausa, idan
aka ɗauki garin Kano, iyakacin bincike ya nuna cewa,
“A lalace an yi shekara dubu (1,000) da fara gina birnin Kano, sannu sannu,
ya kasaita a kan sana’o'i nau'i huɗu, wato ƙira da rini da sassaƙa da kuma gini. Daga nan
sai waɗannan suka haifi kasuwanci da ciniki, nan da nan
sai kasuwanni suka tashi. Cikin waɗannan kasuwanni sai aka
samu babbarsu wadda ake kira kasuwar kurmi...” Aminu Kano (1983, sh. 25). Ko da wannan
misali za a fahimci yadda sana’o’i suka taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa garuruwan ƙasar Hausa.
1.5.3 Fatauci:
“Hausawa kusan sun
yawace ko’ina wajen fatauci da ci-rani zuwa ƙasashen Afirka baƙar fata. Kuma duk inda matafiyan nan suka je, sukan zauna a
unguwar Hausawa ne wato ‘zango’. Ba sa daina magana da harshensu, ba sa barin
tufafmsu da al’adunsu na gargajiya. Sukan auri matan ƙasar da suka je, amma ba su cika bayar da ‘ya’yansu mata ga
mutanen ƙasar ba. Kuma duk abin da ya kama na taimako
a ƙasar suna shiga, don haka ba a cika tashin
hankali da su ba.Wannan ta sanya ma akan yi sha'awarsu” (Adamu, 1997, sh. 15).
Shi ma wannan jigo ne na haɓakar garuruwan ƙasar Hausa, musamman idan aka yi la’akari da yadda Hausawa yayin
fatauci suke auratayya tare da kiyaye al’adunsu (suturarsu da abincinsu da
harshensu d.s) da taimakon juna da ma bare, wannan ba ƙaramin taimakawa ya yi ba wajen bunƙasa yaɗuwarsu da ɗaga darajarsu.
1.5.4 Ƙaura:
An samu ƙaurace-ƙaurace daga nan zuwa can, wanda ya haifar da
barbazuwar al’ummar Hausawa, Dalilan waɗannan ƙaurace-ƙaurace kuwa, a iya cewa neman ilimi ko yaɗa shi, ko sanadiyyar yaƙi ko kore mutane su bar
inda suke, musamman idan ba su yarda da wani abu ba kamar yadda aka samu haka
lokacin zuwan Turawan mulkin mallaka Misali, sarkin Zazzau Aliyu Ɗansidi da sarkin Kano Alu Maisango. d.s. Haka ma lokacin jihadin
Shehu.
1.5.5 Yaƙe-yaƙe:
A da garuruwan ƙasar Hausa, garuruwa ne da suke fama da yaƙe-yaƙe a tsakaninsu ta yadda wani gari zai taso
rundunarsa domin murƙushe wani. Don haka ne ma za a taras duk garin
da aka je suna da ganuwa ko badala da ƙofofi domin tabbatar da tsaro. Alal misali: Sarautar Zazzau ita ce
sarautar Aminatu ɗiyar Sarkin Zazzau, ta yi yaƙi da yawa cikin garuruwa har Kano da Katsina suka bi ta....” NNPC
(1970, sh. 5) Waɗannan yaƙe-yaƙe da garuruwan ƙasar Hausa suka riƙa yi, ba sun tsaya ba ne kawai a tsakaninsu, hatta ƙananan garuruwa na wasu ƙabilun suka rika
mamayewa. Har wa yau, Jaddada Musulunci lokacin Shehu Usman Ɗanfodiyo ba abin mantawa ba ne, wanda wannan ma ya taimaka wajen
bunƙasar ƙasar Hausa.
1.5.6 Nema/Yaɗa Ilimi:
Shi ma wannan babban
jigo ne wajen bunƙasar garuruwan ƙasar Hausa, musamman idan aka kalli yadda jihadin Shehu Usman
Danfodiyo ya wakana, na ƙoƙarin canza
garuruwan ƙasar Hausa, zuwa hanya madaidaiciya (addinin
musulunci). Haka kuma da ƙoƙarin yaɗa ilimin. don ɗora mutane a kan hanyar
nemansa. Wannan ta sa ƙasar Hausa ta samu matsayi da ɗaukaka.
Wannan matsayi na ƙasar Hausa ya bai wa Hausawa wasu fa’idoji masu albarka, a gare
su, kamar haka:
·
Na farko, samun damar
walawar cinikin gida da na fatauci a waje, da hulɗa da jama'a iri
daban-daban.
·
Na biyu, tsarkakkakiyar
zuciya daga aƙidar bambancin ƙabila, da ƙabilanci na girman kai.
·
Na uku, saurin karɓar sabon ra’ayi da sababbin dabaru masu amfani ga jama’a, wannan
ita ce ta ba su wayewar kai da karɓar ƙabilun da suka shigo cikinsu suka zauna, hannu bi-biyu, da ba su
‘yancin walawa, da auratayya da su (Adamu, 2011, sh. 68-69).
1.5.7 Shigowar Baƙin Al’ummu
Babu shakka shigowar baƙin al’umomi (na kusa da na nesa) ƙasar Hausa, waɗanda suka cakuɗu da al’ummar Hausawa,
ta sanadiyyar kasuwanci da zamantakewa da kuma auratayya, sun taimaka wajen bunƙasar ƙasar Hausa. Alal misali, an ga irin yadda
Larabawa suka yi tasiri ta fuskoki daban-daban da suka haɗa da; abinci da suturu da ma harshe a rayuwar Hausawa. Irin waɗannan abubuwa sun taimaka wa Hausawa da ma bunƙasa wasu garuruwan ƙasar baki ɗaya. Haka kuma misalai da za a iya la’akari da su ta ɓangaren ci gaba da wasu garuruwan ƙasar Hausa suka samu sakamakon cuɗanya da wasu al’ummomi
na kusa su ne, zamantakewa da auratayya. Domin an ga yadda ta sanadiyyar
zamantakewa ko auratayyar nan Hausawa sun ɗauki abubuwa da dama
daga wasu al’ummomi daban-daban kamar, al’ummar Fulani da Kanuri/Barebari da
Yarabawa da sauransu.
Haɗuwar da Hausawa suka yi da al’umomi da dama, ta sa a yau sun zama
ababen nunawa, musamman cakuɗuwarsu da al'ummar Larabawa da Turawa. A nan,
Hausawa sun ƙaru da abubuwa da yawa waɗanda suka kai su ga bunƙasa, wanda da sun keɓance kansu sun kuma dogara da abubuwan da suka yi, ko suke da su,
da ba su kai ga haka ba.
Haka da Turawa suka zo,
duk da cewa sun tarar da Hausawa cikin rufin asiri da tsari mai kyau ta fuskar
zamantakewa da mulki, wanda suka samu a ƙarƙashin tutar Shehu Usman Ɗanfodiyo, amma tunda
kogi bai ƙi daɗi ba, Hausawa sun ƙaru da abubuwan da Turawan suka zo da su ta fuskar ilimi da sufuri
da sauransu, waɗanda sun taimaka wajen faɗaɗa cigaban garuruwansu da harshensu da ma ƙasar baki ƙaya.
Babu shakka, ƙasar Hausa a yau ta bunƙasa, ta faɗaɗa ta ɗaukaka ta yaɗu zuwa ga ƙasashe na kusa da na nesa da ita. Amma haka bai
samu ba sai da cigaban garuruwan ƙasar ya kai a nuna, bisa
waɗancan matakai da aka zayyana a baya.
A taƙaice dai, batu na bunƙasar garuruwan ƙasar Hausa, abu ne wanda ba za a iya bayaninsa kai tsaye ba, har
sai an kawo magaanar ƙaura, da fatanci da noma da nema ko yaɗa ilimi da sana'o'i da kuna yaƙe-yaƙe. Da sauransu.
1.6 Kammalawa
Ta la’akari da wannan
bincike da aka gudanar, za a fahimci yadda wasu garuruwan ƙasar Hausa suke da irin cigaban da suka samu, ko bunƙasar da suka yi ta wasu muhimman hanyoyi da aka zayyana. Bagu
da ƙari, wannan shi yake nuna cewa duk wata ƙasa a duniya mai son
cigaba ko ta ci gaban, ba haka kawai ta tsinci kanta ba, tabbas sai da ta
jajirce wajen ilimi ko sana’o’i ko noma da sauransu. Amma fa duka a ƙarƙashin jagoranci nagari.
A wannan takarda an yi
bayanin ƙasar Hausa da yanayinta da asalin Hausawa da
garurwan ƙasar Hausa. Har ila yau, an kawo tarihin garin
Daura da Kano da kuma Damagaran. Daga nan aka faɗi wasu muhimman matakai
waɗanda ƙasar Hausa ta yi amfani
da su daga lokaci zuwa lokaci, kuma suka taimaka wajen bunƙasarta tun daga wancan lokaci har zuwa yau.
MANAZARTA
Adamu, M.T.
(1997). Asalin Hausawa
da harshensu. Kano: Sarkin
Kura Publishers LTD.
Adamu, M.U (2007). Kano da maƙwabtanta. Kano: Goɓernment Printing Press.
Adamu, M.U.
(2011). Sabon tarihin
asalin Hausawa. Kaduna : Espee Printing
And Adɓertising.
Amfani, A.H. (2011). The
Hausa languge and hausa people yesterday, today and tomorrow. (One Day
Symposiun) University Assembly, Hall Ahmadu Bello University, Zaria.
CNHN, (2006). Ƙamusun Hausa. Zaria: Ahmadu Bello University Press Ltd.
Dokaji, A. A.
(1958). Kano ta dabo ciigari.. Zaria: Northern Nigerian Publishing Company.
Fagge, U.U (1999). Ire-Iren
karin harshen Hausa na Rukuni. Kano: Benchmark Publishers Limited.
Kano, M.A (1983). Hikayoyin kaifafa zukata.. Kano: Benchmark Publishers
Limited.
NNPC, (1970). Hausawa da maƙwabtansu, (1). Zaria: Northern Nigerian
Publishing Company.
Yusuf, S.L (2010).
Tarihi da haɓakar harshen Hausa a jiya da yau. Takardar da
Aka Gabatar a Taron Ƙara wa Juna Sani; Sashen Nazarin Harsunan
Nijeriya, Jami’ar Bayero Kano.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.