Citation: Usman IBRAHIM (2018). Shata Mahayi A Sana’ar Waƙa. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. 6. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
SHATA MAHAYI A SANA’AR WAƘA
Usman IBRAHIM
Abstract
Occupation is a process whereby a human being
uses the natural resources, wisdom and endowments that God makes available for
him to utilize for his survival. This research focuses on the gift Dr. Mamman
Shata Katsina has in song. A painstaking research proves that Shata was not
formally bequested this powerful gift from his parents. History has recorded
that, the popular Hausa singer Shata was an intruder in the profession of
singing, because he has mentioned it in his ‘Bakandamiya’. The research therefore
aims at establishing the fact that Shata’s perfection in the profession of oral
literature has not any connections with family background inheritance in
singing.That was the reason Shata uses many examples to exaggerate his
technical know-how through satires and belittling those that have had oral
skills from their parenthood.The methodology used in this research relied on
secondary source data. Finally, the research reveals that the majority of
informal singers of Hausaland are excellent when it comes to performance. To
buttress this statement Gao Filenge was an example among many others.
1.0 Gabatarwa
Asalin
kalmar ‘mahayi’ ta samo asali ne daga haye. Ma’anar haye kuwa ta ƙunshi abubuwa da aka
fara ko aka samu da rana tsaka (Ibrahim, 2011). Saboda haka, Dr. Mamman Shata
Katsina, wanda ake yi wa kirari da ‘Mahadi mai Dogon Zamani’ yana ɗaya daga cikin makaɗan baka da aka
lissafosu a layin mahaya. Alalhaƙiƙa wani abin al’ajabi
a wajen wannan mawaƙi shi ne, a matsayinsa na mahayi a adabin baka na waƙa, amma kuma ga shi
ya tsere sa’a a fagen waƙa, ba ma mahaya irinsa ba, har magada bai musu ƙasa a guiwa ba. Gwani
na gwanaye. Maƙaɗa Shata fasihi ne a
adabin baka da al’adu Hausawa. Misali mafiya yawan ɓangarorin rayuwar bil
Adama Shata ya waƙe su, kama tun daga kan al’adu da ɗabi’u da siyasa da
sana’o’i da zamantakewa da tatsuniya da tarihihi da kuma addinin Musulunci.
Bugu da ƙari, Shata ya ƙutsa cikin abubuwa na
kimiyya da ƙere-ƙere ya waƙe su kamar waƙar ‘Kumbo Appolo.’ Ɓangaren tarihi kuwa, ga
waƙar
‘Sarkin Daura.’A fannin tatsuniya ga ‘Mai Rano Garba Autan Bawo.’
Saboda
haka, wannan takarda ta bibiyi tarihin Shata a sana’o’in da ya aiwatar a
lokacin da yake raye, wato tun daga yarinta har ya zuwa tsufansa. Waɗannan sana’o’i su ne:
tallar alewa da tallar goro da kiwon bisashe da noma da kamun kifi (Su) da
farauta da kasuwancin auduga da gyaɗa da sayar da lemon kwalba da kuma sana’ar kiɗa da waƙa da a cikinta ya yi
suna a duniya baki ɗaya (Sheme da wasu,
2006). Shata yana cikin makaɗan jama’a a cikin rabe-raben makaɗa (Ɗangambo, 2008). Makaɗan jama’a su ne makaɗan da suke yi wa kowa
da kowa waƙa, ba sai mai sarauta ko mai riƙe da wani babban muƙami ba. Sai dai, waɗannan abubuwa da aka
lissafo ba su ne turakun takardar ba, an kawo su ne, a matsayin wasu ƙananan saƙonin takardar.
Lallai, wannan batu ‘Shata Mahayi a Sana’ar Waƙa’ ya fito da
matsayin Shata a masanin adabin baka da al’adun Hausa (Abdulƙadir, 1975 da Sheme,
2006 da Ƙanƙara, 2013).
2.0 Dr. Mamman Shata Katsina
Maƙaɗa Shata an haife shi
ne a hukumar Musawa ta Jihar Katsina a shekarar 1922-1925 (Amin, 2011, p. 120).
Musawa ta samo sunanta daga ‘Sansanin da Musa ya kafa’ tana da nisan mil
casa’in daga birnin Katsina (Ƙanƙara, 2013, p. 21).
Musawa ta kasance cikin ƙaramar Hukumar Kankiya, amma da aka ƙirƙiro ƙananan Hukumomi ran
1/5/1989, sai ta sami cin gashin kanta, ta zama ƙaramar Hukumar Musawa
(Ƙanƙara, 2013, p. 23).
Sai dai, ainihin sunan Shata na yanka Muhammadu, sunan mahaifinsa Ibrahim Yaro
cikakken Bafulatani ne. Shata ya yi karatun allo a lokacin ƙuruciyarsa
‘makarantar toka.’ Malaman Shata na makarantar allo sun haɗa da: Mallam Amadu da
Liman Ɗandaudu da kuma Malam Ali (Anas, 2014, p. 18). Daga
makarantar allo Shata ya fara nuna wasu ɗabi’u na buwaya, har sannu a hankali sai ya
goce daga makaranta ya fara hidimar tallar goro (Sheme, 2006, p. 49). Kodayake
akwai saɓanin ra’ayi daga wasu
malamai, domin akwai masu ra’ayin cewa da farko tallar alewa ya fara yi kafin
tallar goron (Gusau, 2018). A zamanin tallar goro Shata ya yi zage na kasuwanni
suna sayar da goro daga nan asalin shahara ta soma har ake masa laƙabi da ‘yan hamsin.’
Lalle masana sun tabbatar da wannan zance da cewa:
…in ya ɗauko goron a baka sai
ya yi ta juya shi a hannu yana birkitar da hannun, bakar ba ta kifewa kuma
goron ba ya zubewa (Ƙanƙara, 2013, p. 31).
Wato, yana wasa da bakar domin jan hankulan
jama’a, su fahimci baiwa da basira da hikima da Ubangiji ya yi masa.Har ila
yau, an ce a fagen tallar goro da alewa ya tsinto kalmar da ake masa da laƙabi Shata. Ga abin da
ake cewa a kan dalilin samuwar kalmar Shata:
Shi ma kan shi Shatan
lokacin da ya fara tallar goron ya tsiri wata ɗabi’a wadda bai san dalilinta ba. In
yana tallar goro sai ya riƙa ciko ko shato hannu yana ba mutane
ba tare da ya ƙirga ba. Ya ce ta nan ne batun laƙabin ‘Shata’ ya fito.
Kodayake ya ba wannan baƙuwar kalmar fassara daban-daban, amma bayani mafi kamanci
shi ne wanda in ya je ga mutane sai ya turo masu farantin alewa ya ce ‘sha ta’’
ko sha ta alewa, ‘ma’ana, ‘ ku sha alewa.’ To sai wani ɗan uwansa Magaji
Salamu ya riƙa kiran shi Shata. Wasu kuma sunce shi Magaji Salamun ne
ke tambayar sa, ya ce ‘ ina kuɗin ka? In ya dawo daga sana’a, shi kuma sai ya ce ‘na yi
Shata da su’. In ya ce ‘ mene ne Shata? Sai ya ce ‘ na kashe.’ To daga nan sai
ya riƙa kiransa Shata (Ƙanƙara, 2013, p. 33)
3.0 Shata a Sana’o’in Gargajiya
Sana’a
fasaha ce ta neman abin masarufi wadda ɗan’adam ke amfani da ƙarfinsa da basirarsa
da kuɗinsa domin sarrafa
ta. An raba sana’o’in gargajiya na Hausa zuwa kashi uku ta hanyar la’akari da
jinsi, akwai sana’o’in da suka jiɓanci jinsin maza zalla, kamar noma da gini a
yayin da kitso da koɗa da dakau mata ne
zalla suke yin su a al’adance. Hakazalika, waɗannan abubuwa guda biyu wato; waƙa da kirari an yi
tarayya; wato maza da mata suna cikin wannan masana’antar kiɗa da waƙa (Gusau, 2018) da
(Daura, 2016) da Ibrahim, (2011). Kodayake, makaɗa suna yi wa duk wanda ya ba su dukiya
waƙa
da kiɗa, ka ga waƙa tamkar sana’a ce a
wajensu. Haka kuma, babu rukunin jama’a da ba sa yi wa waƙa kama daga talaka da
sarki da mai kuɗi da mai ilimi da
masu iko sojoji da mata masu zaman kansu (karuwai) da makamantansu. Saboda
haka, Shata yana cikin makaɗan jama’a a cikin rabe-raben da masana suka karkasa
rukunin makaɗan Hausa (Ɗangambo, 2008).
3.1 Shata Mahayi
Shata a
matsayinsa na mahayi a sana’ar waƙa ya nuna irin baiwa
da basira da Allah ya yi masa. Domin cewa ya yi shi dai yasan tun da Allah ya
fari duniyarsa bai yi irinsa ba. Ya ce ko a cikin Larabawa ko Turawa ko Baƙar Fata wane ne kamar
Shata Na-Yelwa. Saboda haka, al’amarin Shata babu gado, sai dai baiwa daga Mai
dukka. Har ila yau, a matsayinsa na mahayi ga abin da yake cewa a kan abubuwan
da ya waƙe:
Na yi
wa ruwa waƙa, na yi wa dutse waƙa na yi wa dawa na yi
wa gari, na yi wa raggwaye irin su Salisu Soso, wanda su aikin su cin abinci,
na yi wa teloli irin su Rangama Audu Bukar. In tsire kake yi to na taɓa yi ma Ayuba Musawa,
in kai ɗan jarida ne to na yi
wa Ali Gombe waƙa, na yi wa sheɗan waƙa inda na yi wa kaina
waƙa
ni da Mamuda Wapa da shi kan shi sheɗan ɗin (Ƙanƙara, 2013, p. ɗɓiii)
Har wa yau, Shata ya
fito ƙarara ya nuna cewa shi mahayi ne a cikin wannan sana’ar
roƙo.
Ga abin da yake cewa daga cikin ‘Bakandamiyarsa’ inda ya tabbatar da cewa shi
mahayi ne:
Jagora: Ka kau ga
abin ba gado na ba
: Roƙo shiga nai na gagara
ciki nai
: Sai ƙaƙa Ƙanƙara, (2013, p. 245)
4.0 Shata Mai Salailen Sarrafa Harshe
Salon
sarrafa harshe kusan a ce ƙauli ne da ya bayyana kansa da kansa.
A dunƙule za a iya siffanta salon sarrafa harshe da cewa dabara
ce da kisisina na sarrafa harshe (Bunza, 2009). Sai dai, Muhammed (1997) ya faɗaɗa ma’anar salon
sarrafa harshe da abubuwa kamar: kayan adon harshen waƙa da ya ƙunshi amsa-kama da ƙarangiya da kamance
da mutuntarwa da tamka da saɓi-zarce da kinaya da zayyana da makamantansu.
4.1 Shata Mai Habaici
Yahya
da wasu, (2015) sun ba da ma’anar habaici da cewa kishiyar yabo ne, kuma a
kaikaice yabo ne ga gwarzon da ake yi wa waƙar. Habaici yana ɗaya daga cikin ƙananan rassa na
adabin baka da ake amfani da shi wajen zagin mutum a fakaice. Shata ya yi fice
wajen cusa habaici cikin waƙoƙinsa, a yayin da wani
ya hana shi zarafi, dubi yadda yake habaici a cikin waƙar‘Alo-alo mai ganga
ya Gode’. Ga abin da yake cewa:
Jagora:Wurin
da Kura,
:Take
shan ruwa,
: Kare
baya zuwa,
: Karen
ko na wane ne,
:
Kowace karya tah haifai,
: Ɗan kusun uwa,
A nan
Shata yana yin habaici da cewa wajen da zai yi waƙa babu wani maroƙi da zai je, ko ɗan wane ne shi ko
magaji ne ko mahayi ne da cewa ko wane ne ubangidansa. Daga ƙarshe ya yi amfani da
kalmar lalata mutum da ƙasƙanci da cewa ɗan ‘kusun uwa.’ Har wa yau, Shata ya yi zambo
a cikin Bakandamiyarsa da cewa:
Jagora:
Ni ko yanzu kasuwa taw watse,
:Ɗankoli da hura
goranshi,
:To shi
ko kasuwa tai riba;
:Ni ko
yau aka hana roƙon nan duka
:Mamman
alhamadullahi!
Sheme
da wasu, (2006, p. 236)
Alhaji
Shata ya nuna cewa shi dai karankansa ya amfana da waƙa ya samu arziki da
wadata. Sai dai ya yi habaici a sauran maroƙa da abin duniya ba
shi da faɗi da nauyi a wajensu.
Kuma ya nuna cewa sana’arsa ba guda ɗaya ce ba, suna da yawa ko yau ya bar waƙa ya samu biyan buƙatar rayuwa don haka
yau ma sana’ar roƙo ta watse ba damuwarsa ce ba.
4.2 Shata Mai Barkwanci
Bargery,
(1934, p. 89) ya bayyana barkwanci da cewa wasan zolayako kalmomi na raha da ke
samar da annashuwa domin a dara.Ko kuma wasan dangi da ke haifar da fara’a tare
da farin ciki maimakon baƙin ciki. Alal misali, Shata a waƙar da ya yi wa
‘Tijjani Dagazau’ cewa ya yi, shi Tijjani Babarbaren asali ne, wanda ba ya faɗa da Fulani. Ka ga a
nan ya bayyana wasan abota da ke tsakanin Fulani da Barebari da Arawa da
Gimbanawa da Katsinawa da Kabawa na barkwanci. Bugu da ƙari, a cikin waƙar samun ‘jihar
Katsina’ ya yi barkwanci sosai ga misali kamar haka:
Jagora:Neman
aure a je shi da mu,
:Daurin
aure a je shi da mu,
:Sai
wajen ɗauko amarya,
:Sai a
ce babumu a kiɗa,
:Na bi
ta ina waƙarmu ta ‘yan yara,
:In kin
je kul kika ba da bado.
(Shata: Allah Raya Jihar Katsina)
Saboda
haka, Shata ya ƙware wajen salon sarrafa harshen Hausa, a matsayinsa na
mahayi a sana’ar roƙo. Domin anan ya nuna da shi aka je fadar shugaban ƙasar Nijeriya Janar
Ibrahim Badamasi Babangida domin fafutukar samar da jihar Katsina, amma daga ƙarshe sai ake nuna ba
a buƙatar maroƙa, shi kuwa sai ya yi barkwanci domin
su ankare da cewa akwai matsala idan babu su a cikin harkar.
Haka
kuma, a cikin waƙar ‘Malam Bawa Magajin Doka’ ya yi barkwanci. Ga abin da
yake cewa:
Jagora
:Da na je wajen Malam Bawa magajin doka,
:An ba
ni tuwo sai da na ƙoshi,
:An ba
ni fura sai da na ƙoshi,
‘Y/Amshi:
Alhaji har an ba ka abin ɗan tofi,
Jagora:
Cikinaku wa ya gani ‘yan yara!
‘Y/Amshi:
Alhaji ku biyu dai a cikin ɗakin nan.
(Shata: Malam Bawa Magajin Doka)
4.3 Shata Mai Kinaya
Gusau,
(2008) ya nuna kinaya wata dabara ce ta sakaya zance, wanda take juyar da abu
daga asalinsa wato ma’anarsa ta farko zuwa wata ma’ana ta biyu wato ta
sakayawa. Har wa yau, kinaya na nufin kiran abu, musamman da sunan da ba shi ne
nasa da aka san shi da shi ba, domin wannan suna ya bayar da ma’anarsa da kuma
tunanin da ma’anar za ta kawo ga wanda aka kira da wannan suna, wannan shi ake
kira kinaya (Yahya da wasu, 2015). Alal misali Mamman Shata ya yi amfani da
wannan salon a cikin waƙar ‘Yan Arewa Ku Bar Barci’ domin ya nuna barci talauci
yake haddasawa da mutuwar zuciya. Ga abin da yake cewa:
Jagora:
Kowa ya sha wuya ya nemi abi nai,
: To ya
kashe su ta hanya mai kyau,
‘Y/Amshi:
Kuɗi a kashe su ta hanya
mai kyau
(Shata: Waƙar Kuɗi)
Ka ga
Shata ya yi kinaya da cewa a koyi tattali domin dukiya sai an reneta har take
kai ga yalwa da bunƙasa. Saboda haka, almubazzaranci abu ne mumuna domin
nakasar da dukiya yake yi, har ya kai ta ga lalacewa.
Ba ma
haka ba, Shata ya ma bayyana kinaya a fili, domin a yau ‘yan mata da samari
suna jan aji a tsakaninsu da waɗanda suke so, in har jan ajin ya yi yawa sai a haifar da
matsala ta nadama. Ga misali daga ‘Bakandamiyarsa’.
Jagora:
Kowa ya ja zare idan ya tsinke,
: Bai
ja daidai ba,
‘Y/Amshi:
Alo-alo mai ganga ya gode,
: Yaran
mai ganga sun gode.
(Shata:
Waƙar
Bakandamiya)
A nan
akwai gargaɗi da cewa duk abin da
za ka yi riƙa yi kana lissafi akan abin da zai biyo baya.
4.4 Shata Magori Wasa Kanka da Kanka
Bargery,
(1934, p. 745) ya bayyana ma’anar magori da cewa, mai sayar da magunguna na
gargajiya iri-iri kamar na sammu ko na rashin lafiya da yake ɗauke da burgamin
maganinsa. A yayin da wasa nanufin kaifafa abu ta hanyar kambame. Wato kalmomi
na ƙarin
gishiri da magori yake yi wa kansa. Dr. Mamman Shata ya zaɓi ya riƙa yi wa kansa kirari
kodayaushe ya nuna baiwa da Allah Ta’ala ya yi masa da ya bambanta shi da
sauran maroƙa. Ga abin da yake faɗi:
Irin mu
ubangiji yakan yi mu daban ne, ba muna wasa kanmu ba ne, ba muna faɗi ba ne don kanmu a’a
a’a ba abin da ya dame mu ai ba muke son kan mu ba mutane ke son mu (Ƙanƙara, 2013, p. ɗɓiii).
Haka
kuma, a cikin waƙar ‘Kai ‘yan yara gumina nake ci’ Shata ya nuna shi ba ci
ma zaune ne ba, domin da ƙarfinsa da basirarsa yake aiwatar da sana’ar waƙa. Alal misali
Jagora:
Ka ji kalanguna ya canza,
:Faɗi yake Shata guminai
yake ci,
Y/Amshi:
Kai ‘yan yara gumina nike ci. Gusau, (2009, p. 328)
A nan
Shata yana zuga kansa da cewa ai idan ya ɗauki ‘yar gangarsa, har kalangunsa yana sauya
kiɗa, domin ya tabbatar
da cewa shi da sana’ar waƙa yake samun kuɗi, ba haka siddan jama’a suke ba shi kuɗi ba, domin sai ya
wahala kafin ya samu zarafi. Bugu da ƙari, a duk lokacin da
mutum ya fitar da gumi to an daurewa wahala. A sakamakon haka, ya lissafo
sana’o’i da suke bayyana samun kuɗi su ne: ofis da gona da leburanci da tireda
da tuƙi da kuma fatauci.
Haka
kuma, a cikin waƙarsa ta ‘Alo-alo mai ganga ya Gode’ Shata ya yi wa kansa
kirari da cewa:
Jagora:Allah
ya yarda,
:Ba ku
samo canjina ba,
:Balle
in zauna,
:Wai
har in ce zan huta,
:In dai
ɗan samu in sarara,
:M’m
wane hutu Shata,
:Ka riƙa dai,
:Gwamron
giwa mai ban tsoro,
:Na
Habu ɗan Ibrahim,
:Kyarkeci
mai wawar kora ɗan yaro,
:Zaki
mai ta’adin ƙarfi ɗan Iro,
:Kowa
ya san kowa Katsinawan Dikko,
:Su da
Kanawan Dabo,
:Da
mutanen Zazzau,
:Gauraya
da Jasawa namu,
:Hillanin
Yola,
:Shata
shiga Gombe kai ne,
:Balle
Bauchin Yakubu,
:Shata
tafi Borno ni ne,
:Sun
san ni,
:Na san
su,
:Shata
ne,
:To
kuma ƙaƙa?
:Eye!
Gusau,
(2009, p. 348)
Babu
shakka, daga jin waɗannan saɗarori an san Shata
yana yi wa kansa kirari ne, domin ya nuna tserewa sa’a. Haka kuma, ya faɗaɗa nason ɗuriyarsa illahirin
Nijeriya ta arewa babu inda ba a san Shata ba. Sai dai, ya ƙara kwarzanta kansa
da kansa a cikin ‘Bakandamiyar’ kamar haka:
:Kowar
rasa Shata, ya yi asarar waƙa,
:Kowar
rasa ni bai sha waƙa ba, ko wane ne,
:Kuma
ko ɗan wa, Allah kau!
Shema
da wasu, (2006, p. 25)
Har ila
yau, Shata ya nuna idan ba shi ya yi wa mutum waƙa ba, to bai sha waƙa ba, ko da magajin
waƙa
ne ya yi ma sa, ballantana mahayi kamarsa. Hakazalika, Shata ya ƙara fito da zuga
kansa da yake yi a cikin wannan saɗara da cewa:
:’Ciji’ in ji yara,
:Abin
tsoro ni,
:Sun
san ni, Shata ne,
:Sai ƙaƙa, iye?!
:To!
Shema
da wasu, (2006, p. 25)
A nan
Shata ya ƙara siffantar da kansa da cewa shi abin tsoro ne. Daɗin da ɗawa su maroƙa abokan sana’arsa ta
roƙo
sun san ko shi wane ne a filin waƙa, domin ya tsere
sa’a.
5.0 Kammalawa
A duk
inda ake maganar mawaƙi mahayi a sana’ar kiɗa da waƙa dole ne a ambato
‘mai tambura na Balkin Sambo’ Dr. Mamman Shata Katsina. Shata ya amfana da wata
karin maganar Bahaushe da yake cewa: ‘sana’a goma maganin mai gasa’ domin Shata
ya gwada sa’ar sa a kan sana’o’i daban-daban har ya kai ga tsayawa a kan kiɗa. Lallai duk wani
abu da ɗan’adam yake fatan
samu Shata ya samu domin shi attajiri ne don dukkan abin da mutum ke buri a
duniya a sanadiyyar yin shigege a sana’ar da ba magaji ba ya samu. Shata ya yi
sana’o’i iri-iri kamar yadda aka lissafa a sama, amma abin da ya yi fice ita ce
waƙa.
Saboda haka, wannan takarda ta fito da matsayin ‘Mahdi mai dogon zamani’ a
gurabe daban-daban. Alalmisali Shata a waƙoƙin sana’o’i da masu
sana’o’in gargajiya da Shata mai raya adabin Hausa domin a fahimci basirar da
Allah ya yi masa a matsayinsa na mahayi a sana’ar kiɗa. Bugu da ƙari, wannan takarda
ta nuna Shata wakilin sarrafa harshe a waƙar baka da mai
dabarun koɗa kansa. Hakazalika,
wannan maƙala ta yi ƙoƙarin nuna Shata a
matsayinsa na mahayi babu wani ɓangaren adabi da al’adun Hausawa da suka gagare shi da ya
nuna hikimarsa a waƙa.
Manazarta
Abdulƙadir, D. (1975). The role
of an oral singer in Hausa/Fulani society: A case study of Mamman Shata. Ph.D. Thesis. USA:
Indiana University.
Amin,
M.L (2011). Gudummuwar Dr. Mamman Shata Katsina wajen bunƙasa falsafar Bahaushe.
A cikin Funtua da Gusau (editoci) Waƙoƙin Baka
Na Hausa.Kano
Century Research and Publishing
Limited.
Anas,
S. M. (2014). A study of ɗandatti abdulƙadir’s appraisal of
Mamman Shata in Rasheed & Aliyu (eds.) Folklore,
Integration and National Deɓelopment in Nigeria. A Festschrift for Professor Ɗandatti Abdulƙadir, OFR. Zaria. ABU
Press.
Bargery,
G.P. (1934). A Hausa Englishd dictionary
and English Hausa ɓocabulary (2nded) Zaria: Ahmadu Bello University Press
Limited.
Bunza,
A. M. (2006). Gadon feɗe al’ada. Lagos: Tiwal
Nigerian Ltd.
Bunza,
A. M. (2009). Narambaɗa, Lagos: Ibrash
Islamic Publications.
CNHN,
(2006) Ƙamusun Hausa. Zaria: A.B.U. Press Ltd
Ɗangambo,
A. (2007). Ɗaurayar gadon feɗe waƙa. Amana Publishers Ltd.
Ɗangambo,
A. (2008). Rabe-raben adabin Hausa da
muhimmancinsa ga rayuwar Hausawa. Kano:
Trimph Publishing Company.
Daura,
H. K. (2016). Kirarin saraki a bakin mata: Nazarin zabiyanci a ƙasar Hausa. Kundin Digiri
na Uku, Jami’ar Ahmadu Bello.
Gusau,
S. M. (2008) Waƙoƙin baka
na Hausa: Yanaye-yanayensu da sigoginsu. Kano: Benchmark Publishers
Limited.
Gusau,
S. M. (2009). Diwanin Waƙoƙin Baka:
Zaɓaɓɓun Matanoni na Waƙoƙin Baka
na Hausa.
Kano: Century Research and Publishing Ltd.
Gusau,
S. M. (2018). Diwanin waƙoƙin baka
juzu’i na uku, matanonin wasu waƙoƙin Alh. Dr. Mamman Shata Katsina. Kano: Century
Research and Publishing Ltd.
Ibrahim,
U. (2011). Tasirin haye a sana’o’in Hausawa na gargajiya. Kundin Digiri na
Biyu, Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero Kano.
Ƙanƙara, A. I. (2013). Mahadi mai dogon zamani: Shata da kundin waƙoƙinsa. Kaduna:Labson
Production.
Sheme da wasu, (2006). Shata ikon Allah. Kaduna: Informart Publishers
Yahya
da wasu, (2015) “SAI ALU” sharhi kan
waƙoƙin da aka yi wa Dr.
Aliyu Magatakarda Wamakko
(Sarkin Yamma Sakkwato). Zaria: A.B.U. Press Ltd

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.