Citation: Hauwa Shitu LAWAL (2018). Nazarin Salon Rubutun Mujallar Fim. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. 6. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
NAZARIN SALON RUBUTUN
MUJALLAR FIM
Hauwa
Shitu LAWAL
Abstract
The Mujallar Fim (Fim Magazine) is a monthly
magazine produce in Hausa, which cover most of the activities of the Hausa film
industry (Kannywood). Buying and reading the magazine every month gave the
opportunity of coming into contact with the many orthographical errors being
made repeatedly by the writers and publishers of the magazine. As Hausa
language is really in need of a harmonized writing system. I saw a chance of
bringing out these orthographical errors to the publishers notice and public in
general for rectifications. The paper therefore brought out these errors which
usually distort the meaning of what is intended to conveyed or communicated.
The research employed reading the magazine and extracting the places where the
standard Hausa orthography was not properly adhered to a method of data
collection, and provided the correct versions based on the standard Hausa
orthography. As the Mujallar Fim (Film Magazine) is a popular magazine, it
should give its own contribution in the harmonization of Hausa writing system.
Tsakure
Wannan maƙala
ta yi nazarin Mujallar Fim wadda ke bayar da labarai, musamman waɗanda
suka shafi harkokin fina-finan Hausa, tare da duba ire-iren kura-kuren da ke
tattare da labaran. Ta hanyar tu'ammali da wannan mujalla ta fim da kan fito
wata - wata ne, na fahinci yawan kura-kuren da ake maimaitawa a kowane bugu, na
kuma ga cewa ya dace in fargar da mawallafan Mujallar domin a yi gyara, a kuma
kyautata ma'ana ga abin da ake rubutawa. Haka kuma wannan maƙalar ta yi ƙoƙarin fito da waɗannan
kura-kuren da aka tafka a wajen rubutu na yau da kullum. Akasari, mutanen da ba
su san da waɗannan ƙa'idoji
ba, sukan ɓata ma'ana ko zance ko manufar da ake son
isarwa. Hanyoyin da aka bi aka yi binciken su ne, ta hanyar karanta Mujallar da
tsakuro wuraren da ba a bi ƙa'idojin
rubutun ba. Sannan kuma da duba kalmomin harshen Hausa da masana suka taru suka
tace, suka amince a yi amfani da su wajen rubuta daidaitacciyar Hausa. Irin karɓuwar
da Mujallar Fim ta yi, ya dace a ce tana bin waɗannan
ƙa'idojin rubutu na Hausa
don ta bayar da ta ta gudunmowar wajen samar wa Hausa rubutu bai ɗaya.
1.0 Gabatarwa
Harshen Hausa, harshe ne
da kimanin ƙasashe ashirin ke amfani
da shi wajen zirgazirgarsu da sadarwa ta hanyar kasuwanci da waɗansu mu’amuloli na yau da kullum. Harshen Hausa shi ne mafi girma
kuma mafi sanannen harshe a nahiyar Afrika. Harshen Hausa ya zama harshen yau
da kullum ga miliyoyin jama’a da ba Hausawa ba ne a nahiyar Afrika. Kasancewar
harshe ne wanda ya samu karɓuwa a duniya, ya sanya masana da dama suka ga ya
dace a riƙa tsarkake ƙa’idojin rubutun da ke tattare da harshen.
Alal haƙiƙa an gudanar da tarurruka da dama a wurare daban-daban waɗanda suka ƙunshi masana ilimin
harshen Hausa domin tabbatar da yadda za a riƙa rubutun wannan harshen ta hanyar amfani da daidaitacciyar Hausa.
Kamar yadda Wurrna, (2005) ya ce, “Daidaitaciyar Hausa, ita ce wadda aka tace
ta, kuma masana ilimin harshen a tarurruka daban-daban suka amince a yi amfani
da ita”. Ya ci gaba da cewa, “An yi duka waɗannan tarurruka domin
amincewa da kalmomin harshen Hausa waɗanda za a riƙa amfani da su a rubutu. Saboda haka
daidaitacciyar Hausa ita ce wadda ake amfani da ita wajen rubuta ƙasidu da littattafai sannan kuma a wajen sadarwa
ta yau da kullum ta zama ita ce ake amfani da ita".
Kamar yadda Sa'id (2004)
ya ce, "Tun shekarar 1932 ne aka fara yunƙurin samun ingantacciyar hanyar rubuta Hausa, saboda muhimmancinta
wajen wallafe-wallafe cikin harshen Hausa". Saboda haka ya wajaba ga
kamfanonin Mujallu da na yaɗa labarai na Hausa su kiyaye tare da bin ƙa'idojin wannan dokar.
Sanin kowa ne kafofin yaɗa labari suna taka rawa muhimmiya, musamman ma a ƙasar Hausa wadda aka sami ɗaya daga cikin koma baya wajen karatu da rubutun boko.
1.1 Mujallu
Mujalla ba kamar jarida
ba ce da take fitowa kullum, ita Mujalla takan fito ne bayan kowane wata shida
ko uko ko biyu ko ɗaya ko ma bayan duk sati biyu ko ɗaya. Wannan dai ya danganta da masu buga ta. A kan haka ne ma,
Wurma, (2005, p. 11) ya ce, "Mujallu kamar Jaridu suke, sai dai akan yi
masu bango mai laushi irin na ƙaramin littafi, sannan
kuma sukan fito bayan mako ɗaya ko biyu ko wata, dangane da yadda aka tsara
da buƙatar jama'a".
1.1.1 Mujallar Fim
Wannan Mujalla ce da ke
watsa labaranta na yau da kullum da harshen Hausa, kuma tana yaɗa manufarta da tallace-tallacenta. Tana fitowa ne sau ɗaya a kowane wata. Sai dai kamar yadda aka yi bayani a baya, cewa
za a yi nazari ne a kan labaran da take watsawa a idon duniya tare da gano da
kuma fito da kura-kuran da ke tattare, ƙarara domin hannunka mai sanda ga marubuta labaran.
Ga yadda labaran sukc a
rubuce kamar haka;-
Labari na Farko
"Mahaifiyar Jamila Umar Tanko ta Rasu"
“Allahu Akbar! A ranar
Lahadi, 17 ga Afrilu, 2016 Allah ya karɓi ran Hajiya Yalwa Ahmad
Turaki a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano da ke birnin Kano.
Marigayiyar, mai shekaru
58 a duniya, ta rasu ne da misalin ƙarfe 10 na safe bayan ta sha fama da rashin lafiya inda ta shafe
tsawon lokaci ta na jinya a asibitin. Bayan rasuwar ta an ɗauke ta aka kai ta mahaifar
ta, wato garin Gumel a Jihar Jigawa, aka yi mata jana’iza, daga nan aka
dawo Kano aka yi zaman makoki.
Hajiyar ta rasu ta bar
'ya'ya bakwai, maza uku, mata huɗu, ciki har da
fitacciyar marubuciyar nan Hajiya Jamila Umar Tanko.
Marubuta da dama sun je
gidan su Jamila din da ke Giginyu su ka yi mata ta'aziyya.
Muna fatan Allah Ya jiƙan ta, kuma Ya albarkaci, abin da ta bari. amin."
Yadda
aka ruwaito a Mujallar Fim (“Yakubu” 2016, p. 49).
Har ila yau a wannan
labarin, marubucin ya haɗe kalmar aikatau da ta 'yar mallaka wuri ɗaya. Sa'id, (2005, p. 11) ya ce, “Babbar manufar kula da raba
kalmomi ko haɗe su a muhallin da ya dace ita ce, don a
tabbatar da ma'anar da ake nufin rubutawa ba ta canza ba". Don haka ga
yadda ya kamata a rubuta, Allah ya ji ƙanta ba "Allah ya Jiƙan ta ba" Haka kuma an rubuta “mahaifar ta” maimakon mahaifarta.
Marubucin ya saɓa wa dokar nahawun Hausa. Masana da dama sun
bayyana cewa kalmomin gajeruwar 'yar mallaka a haɗe suke da abin da aka mallaka ba a raba su.
Sa'id, (2005, p. 6) ya
ce "n" da "r"… ana amfani da su ne wajen mallaka ko jingina
wani abu da wani. "n" a gurbin namiji ko jam’i. "r" kuma a
gurbin mace.”
Labari Na Biyu
"Zee-Zee ta caza ƙwaƙwalwar masoyan
ta
FITACCIYAR jaruma kuma
mawaƙiya Ummi Ibrahim
(Zee-Zee) ta shirya gasa ga abokan ta na shafin ta na BBM. A
gasar, wadda ta sanar tun kusan wata biyu da suka wuce, ta ce za ta bada
tambayoyi goma game da ita, duk wanda ya amsa daidai kuma ya fara tura mata, za
ta ba shi kyautar N100,000.
Kuma haka aka yi, domin
kuwa ran Asabar, 9 ga Mayu, 2015, da misalin ƙarfe 1:00 na rana ta tura wa dukkan abokan ta da ke bin ta
a shafin nata na BBM sako da ce wa: “Salam friends, yau ne ranar gasar da na ce
zan yi. Zan aiko da tambayoyi goma a game da ni, wanda ya fara amsa su daidai
zan ba shi kyautar N100,000 ran Litinin. Kuma sai ran Litinin zan fadi wanda ya
yi winning. Sannan Pls kowa sau ɗaya kawai zai bada amsa. Na gode, a saurari tambayoyin, zan
aiko bada jimawa ba in
"God I trust"
“Bayan kamar awa ɗaya haka, sai ga shi ta aiko da tambayoyin kamar haka:
1. Menene cikakken suna
na?
2. Ni wace yare ce?
3. Shekaru na nawa?
4. Wane gari aka haife
ni?
5. Wane abinci na fi so?
6. Wane kala na fi so?
7. Wace ƙasa na fi zuwa hutu?
8. Menene sunan mawaƙina na Indiya?
9. Menene sunan Sahabin
Annabi da na fi so?
10. A wane gari na ke da
zama?
Nan take aka fara aiki,
kowa ya yi ta caja ƙwaƙwalwar sa don ganin cewa ya bada amsa
daidai kuma ya fara turawa don ya samu nasarar lashe wannan kyauta.”
Yadda
aka ruwaito a Mujallar Fim (“Muhammad” 2015, p. 15).
A labari na sama akwai
kura-kurai da aka yi wajen rubuta kalmomin 'yar mallaka. Sa'id (2005, p. 69)
ya ce, “Mallaka kalma ce wadda ke nuna mallakar wani abu, ta rabu
zuwa gida biyu …. akwai doguwa da kuma gajeruwa.
Wani abin la'akari da
shi a nan, shi ne a duk inda aka ga doguwar mallaka, to za a ga cewa ba liƙe take da abin da aka mallaka ba. Haka kuma a
duk inda aka ga gajeruwar 'yar mallaka, to za a ga cewa liƙe take da abin da aka mallaka.
|
Doguwar Mallaka |
Gajeruwar Mallaka |
|
Gida nawa |
Gidana |
|
Mota tawa |
Motata |
|
Gona tasa |
Gonarsa |
Ga sauran kura-kuren da
wannan labari yake tattare da su tare da gyare-gyaren da aka yi kamar haka:
|
Kuskure |
Daidai |
|
Masoyan ta |
Masoyanta |
|
Menene |
Mene ne? |
|
Abokan ta |
Abokanta |
|
Shafin ta |
Shafinta |
|
Suna na |
Sunana |
|
Shekaru na |
Shekaruna |
|
Mawaƙi na |
Mawaƙina |
|
A wane gari na ke da
zama? |
A wane gari nake da
zama? |
|
Ƙwaƙwalwar sa |
Ƙwaƙwalwarsa |
|
Su ka |
Suka |
|
Bada |
Ba da |
|
Wane kala na fi so? |
Wace kala na fi so? |
Haka kuma marubucin
wannan labari ya yi kuskure wajen rubuta kalmar wakilin suna tambayau, ya rubuta “menene" a
maimakon mene ne? Abin lura a nan shi ne, tambaya aka yi, amma sai ba a
nuna alamar tambayar ba. Sa’id, (2005) na da ra'ayin cewa ayar tambaya takan zo
bayan an gama tambaya. To amma wannan Mujallar wajen bayar da wannan labarin ba
ta yi amfani da alamar tambaya ba.
A tasu gudumuwar,
Abdulkadir da wani, (2017, p. 37) sun ce “Alamar tamabaya ana amfani da ita ne
a lokacin da aka yi tambaya”.
Labari na Uku
“Ali Show ya samu Haidar, kuma ya yi rashin mahaifi.
ALLAH Sarkin daɗi, inji ɓarawon takanɗa. Allah Ya albarkaci
fitaccen mawaƙin nan Aliyu Mukhtar,
wato Ali Show, da matar sa Maryam da samun ɗa namiji. Maryam ta
haihu da misalin ƙarfe 12:00 na dare a
ranar Asabar, 29 ga Janairu, 2017 a asibitin tarayya mai suna Federal Medical Centre da ke Katsina.
An raɗa wa yaro suna Aliyu, wato ya ci sunan mahaifin sa kenan.
Amma kuma da Haidar za a riƙa kiran shi.”
Yadda
aka ruwaito a Mujallar Fim (“Doro” 2017, p. 36).
Labari na Huɗu
"Alƙalam
Ta Karrama Gwarzayen Adabi
An jaddada tasiri da matsayin Alhaji Abubakar Imam
MANYAN masu jawabi a
wajen wani taro da ya zo daidai da Ranar Marubuta ta Duniya da aka yi a Kaduna
a watan jiya sun ƙara jaddada matsayin
marigayi Alhaji Dr. Abubakar Imam a fagen adabin Hausa, suka ce har yanzu babu
kamar sa. Taron wanda aka yi a ranar Asabar, 4 ga Maris, 2017, ƙungiyar marubuta mai suna Alƙalam ce ta shirya shi domin tunawa da Imam tare
da karrama wasu mutane da su ka agaza wa ci gaban adabi.
A bikin, an karrama Imam
da bayyana ayyukan sa da lambobin yabo da ya samu da kuma bayar da
kyauttutukan yabo ga wasu marubuta littattafan Hausa da su ka yi ftce a
fannonin adabin Hausa guda huɗu, da kuma jinjina ga wasu da suka bayar da
gudunmawa wajen haɓaka adabin Hausa. An fara bikin da misalin ƙarfe 11:05 na safe a babban ɗakin taro na Arewa House,
da ke Unguwar Sarki Kaduna.
Da farko mai gabatarwa
Malam Hassan Umar Kainuwa, yu umarci Malam Shehu Ayatullahi ya buɗc taro da addu’a.”
Yadda
aka ruwaito a Mujallar Fim (“Muhammad” 2017, p. 45).
Marubucin wannan labarin
ya fara rubuta shi ne da manyan haruffan Hausa. A dokar nahawun Hausa babban
harafin farko ne kaɗai ake fara rubutu da shi. Marubucin ya rubuta
"MANYAN masu jawabi” a maimakon Manyan masu jawabi.
Abdulkadir da Wani,
(2017, p. 22) sun ce “Akwai wurare da dama inda ya zama wajibi a fara rubutu da
manyan haruffa. Waɗannan wurare: rashin fara rubuta su da manyan baƙaƙe kuskure ne”. Sun ci gaba da cewa waɗannan wurare sun haɗa da farkon rubutu ko
farkon magana....”
Haka kuma a wannan
labarin na sama, marubucin ya yi kuskure a wajen rubuta kalmomin manunin lokaci
shuɗaɗɗe. Misali ya rubuta su
ka a maimakon suka. Haka kuma an rubuta kalmomin lokacin gaba kamar haka "Mu na a maimakon, muna.
Wurma (2005, p. 64) ya ce, “Manunin lokaci shuɗaɗɗe su ne kalmomin da suke nuna cewa an aikata wani abu, kuma ga
yadda ake rubuta su tare da kalmomin aikatau masu gaba ɗaya…."
|
Kuskure |
Daidai |
|
Ayyuna sa |
Ayyukansa |
|
Su ka |
Suka |
|
Mu na |
Muna |
3.0 Naɗewa
Harshen Hausa, harshe ne
da ya riga ya haɓaka ƙwarai, amma babbar matsala ita ce har yanzu rubutunsa bai zama bai
ɗaya ba. Ba Mujallar
fim kawai ba, har Malaman Hausa da Ɗaliban da Hukuma da Gidajen Rediyo da na Talabijin, da sauran
kafafen sadarwa da yawa, suna da babbar rawar da ya kamata su taka don ganin
wannan mashahurin harshe ya samu hanyar rubutu bai ɗaya a duka duniya. Ana da tsananin buƙatar yaɗuwar wannan fanni,
saboda masu sha’awar rubutu a cikin Hausa a kullum daɗa yawa suke yi. Don haka ya dace a yawaita wallafe- wallafe
cikinsa ana yaɗawa. Ita kuma Mujallar Fim, saboda irin karɓuwar da ta yi, ya dace a
ce tana bin waɗannan ƙa’idojin rubutu sau da ƙafa don ta bayar da ta ta gudunmuwar wajen samar da rubutun Hausa
ya zama bai ɗaya. Hukuma (wato gwamnati) da malamai da sauran
ɗaliban Hausa da sauran masu faɗa a ji da kuma musamman gidajen rediyo da talabijin da sauran
kafafen yaɗa labarai kamar su Jaridu da Mujallu su yi ƙoƙarin taimakawa wajen ganin wannan harshe ya samu hanyar rubutu bai
ɗaya. Haka kuma yana da kyau kamfanonin Mujallu
na Hausa su zage dantse domin ganin an magance faruwar waɗannan kura-kuren, ta hanyar ɗaukar ma'aikata ƙwararru, musamma masu takardar digiri a fannin
Hausa.
Manazarta
Abdullahi, G.W. (2006). Daidaitacciyar Hausa da ƙa'idojin rubutu. Kaduna. Olatunde Rasheed Publishing Works.
Abdullahi, Y. da Ɗangambo, A. (1986). Jagorar nazarin hausa. Zariya. Kamfanin Buga Litattafai na Nijeriya
ta Arewa.
Abdulƙadir, K.A. da Mika'il, A.M. (2017). Jagoran mai rubutun Hausa. Kano, Albarka
Publishers.
Bargery, G.P. (1934). A Hausa - English dictionary and English -
Hausa Ɓocabulary. Zaria. Ahmadu Bello University Press Limited
Nigeria.
Bello. S. (2005). Ƙa'idojin rubutun Hausa: Jagora ga marubuta. Kano. Benchmark Publishers Lid. Nigeria.
Doro, I. B. (2017,
March). Ali show ya samu haidar, kuma ya yi rashin mahaifi. Mujallar Fim, p. 36.
Muhammad, A. (2015,
June). Zee-Zee ta caza ƙwalƙwalwar masoyonta. Mujallar Fim, p. 15.
Muhammad, A. (2017, Afril).
Alƙalam ta karrama gwarzayen adabi. Mujallar Fim, p. 45.
Shehu, M. (2010). Hausa ba
dabo ba ce: Nazari a kan kura-kuren da wasu kafofin yaɗa labarai ke yi a wajen rubuce-rubucensu na Hausa cikin JOLALI, Volume
I. No. 1 School of Languages
Federal College of Education, Katsina.
Shehu, M. (2013). Hausar
rediyo: Nazarin gurɓatar ma’ana cikin matani "a rediyon
Jamhuriyar Muslunci ta Iran", cikin Ɗunɗaye Journal of Hausa Studies Vol. 1 Number 5. Sokoto, Department of Nigerian
Languages, Usman Ɗanfodiyo University.
Yahaya, I. Y. (1988). Hausa a rubuce: Tarihin rubuce - rubuce
cikin Hausa Zaria: Kamfanin Buga Litanafai na Nijeriya ta Arewa.
Yakubu, M. (2016, May). Mahaifiyar Jamila Umar Tanko ta rasu. Mujallar Fim, p. 49.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.