Citation: Dr. Ɗahiru ABDULƘADIR (2018). Ƙwaya Da Warwarar Jigon Waƙar ‘Tabban Haƙiƙan’ Ta Shehu Usmanu Ɗanfodiyo. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. 6. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
ƘWAYA DA WARWARAR JIGON: WAƘAR ‘TABBAN HAƘIƘAN’ TA SHEHU USMANU ƊANFODIYO
Dr.
Ɗahiru ABDULƘADIR
1.0 Gabatarwa
Waƙa wani sarrafaffen
harshe ne mai tsari da dokoki na musamman da al’ummar Hausa take amfani da ita
cikin hikima da basira ta yi wa kanta maganganu kan inganta rayuwarta. Ta haka
ne waƙa ta zama kafa ce ta isar da saƙonni daban-daban da
suka shafi yi da hani zuwa ga al’ummar Hausawa. A wannan takarda za a yi
sharhin waƙar ‘Tabban Haƙiƙan’ wadda Shehu Usmanu Ɗanfodiyo ya rubuta a
tsari na rubutacciyar waƙa wadda ake zaɓo kalmomi a daidaita sua tsara su cikin
azanci bisa baiti-baiti tare da amsa-amo ta hanyar amfani da dabarun jawo
hankalin mai sauraro don cim ma manufa.
1.1 Marubucin Waƙar
‘Tabban Haƙiƙan’
Mujaddadi
Shehu Usmanu Ɗanfodiyo ne ya tsara wannan waƙa mai suna ‘Tabban Haƙiƙan’ kuma ana zaton ya
yi wannan waƙa ne a Sifawa a cikin shekara ta 1809 yayin da ake
gudanar da jihadi. Shehu Usmanu ya tsara waƙar cikin harshen
Larabci, sannan ’yarsa Nana Asma’u ta fassara ta zuwa harshen Hausa. Daga
bisani kuma ɗansa Malam Isan
Kware, autan Shehu ya yi mata tahmisi a shekara ta 1832 (1247H.).
2.0 Taƙaitaccen Sharhin
Jigon Waƙar
Waƙar ‘Tabban Haƙiƙan’ cike take cunkus
da gargaɗi da tsoratarwa a kan
wasu halaye da mutane suke yi a wannan lokaci. Gundarin jigo na wannan waƙa ta ‘tabban haƙiƙan’ shi ne neman mutane
su daina ayyuka na assha, su tuba su dawo kan ayyukan salihai domin Allah ya
yafe musu, su sami tsira a lahira.
2.1 Ƙwayar Jigo
Ƙwayar
jigon wannan waƙa ta bayyana a baitit na 3 kamar haka:
3. Kui
nazar ’yan’ uwa ku samu ku duba,
Don
nasiha ku zam faɗi don muhibba,
Mui ta
bin godabe mu tsere azaba,
Duk ku
saurari za ni waƙa ku tuba,
Don ku
samu ku tsira tabban haƙiƙan.
A nan
Shehu Usmanu ya yi gargaɗi wa ’yan’uwa su
dinga yin nasiha da faɗakarwa kan a dinga
bin hanya madaidaiciya ta yadda za a iya kuɓuta daga fushin Allah da kuma azaba tasa.
Mawallafin ya daɗa bayyana ƙwayar jigon waƙar na gargaɗi yana cewa:
4. Ko
mutum ya zamo mutum mai muƙami,
Ko
sarauta gare shi ko ko adimi,
Ko
ganiyyi marowaci ko karimi,
Wanda
bai girgiza ma Sarkin Musulmi,
Shi ka
mutuwa ga jahalu tabban haƙiƙan.
5. Don ibadakka mai
yawa wadda kay yi,
Ka zamo
salihi na Allah waliyi,
Ko sani
ag gare ka tari jaliyyi,
Wanda
duk yaƙ ƙi bin hukunci da yay yi,
Ba shi
hujja ga gobe tabban haƙiƙan.
Cikin waɗannan baitoci guda
biyu Shehu Usmanu ya ja hankalin al’umma kan su girmama duk wanda Allah ya danƙa riƙon jama’a a hannunsa,
musamman Sarakunan Musulunci. Kuma a karɓi hukunci da suka yi ba don halinsu ba, sai
dai domin yin hakan bin umarni ne na Allahu, tabaraka wa ta’ala
Shi
kuma Shugaban ana so ne ya kyautata wa jama’arsa don su amince masa ko ya sami
tsira. Ga misali:
6. In
fa ka zam Imamu to yo karimci,
Nai
foron ka ya da hanyab bahilci,
Don ka
samu ga ’yan’adam duka aminci,
Wanda
yaz zamu Imamu yay yo adalci,
Shi da
inwa ga gobe tabban haƙiƙan.
7. In
daɗa ka zamo Imamun
mutane,
To
tsare alhakinsu balle ubanne,
Ka ji
kyauta daɗa fa don kar ka ƙone,
Wanda
yaz zam Imamu don cin mutane,
Shi
wuta kan ci gobe tabban haƙiƙan.
11.
Masu iko su ba da himma su kyauta,
Kun
jiya masu ji daɗa kada ku ɓata,
Ba da
tsanini garin biɗowab bukata,
Masu
matsuwat talakka ko don sarauta,
Su ka
matsuwa ga gobe tabban haƙiƙan.
2.2 Warwarar Jigon Waƙar ‘Tabban Haƙiƙa’
Tun a
tashin farko a wannan waƙa, Shehu Usmanu ya yi kira ga shugabanni su zamo masu
adalci, kuma yin haka a al’amuran iko da shi ne a wurin Allah za a iya samun
rahamarsa. Amma dukkan shugabancin da aka gudanar bisa musguna wa mabiya, to,
fa sakamakonsa azabar Allah.
Waƙar nan kuma ta ƙara fito mana da wata
mummunar hanya da wasu kan bi domin su zama shugabanni. Ga abin da Shehu Usmanu
yake faɗi:
8.
Wanda duk yab biɗo ga rainai sarauta,
Don shi
sam dukiya shi samo bijinta
Don shi
kurɗa daɗa cikin masu cuta,
Masu
aza dukiya garin ban sarauta,
Babu
shakka su ƙuna tabban haƙiƙan.
A baitin nan da ya gabata an yi nuni na illar
da ke tattare da neman shugabanci domin burin tara dukiya. Masu irin wannan ɗabi’a kuwa za su auka
cikin ƙunar wuta.
Sannan
Shehu Usmanu ya ci gaba da faɗakar da mu kan amsa kiran mai shara’a wanda abu ne na
ibada. Ga abin da waɗannan baitoci suke
nunawa.
16. In
fa Alƙali yai kira zo ka karɓa,
Ƙin
zuwa cana Jalla shi anka saɓa,
Kama
hanya zuwa garai kar ka raɓa,
Wanda
Alƙali
yak kira yaƙ ƙi karɓa,
Shi
wuta kan kiraya tabban haƙiƙan.
18. In
fa Alƙali can cikin nashi hukumi,
Yaƙ ƙi bin godabe ku san
ya yi zulmi,
Gobe
can Lahira ana sa shi ƙuƙumi,
In fa
Alƙali
kul fa ya sake hukumi,
Kafira
na da amdu tabban haƙiƙan.
Amsa kiran mai
hukumci wato Alƙali a kowane matsayi wajibi ne. An kira mutum ne kuwa a
matsayin wanda ake tuhuma ko mai ba da shaida. Irin wannan hukunci ba wai sai a
ɗakunan da aka gina
domin shari’a kawai ba, har da kwamitoci da a kan naɗa a makarantu da
ma’aikatu don bin kadin waɗanda aka zalunta. Duk wanda ya ƙi amsa kiran mai
shara’a to a gaskiya ba makawa zai shiga wuta.
Hakazalika
duk mai hukunci da ya bi son ransa yayin gudanar da wani hukunci to azabar
Allah na nan tana jiran sa. Tafarki madaidaici don yanke hukunci shi ne bin
abin da Allah ya ce a yi ko a bari.
Har ila
yau akwai nuni a kan tsare alƙawari da sanin matsayin ɗan’uwa mumini. Ga
misali a waɗannan baitoci.
21.
Wanda yak ka kwance alƙawari ya yi zambo,
Dud da
mai rena mumini sai shi tuba,
Ya yi
saɓo ina kamatai ku
duba,
Mai fa
bautad da ɗa shi shawo azaba,
Shi ka
bautar wuta fa tabban haƙiƙan.
22.
Masu cin kura kasuwa duk akwai su,
Wansu
keri su kai su samo bukinsu
Wansu
na nan ina faɗa ma kamassu,
Masu
cin dukiya ta baital wasunsu,
Su wuta
kan ci gobe tabban haƙiƙan.
Baitocin nan sun tabbatar da ƙin cika alƙawari laifi ne mai
girma, haka maɗaukar ɗan’uwa mumini a bakin
baza. Maganin wannan shi ne a tuba a gyara. Sannan ƙarin kuɗi cikin sha’anin
kasuwanci laifi ne mai girma, haka kuma ƙarya ko cin dukiyar
baitil-mali duka laifuka ne, azaba na nan jiran mai aikata su idan bai tuba ya
daina ba.
Shehu
Usmanu ya kalli daraja da matsayin mata sai bai bar su a gefe ba. Dangane da
abubuwan da suka shafi mata Shehu Usmanu yana cewa:
38.
Wansu can gobe za suna har lahira,
An ƙuƙumce su sun ƙi tun nan su gyara,
Su ka
sha gobe can bugu har su ƙara,
Dud da
matan da ke fita ba lalura,
Ba su
tsira ga gobe tabban haƙiƙan.
39. Dud
da kau mai matse adimi ga bashi,
Dud da
kau mace wadda tat tar da kishi,
An yi
foronta babu kyawo ta bar shi,
Hakana
mace mai fa kwarcen kiyoshi,
Gobe
ana zallata ta tabban haƙiƙan.
Dubi kuma wani gargaɗi da Shehu Usman ya
yi a baitocin da suka gabata kan fitar mace daga gidan mijinta babu dalili da
ya zama tilas, laifi ne babba, wanda zai kai ta ga shiga wutar sa’ira. Ashe ke
nan gaskiyar masu azanci da sukan ce, darajar mace ɗakinta. Mawallafin
wannan waƙa ƙarara ya nuna kishi ba shi da amfani don haka a guji yin
sa, saɓanin haka kuwa za a
iya saduwa da azabar Allah a ranar lahira.
Kuma
Shehu Usmanu ya yi wani nuni a kan da illar da ke tattare da ƙwace da zalunci da
kuma ɓoye ganima ta yaƙi kamar dai yadda
yake ambatawa a baitocin da suke tafe kamar haka:
26.
Lokacin nan na cin gari ba da zulmu,
Babu
kyawo haƙiƙatan nan gare mu,
Wansu
na nan suna ta yi nai cikinmu,
Masu ƙwace ma wanda yaf
fara kamu,
Su wuta
kan fa ƙwace tabban haƙiƙan.
27. Ba
da ɓoyon fa dukiya babu
shakki,
Ai ta
yaƙi
a kai ta duk inda Sarki,
Wansu
na nan haƙiƙan masu tarki,
Masu
hana airabo da khumsi ga yaƙi,
Su wuta
ar rabon su tabban haƙiƙan.
28. Can
ga yaƙi idan fa an sami sa’a,
Anka
sam bai walau na nan nan a bai’a,
Wansu
nan ba su bin tafarkin shari’a,
Masu
zafi su faɗa bai ba bara’a,
Su ka faɗa wuta fa tabban haƙiƙan.
Waɗannan baitoci sun
fito da illar fin ƙarfi, musamman a ƙwace abin da ɗan’uwa ya samu
lokacin yaƙi. Haka nan ba ya bisa ƙa’ida mayaƙa kowa yai gamon
kansa da duk dukiyar da ya samo lokacin yaƙi. Ballantana kuma
mata waɗanda ake kamawa a
ganimar yaƙi sai wasu su mayar da su nasu har su dinga faɗa musu ba su yi
bara’a ba. Akwai tsayayyen tafarki na raba ganimar yaƙi bisa shari’a.
A waƙar, har wa yau, Shehu
Usmanu ya taɓo al’amarin zama da
iyali sannan da haƙƙin maƙwabtaka, yana faɗin:
36.
Wanda bai tuba kun ji haƙƙan shi ƙuna,
Kun
jiya wa’azu na ku zam yin fa sauna,
Kada ku
ɓoye ma kowanne ko
zuru na,
Hakana
wanda yaƙ ƙi daidaita kwana,
Gobe
ana karkace shi tabban haƙiƙan.
Wajibi ne ga duk
mijin mata biyu ko abin da ya fi haka ya daidaita kwana a tsakaninsu. Duk wanda
bai yi haka ba, ya yi zalunci, kuma ko shakka babu zai ɗanɗana azabar Allah. A
baiti na gaba ya yi maganar sata kamar haka:
37.
Wansu himmarsu ba su ci sai ga ƙwace,
Wansu
ko na jirin a ɓoye su sace,
Wansu
sata sukai suna nana ƙwace,
Masu ɗamre miji su ƙulla da kwarce,
Su akan
ɗamre gobe tabban haƙiƙan.
Mujaddadi Shehu
Usmanu ya nuna mana a cikin al’umma akwai waɗanda ke rawar ƙafa domin yin sata.
Ba sa wani kazarkazar sai sun laluba sun ɗauke kayan wani da ya adana. Haka nan akan
sami mata da kan sa mazansu cikin wani hali na cutarwa. Duka yin hakan ba shi
da kyau. In an ƙi bari, to da ma Hausawa na cewa, ‘abin da aka shuka, shi
ake gurba’.
Akwai
kira na neman ilimi da Shehu Usmanu ya yi a cikin ƙarfafawa kuma ya
tabbatar da shi ne ginshiƙin ci gaban rayuwa. Ga wani baiti da ya faɗa a kan haka:
31. Kui
karatu zumai ku san tar da ilmi,
Shi ka
ba ɗan’adam shi zam mai
muƙami,
Kada ka
zamna cikin waɗanda bas u san ta
komi,
Masu ƙwace cikin ƙasaisan Musulunci,
Gobe za
su zo wuta fa tabban haƙiƙan.
Wajibi mutum ya
kasance yana neman ilimi kowane lokaci, ko kuma ya zama kusa da masani, amma
kada ya yi nesa da su. Yin haka shi ne ginshiƙin ci gaban al’umma.
Shehu Usmanu kuma yana nanata kira a wurare daban-daban cikin waƙar kan abubuwan da
yake zayyanawa a matsayin gargaɗi ga jama’a. Ya kuma ƙara jan hankali na
mutane da a tubadomin Allah. Idan har an yi hakan, to za a sadu da rahamar
Ubangiji, kamar dai yadda ya gabata cikin baiti na 46:
46.
’Yan’uwa na cika daɗa kun ji haƙƙan,
Don ku
karɓa cikin zukatanku haƙƙan,
Gaskiya
na faɗi ga nau kun ji haƙƙan,
Ya
jama’a ku tuba don wanda haƙƙan,
Yay yi
tuba shi tsiri tabban haƙiƙan.
3.0 Kammalawa
Kamar
yadda bayanai suka gabata, awannan takarda an yi nazari ne na gundarin jigo na
waƙar
‘Tabban Haƙiƙan’ ta Mujaddadi Shehu
Usmanu Ɗanfodiyo, sannan aka kuma yi bayani na warwarar ƙananan saƙonnin da waƙar ta yi magana a
kansu. Waƙar ta yi gargaɗi ne da nuni cikin faɗakarwa a kan dukkan
dangogi na rayuwar mutum, Musulmi. Waƙar ta kawo yadda za a
yi shugabanci da yanayin biya da zaman aure da na maƙwabtaka da illar
zalunci. A waƙar, har wa yau, an nemi al’umma ta himmatu ga yin ilimi
da sauran abubuwan da suka wajaba Musulmi ya nema.
An lura
wannan waƙa cike take da baƙin kalmomi, musamman
daga harshen Larabci da kuma ambaton nassoshin Alƙur’anida na hadisai. Haka kuma waƙa ce wadda ta farfaɗi tsagwaron
hukunce-hukunce na shari’a na yi da bari da kuma sakamakon da za a samu idan an
yi da abin da za a cim masa na azaba idan ba a yi ba.
Hakazalika,
an fahimci idan aka yi aiki da darussan da wannan waƙa take koyarwa za a
yi rayuwa mai sauƙi, ba tare da shiga cikin wata tsangwama ba. Sannan kuma
za a sami albarkatun rayuwa ta kowane gefe na hidimomi na zamantakewar al’umma.
Allah ya sa mu dace, mu yi gam-da-katar da sa’adar rayuwa,
MANAZARTA
Auta,
A. L. (2017). Faɗakarwa a rubutattun
waƙoƙin Hausa. Kano: Bayero University Press.
Gusau,
S.M. (2015). Mazhabobin ra’i da tarke a
adabi da al’adu na Hausa. Kano: Century Research and Publishing Limited.
Junaidu,
I, & ’Yar’aduwa, T.M. (2007). Harshe
da adabin Hausa a kammale: don manyan makarantun sakandare. Ibadan:
Spectrum Books Limited.
Ɗangambo,
A. (2007). Ɗaurayar gadon feɗe waƙa (sabon tsari). Kano: K.D.G. Publishers.
Ɗangambo,A.
(2008). Rabe-raben adabin Hausa (sabon
tsari). Zaria: Amana Publishers Limited.
Mukhtar,
Isa (2005). Bayanin rubutattun waƙoƙin
Hausa.
Abuja: Countryside Publishers Limited.
Sa’id,
B. (2016). Rubutacciyar waƙar
Hausa: ma’auninta da amsa-amonta da ire-irenta. Kano: Bayero University
Press.
Yahya,
A.B. (1997). Jigon nazarin waƙa. Kaduna: Fisbas
Media Services.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.