𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum, don Allaah tambaya ce da ni: Mene ne hukuncin mutumin da yake jan mutane limanci a sallah, amma a wajen ɗagowa daga ruku'u sai ya ce: ‘ALLAHU AKBAR’ a maimakon ya ce: ‘SAMI'AL LAAHU LI MAN HAMIDAH.’Sannan kuma mene ne hukuncin faɗin: ‘SAMI'AL LAAHU LI MAN HAMIDAH’a sallah?
HUKUNCIN WANDA YAKE FAƊIN "ALLAHU AKBAR"
YAYIN ƊAGOWA
DAGA RUKU'U:
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
W alkm slm w rhmt laah.
Da farko wajibi ne
kowannenmu ya san cewa abin da ya tabbata a Sunnah Sahihiya, kuma malamai suka
yiittifaaƙia kansa shi ne:
Duk lokacin da liman ko mai
Sallah shi kaɗai yake ɗagowa
daga ruku'u sai ya ce:'SAMI'AL LAAHU LI MAN HAMIDAH'.Idan kuma ya daidaita a
tsaye sai ya ce:'RABBANAA LAKAL HAMD'ko'RABBANAA WA LAKAL HAMDU'ko'ALLAAHUMMA
RABBANAA LAKAL HAMDU'ko'ALLAAHUMMA RABBANAA WA LAKAL HAMDU.'
Amma game da mamu mai Sallah
a bayan liman ne malaman suka sha bamban. Kuma abin da ya fi bayyana, kuma ya
fi zama daidai a fahimtarmu daga cikin maganganunsu shi ne:
Shi ma dai yadda limaminsa
ya yi haka zai yi, watau ya faɗi'SAMI'AL LAAHU LI MAN
HAMIDAH'a lokacin ɗagowa, kuma ya faɗi'RABBANAA
WA LAKAL HAMDU'bayan ya gama ɗagowa. Saboda Hadisin
Al-Bukhaariy wanda a cikinsa Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya
ce:
صَلُّوا كَمَا رَأَيْتُمُونِي أَصَلِّي
Ku yi Sallah kamar yadda
kuka ganni ina yin sallar.
Kuma da wanda ya ce:
إِنّمَا جُعِلَ الْإِمَامُ لِيُؤْتَمَّ بِهِ
An sanya Liman ne kaɗai
domin a yi koyi da shi.
Kuma amma game da hadisin da
ya ce:
إِذَا قَالَ ألْإِمَامُ: (سَمِعَ اللهُ لَمَنْ حَمِدَهُ)فَقُولَوا: (رَبَّنَا وَلَكَ الْحَمْدُ)
Idan Liman ya ce: 'SAMI'AL
LAAHU LI MAN HAMIDAH'sai ku ce:'RABBANAA WA LAKAL HAMDU'
Malamai irinsu Al-Imaam
As-Suyuutiy a cikinAl-Haawiy Lil Fataawiysun nuna cewa, bai saɓa wa
abin da ya gabata ba, saboda wasu bayanai ingantattu da ya zo da su a can.
Game da hukuncin faɗin'SAMI'AL
LAAHU LI MAN HAMIDAH'kuwa, abin da ya fi bayyana daga maganganun malamai shi
ne: Shiwajibi ne, ko kumaSunnah Mu'akkadahdomin hadisin da Al-Imaam Abu-Daawud
ya riwaito daga hadisin mutumin nan Mai Munana Sallarsa, inda Annabi (Sallal
Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya umurce shi da faɗin
wannan zikirin a lokacin ɗagowa daga ruku'u.
Don haka, limamin da ba ya
faɗin
wannan zikirin a lokacin ɗagowa daga ruku'u, kuma yake
musanya shi da wani zikirin daban, sai a ce ya kayar da wannan wajibi kenan
daga cikin sallarsa. Kuma dole a yi masa nasiha domin ya gyara.
Idan kuma ya ƙi yarda da nasihar, ya ci gaba da wannan
ɓarnar,
to sallarsa tana iya ɓaci, saboda wulaƙanta surar sallar da ya yi.
Wanda ya yi Sallah a bayan
irin wannan limamin sallarsa ta yi, matuƙar
dai shi ya faɗi abin da yake daidai a lokacin ɗagowarsa
da lokacin tsayuwarsa, saboda hadisin da Al-Imaam Al-Bukhaariy ya riwaito cewa
Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:
Suna yi muku limanci; to
idan suka dace, duk kun dace. Idan kuwa suka yi ba daidai ba, to kun dace, su
kuma sun kauce wa daidai.
Wal Laahu A'lam.
Sheikh Muhammad Abdullah
Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.