Ticker

6/recent/ticker-posts

Daidaita Sahu Yayin Salla

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Daga ina ya fi dacewa a fara sahun sallah na-biyu, daga tsakiya ko daga dama?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.

Abu na-farko dai da ya dace kowannenmu ya sani shi ne, ba a fara sahu na-biyu sai in sahu na-farko ya cika, kuma ba a fara na-uku har sai na-biyu ya cika, haka nan dai har zuwa ƙarshe. Al-ImaamAbu-Daawud (671)ya riwaito daga Anas Bn Maalik (Radiyal Laahu Anhu) daga Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

« أَتِمُّوا الصَّفَّ الْمُقَدَّمَ ، ثُمَّ الَّذِى يَلِيهِ ، فَمَا كَانَ مِنْ نَقْصٍ فَلْيَكُنْ فِى الصَّفِّ الْمُؤَخَّرِ »

Ku cika sahu na-gaba, sai kuma wanda yake bin sa, kuma duk abin da zai rage sai ya kasance a sahu na-ƙarshe.

Haka kumaAl-Imaam Muslim (996)ya riwaito daga Sahabi Jaabir Bn Samurah (Radiyal Laahu Anhu), daga Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

« أَلاَ تَصُفُّونَ كَمَا تَصُفُّ الْمَلاَئِكَةُ عِنْدَ رَبِّهَا »

Ba za ku yi sahu kamar yadda Mala’iku suke yin sahu a wurin Ubangijinsu ba?

Da suka tambaye shi, yadda Mala’iku suke yin sahu a wurin Ubangijinsu, sai ya ce:

« يُتِمُّونَ الصُّفُوفَ الأُوَلَ وَيَتَرَاصُّونَ فِى الصَّفِّ »

Suna cika sahuhuwan farko, kuma suna haɗuwa da juna a cikin sahu.

Abu na-biyu: Malamai sun nuna akwai falala a gefen dama na sahu, saboda hadisin daAl-Imaam Abu-Daawud (676)ya riwaito da isnadinsa kyakkyawa har zuwa ga Ummul-Mu’mineen A’ishah (Radiyal Laahu Anhaa), daga Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

 « إِنَّ اللَّهَ وَمَلاَئِكَتَهُ يُصَلُّونَ عَلَى مَيَامِنِ الصُّفُوفِ »

Haƙiƙa! Allaah da Malaikunsa suna yin salati ga geffan dama na sahuhuwa.

Sai dai kuma kodayake hadisin yana da matsala ta mataninsa, don haka ne ma Al-Imaam Al-Mujaddid Al-Albaaniy ya saka shi a cikinDa’eef Abi-Daawud: 104, amma kuma akwai wasu hadisan da ba su da wata matsala, waɗanda kuma suka zo a kan haka, kamar hadisin Al-Baraa’ Bn Azib (Radiyal Laahu Anhu) wanda Al-Imaam Al-Albaaniy ya inganta shi a cikin Sahih Abi-Daawud: 628 mai lafazin:

كُنَّا إِذَا صَلَّيْنَا خَلْفَ رَسُولِ اللَّهِ - صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ - أَحْبَبْنَا أَنْ نَكُونَ عَنْ يَمِينِهِ ، فَيُقْبِلُ عَلَيْنَا بِوَجْهِهِ - صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ

Mun kasance idan muka yi sallah a bayan Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) mukan so mu zama ta gefen damansa, sai ya fuskance mu da fuskarsa (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) (bayan sallama).

Saboda irin waɗannan hadisan ne wasu malamai (Allaah ya saka musu da alkhairi) suke ganin a fara sahu na-biyu daga gefen daman masallaci. Wannan fahimta ta iya zama daidai ce.

Amma kuma Al-Imaam Muslim ya ƙulla babi a cikin Sahin Littafinsa wanda ya ba shi suna:

باب تَسْوِيَةِ الصُّفُوفِ وَإِقَامَتِهَا ، وَفَضْلِ الأَوَّلِ فَالأَوَّلِ مِنْهَا ، وَالاِزْدِحَامِ عَلَى الصَّفِّ الأَوَّلِ ، وَالْمُسَابَقَةِ إِلَيْهَا ، وَتَقْدِيمِ أُولِى الْفَضْلِ ، وَتَقْرِيبِهِمْ مِنَ الإِمَامِ

Baab: Daidaita sahuhuwa da tsayar da su, da falalar sahun farko sai mai bin sa a cikin haka, da cunkoso a kan sahun farko, da yin tsere da juna zuwa gare shi, da gabatar da ma’abuta falala a wurin haka, da kuma kusancinsu ga liman.

A ƙarƙashin wannan babin sai kuma ya kawo hadisai masu yawa, a ciki har da wannan da ya riwaito daga Sahabi Abu-Saeed Al-Khudriy (1010) daga Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) a lokacin da ya ga Sahabbansa suna yin baya-baya a ƙarshen masallaci, sai ya ce:

« تَقَدَّمُوا فَائْتَمُّوا بِى وَلْيَأْتَمَّ بِكُمْ مَنْ بَعْدَكُمْ »

Ku gabato ku yi koyi da ni, sai kuma waɗanda suke a bayanku su yi koyi da ku.

Daga wannan hadisin, idan mutane biyu suka zo kafa sahu sai ɗayansu ya tsaya a saitin liman, ɗayan kuma ya koma ƙarshen gefen dama na masallacin a kan sahun

1. Wanne ne daga cikinsu za a ce ya bi umurnin wannan hadisin a fili?

2. Wanne ne za a ce ya gabata ko ya yi kusa da liman?

3. Sannan kuma wanne ne yake a matsayin ji da ganin liman yadda ya kamata?

4. Kuma wa za a ce yana iya koyi da Limamin yadda ya dace?

5. Wanne ne za a ce ya zama abin koyi ga na-baya a haƙiƙa?

A fahimtarmu, wanda ya tsaya a saitin liman shi ya fi a cikin duk waɗannan tambayoyin fiye da wanda ya je gefe.

Don haka dai idan aka zo dasa sabon sahu na-biyu, gara a fara a saitin liman amma ta gefen dama kaɗan, domin a samu haɗa falalar damaitawar da kuma kusanci da limamin, in shaa’al Laah.

Allaah ya datar da mu.

 Wal Laahu A’lam.

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam𝐃𝐀𝐆𝐀 𝐈𝐍𝐀 𝐒𝐀𝐇𝐔 𝐘𝐀𝐊𝐄 𝐅𝐀𝐑𝐀𝐖𝐀?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum. Malam sahun Sallah ta dama za a fara ne ko ta hagu?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikum assalam. To ɗan'uwa sahun da yake bin liman zai fara ne daga bayan liman, ma'ana a sanya liman a tsakiya, saboda faɗin Annabi (Sallallahu alaihi Wasallam): "Masu hankali daga cikinku, su bi bayana", kamar yadda Muslim ya rawaito a Hadisi mai lamba ta 116. Da faɗin Anas (R.A.) lokacin da yake ba da labarin ziyarar da Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya kai gidansu: "Sai muka tsaya ni da marayan a bayansa", kamar yadda Bukhari ya rawaito a Hadisi mai lamba ta 694. Daga nan kuma sai a ci gaba da cika shi ta ɓangaren dama.

Haka nan ake so sahu na biyu shi ma ya kasance, ya fara daga tsakiya ya tafi zuwa dama, saboda faɗin Bara'u ɗan Azib (R.A.): "Mun kasance idan muka yi sahu a bayan Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) mu kan so mu kasance a damansa, ya fuskanto mu da fuskarsa", Muslim a Hadisi mai lamba ta 709.

Allah ne mafi sani.

𝑨𝒎𝒔𝒂 𝒅𝒂𝒈𝒂 𝑫𝒓. 𝑱𝒂𝒎𝒊𝒍𝒖 𝒀𝒖𝒔𝒖𝒇 𝒁𝒂𝒓𝒆𝒘𝒂

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa... 

Post a Comment

0 Comments