𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam Alaikum. Ni ne na ɗauke abin wani, na je na sayar ba tare da ya sani ba. Yanzu kuma ya rasu, shi ne nake son in biya shi. To, zan biya asalin farashin abin ne, ko kuwa yadda na sayar da shi?
BIYA ABIN DA KA ƊAUKA WA MAMACI
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa
Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.
Ɗaukar
kayan wani mutum ba da yardarsa da izininsa ba haram ne. Allaah Maɗaukakin
Sarki ya ce:
یَـٰۤأَیُّهَا ٱلَّذِینَ ءَامَنُوا۟ لَا تَأۡكُلُوۤا۟ أَمۡوَ ٰلَكُم بَیۡنَكُم بِٱلۡبَـٰطِلِ إِلَّاۤ أَن تَكُونَ تِجَـٰرَةً عَن تَرَاضࣲ مِّنكُمۡۚ
Ya ku waɗanda
suka yi Imani! Kar ku ci dukiyoyinku a tsakaninku a bisa zalunci, sai dai in ya
kasance a bisa ciniki ne, a bisa yarda daga gare ku. (Surah An-Nisaa’i: 29).
Kuma Manzon Allaah (Sallal
Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:
« فَإِنَّ دِمَاءَكُمْ وَأَمْوَالَكُمْ وَأَعْرَاضَكُمْ بَيْنَكُمْ حَرَامٌ كَحُرْمَةِ يَوْمِكُمْ هَذَا ، فِى شَهْرِكُمْ هَذَا ، فِى بَلَدِكُمْ هَذَا »
Domin jinainanku da
dukiyoyinku da mutuncinku haram ne a tsakaninku, kamar haramcin yininku wannan,
a cikin watanku wannan, kuma a cikin garinku wannan. (Sahih Al-Bukhaariy:
67,105, 1739; Sahih Muslim: 1218, 1679).
Kuma wajibi ne ga wanda ya
aikata wannan ta’asar ya tuba ga Allaah (Tabaaraka Wa Ta’aala) a kan haka, don
ya saɓa
masa. Sannan kuma dole ya mayar da abin da ya ɗauka
ga mai shi. Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:
« لاَ يَأْخُذَنَّ أَحَدُكُمْ مَتَاعَ أَخِيهِ لاَعِبًا وَلاَ جَادًّا ، وَمَنْ أَخَذَ عَصَا أَخِيهِ فَلْيَرُدَّهَا »
Kar ɗayanku
ya kuskura ya ɗauki kayan ɗan’uwansa
ko da wasa ne ko da gaske. Kuma duk wanda ya ɗauki
sandar ɗan’uwansa,
to ya mayar da ita. (Abu-Daawud: 5003; At-Tirmiziy: 2160; Ahmad: 4/221; kuma
Al-Albaaniy ya hassana shi a cikin Sahih At-Targheeb: 2808).
Malamai (kamar a cikin Tamaamul
Minnah: 4/98-100) suka ce: A ƙarƙashin wannan akwai wasu abubuwan lura,
kamar haka:
1. Ɗawainiya da wahalhalun mayar da kayan
duk a wuyan shi da ya ɗauke su suke, ba a wuyar mai
kayan na asali ba.
2. Idan kuma abin da ya ɗauken
ya lalace ko ya salwance, to wajibi ne ya biya irinsa daidai-wa-daida, ko kuma
ya biya ƙimarsa na kuɗi.
3. Sannan kuma ko da abin da
ya ɗauka
ya ƙaru ta hanyar hayayyafa ko ribar ciniki
da makamantan hakan, to wannan ƙarin
ma na mai kayan ne, kuma dole ya mayar masa.
4. Sannan kuma idan wani abu
daga cikin abin da ya ƙarun
ya salwanta a hannunsa, to shi ma dole ya biya mai kayan. Annabi (Sallal Laahu
Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:
« لَيْسَ لِعَرَقٍ ظَالِمٍ حَقٌّ »
Babu wani haƙƙi ga jijiyar zalunci. (Abu-Daawud:
3073; At-Trimiziy: 1378; kuma Al-Albaaniy ya sahhaha shi a cikin Al-Irwaa’u: 1520).
Yanzu da mai kayan ya rasu,
sai ya ci gaba da roƙa
masa gafara, saboda cutar da shi da ya yi. Sannan kuma sai ya mayar da dukkan
haƙƙoƙin ga magadansa.
Allaah ya ƙara mana ilimi mai amfani.
Wal Laahu A’lam.
Sheikh Muhammad Abdullaah
Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.