𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Asalamu alaikum. Dan Allah malam ina da tambaya. Idan Mutum ya yi wasiyya a kan kar a raba masa gado har sai an aurar da yaransa da suka rage. Sai wani kuma acikin 'ya'yansa ya ce shi idan aka yi haka bai yafe ba. Muna neman fatawa a kai.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikis salam wa
rahmatulLahi wa barakatuhu.
Ita dai wasiyyah tana daga
cikin abubuwan da shari'ar addinin Musulunci ta shar'anta. Wasu daga cikin
Malamai kamar su Ibnu Hazmin da Ibnu Shihab Azzuhriy sun tafi akan cewa yin
Wasiyyah wajibi ne akan duk musulmin da ya mallaki wani abu na dukiya wanda za
a iya raba gadonsa bayan mutuwarsa.
Wasu Malaman kuma suna ganin
cewa yin wasiyyah zuwa ga iyaye da kuma makusanta waɗanda
ba zasu ci gadon mutum ba, shi ne kaɗai
wajibi. Wannan ita ce fatawar su Imam Ƙataadah
da Masruƙ da Iyaas da Ibnu Jareer (Allah yai
rahama garesu).
Wasu Malaman kuma suna ganin
cewa hukuncin yin wasiyyah yana bambanta ne bisa gwargwadon hali ko yana yin da
mutum ya tsinci kansa. Wani lokacin takan zama wajibi ayita, wasu lokutan kuma
Mustahabbi.
Misali wanda ake binsa
bashi, ko aka bashi ajiyar wata amana, to wajibi ne gareshi ya yiwa magadansa
wasiyyar cewa su biya masa bashin da ake binsa, ko kuma su mayar da amanar nan
dake hannunsa. Wannan shi ne ra'ayin Jagororin mazhabobin nan guda huɗu na
Ahlus Sunnah wal jama'ah. Kuma shi ne ra'ayin Mazhabar Zaidiyyah daga ɓangaren
Mazahibu na Shi'ah.
Wasiyyah kuma takan zama
haramun idan ya zamto anyita da mummunar manufa kamar tauye hakki ko hana
hakkokin wasu daga magadan, ko kuma idan aka yita domin assasa wasu abubuwan da
shari'ah ta haramta.
Wasiyyah tana da wasu Ƙa'idodin bayan wannan. Shi ne kamar
yadda ya zo acikin wani hadisi Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam Ya ce
"BA'A YIN WASIYYAH GA MAGAJI". (Ahmad Abu Dawud da Tirmidhiy ne suka
ruwaitoshi).
Wato duk wanda ya kasance
yana cikin masu cin gadonka, babu damar ka bar wasiyyar cewa shi za a bama gona
kaza ko gida kaza, ko abashi Miliyan kaza daga cikin dukiyarka bayan ka rasu.
Kuma babu damar ka keɓance shi da wani abun amfani
ko amfanarwa domin kansa shi kaɗai.
Manzon Allah Sallallahu
Alaihi Wasallam acikin wani hadisin da Imam Abdurrazzaƙ ya ruwaito acikin Almusannaf nashi cewa:
"Mutum yakan kasance yana aikata irin ayyukan mutanen kirki har tsawon
shekara saba'in amma idan ya aikata wauta acikin wasiyyarsa sai wannan ya janyo
masa mummunar cikawa sai ya shiga wuta".
Sa'eed bn Mansur ya ruwaito
ta hanyar Abdullahi bn Abbas (radhiyalLahu anhuma) yana cewa "CUTARWA
ACIKIN WASIYYAH YANA DAGA CIKIN MANYAN LAIFUKA".
A takaice dai, ita wannan
wasiyyar da kika ce mamacin nan yayi, ba halastacciya bace bisa dokokin addinin
Musulunci, kuma ta saɓa da Umurnin Allah da
Manzonsa (Sallallahu Alaihi Wasallam). Don haka haramun ne a zartar da ita.
Wajibi ne ku raba gadon nan a bama kowanne mai gado rabonsa da Allah ya riga ya
bashi.
Jinkirin raba gado zalunci
ne da wasu suke fakewa dashi suna cin hakkin masu hakki. Sannan mamaci fa bashi
da wani sauran hakki acikin dukiyar da ya bari, bayan an biya masa basussukan
dake kansa sai kuma zartar da halastattun wasiyyoyinsa, shikenan. Amma gaba ɗayan
sauran dukiyar nan ta magada ce. Kuma bashi da damar tsara musu lokaci ko yana
yin yadda zasu raba gadonsu.
Shi wannan ɗan
nasa da ya bukaci azo araba a bashi nasa rabon, ya yi daidai. Su kuwa waɗannan
yaran da mamacin ya ce ayi aurensu da dukiyar da ya bari, ai ba nasu ne su kaɗai
ba. Don haka ba za a yi biyayya ga wannan umurnin nasa ba. Umurnin Allah da
Manzonsa (Sallallahu Alaihi Wasallam)kadai za a bi anan.
Inama da cewa ya yi Idan
lokacin auren nasu yayi, dukkan 'ya'yansa su haɗa
kai su ba da gudunmuwa su aurar dasu, to da wannan ya fi daidai kuma ya fi alkhairi.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.