𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam Ya hukuncin wanda ke bin liman kuma har aka gama sallar shi bai karanta fatiha ba.?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuh
karatun fatiha rukunine daka
cikin rukunan sallah akan mamu da liman da wanda zaiyi sallah shi kaɗai,
saboda faɗin Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam (Babu
sallah ga wanda bai karanta fatiha ba) Imamul bukhari yafitar da wannan hadisi
ababin kiran sallah (714). Amma karatun fatiha ga wanda yake bin liman asallar
da ake bayyana karatunta akwai maganganu biyu na malama:
1. Magana tafarko: suka ce
wajibine karatun fatiha ga wanda yake bin liman asallah, dalili akan haka suka
ce faɗin
maganar manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam daya ce (Babu sallah ga wanda
bai karanta fatiha ba), saboda Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam lokacin da
yake koyar da wanda bai iya sallah ba ya umarceshi da karantata. Ya inganta
daka Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam yakasance yana karanta ta akowacce
raka'ar sallah.
Ibnhu hajar Rahimahullah ya
ce: Acikin fathul baary, hakika ya tabbata umarnin karatun fatiha akan mamu
asallar da ake bayyana karatunta batare dawani kaidi ba, hakan yanan cikin
abunda imamul bukhary yafitar, da turmuzi da ibnu hibban daka ruwayar makhuul,
daka mahmud binu rabee'i binu ubadah, watarana Annabi Sallallahu Alaihi
Wasallam karatu yai masa nauyi asallar asuba, lokacin da'aka idar da sallah sai
Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce: watakila kuna yin karatu abayan
limaminku? Sai sahabbai suka ce eh, sai Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce:
kada kudunga aikata hakan saifa karatun fatiha saboda babu sallah ga duk wanda
bai karantata ba.
2. Magana ta biyu: suka ce
karatun liman shi ne karatun mamunsa dalili akan haka suka ce faɗin
Allah maɗaukakin
sarki:
وَإِذَا قُرِئَ الْقُرْآنُ فَاسْتَمِعُوا لَهُ وَأَنْصِتُوا لَعَلَّكُمْ تُرْحَمُونَ ٢٠٤
Idan Ana karanta Alƙur'ani kuyi sauraro na fahimta, kuma
kuyi shiru, shiru na nutsuwa ko kwa samu Rahamar Allah. (Surah Al-A'raf - 204).
Ibnu hajar ya ce: Masu cewa
karatun fatiha yafadi akan mamu daka malikiyyah sunkafa hujja da wani hadisi
dayake cewa (Idan ana karanta Alƙur'ani
kuyi shiru) kuma hadisine ingantacce muslim ya ruwaitoshi daka hadisin Abu musa
Al Ash'ary Allah yakara yarda dashi.
Waɗanda
suke fatawa da wajabcinta suntafi akan cewa mutum zai karantata bayan liman
yagama karatun fatiharsa atsakanin ɗan
shirun dayake kafin yashiga karatun surah, sai ka karanta duk da wannan shirun
da liman yake malamai sun ce bidi'ane baida asali, ibnu hajar ya ce: mamu
"zaiyi shiru idan liman yana karanta fatiha, shi mamu zai karanta idan yai
shiru"
Sheik bin baaz ya ce: Abunda
ake nufi da shirun liman shi ne shirun da mamu zai iya karanta fatihar, ko
bayanta, ko acikin surar datake bayan fatihar, idan liman baya shiru ɗin
to abunda yake wajibi akan mamu shi ne karanta fatihar koda liman yana karatun
surah ne, wannan shi ne mafi ingancin magana cikin maganganun malamai, fatawa
sheik bin baaz (221).
An tambayi majalisar fatawa
da ilmi ta kasar saudiyyah irin wannan tamabaya sai suka amsa dacewa: Magana
igantacciya wajan ma'abota ilmi shi ne karatun fatiha wajibine akan wanda zai
sallah shi kaɗai, da kuma liman da mamu asallar da ake
bayyana karatunta ko ake boye karatunta, saboda dalilai dasuka nuna hakan, da
kuma kebantuwar dalilan, Amma faɗin
Allah madaukakin sarki daya ce:
وَإِذَا قُرِئَ الْقُرْآنُ فَاسْتَمِعُوا لَهُ وَأَنْصِتُوا لَعَلَّكُمْ تُرْحَمُونَ ٢٠٤
Kuma idan an karanta Alƙur'ani
sai ku saurara gare shi, kuma ku yi shiru; Tsammaninku, ana yi
muku rahama. (Surah Al-A'raf - 204).
Da fadin Manzan Allah (ﻭﺇﺫﺍ ﻗﺮﺃ ﻓﺄﻧﺼﺘﻮﺍ )
ya haɗe
karatun fatiha da waninta, sai ake bance su da hadisin dayake cewa (Babu sallah
ga wanda bai karanta fatiha ba). Ma'ana waccan aya da waccan hadisi basu shafi
wajabcin karatun fatiha akowacce sallah ba, kuma basu shafi wajabcin karatun
fatiha akan kowaba asallah dan haɗa
dalilan gaba ɗaya kai aiki dasu.
Amma hadisin dake cewa (karatun
liman shi ne karatun mamu )wannan hadisine mai rauni, maganar da ake cewa, faɗin
mamu Ameen idan liman yagama karanta fatiha yana matsayin karatun fatihar su,
wannan maganace mai rauni bata ingantaba.
Muna rokon Allah shiriya
cikin abunda akai saɓani kansa nagaskiya domin
shi mai jine da amsa addu'ar bayinsa.
WALLAHU A'ALAM
Ku kasance damu cikin wannan
group domin ilimintarwa, Fadakarwa da Tunatarwa a Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.