𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum Malam. Mene ne hukuncin wanda ya bar sallar juma'a ba tare da wani kwakwkwaran dalili ba?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumusalam
warahmatallahi wabarakatuh.
Barin zuwa sallar juma'a ga
mutum baligi Mai lafiya wanda ta wajaba akansa ba tare da wani dalili na
shari'a ba Kaba'irace cikin Manyan Laifuka, duk wanda kuma ya bar sallar Juma'a
har Uku ajere bai jeba Allah zai toshe Zuciyarsa yakasance Cikin gafalallu,
kamar yanda Muslim Yaruwaito A cikin Sahihin Littafinsa Daka Abu Huraira Yardar
Allah takara tabbata a gareshi da Abdullahi Ɗan
Umar, Allah ya kara yarda dasu, Sun ji Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam akan
Munbari yana cewa (Kodai Mutane Sudena barin kinzuwa Sallar Juma'a kokuma Allah
yakulle zukatansu, Sannan Sukasance Cikin gafalallu). Awani hadisin Daban (Duk
wanda ya bar Sallar juma'a uku dagan-ganci Allah Zai toshe Zuciyarsa).
Waɗannan
Uƙubobine Nazuciya, Sunfi tsanani akan uƙuba tajiki tahanyar kulle mutum akurkuku
ko dukansa da bulala, Kuma wajibi ne ga shugaba Yahukunta waɗanda
ba sa Zuwa Sallar Juma'a ba tare da Wani Uzuri karɓabe
Ashari'aba, Abin da zai zamto Firgici Na laifinsu, Dukkan Musulmi ya ji tsoran
Allah karya tozarta wani wajibi ciki Abubuwanda Allah ya wajabta masa, Ya dunga
Tunawa Kansa Uƙubar Allah, Ya kiyaye
Abin da Allah ya wajabta masa danya Samu ladansa Awajan Allah, Allah yana bayar
da Falalar ga Wanda yaso.
Shaiek Abdurrahman Mubaraka.
Saboda Haka wanda ya bar sallar juma'a ba tare da wani Uzuriba ya aikata babban
laifi cikin Manyan Laifuka, Kuma Inbai tubaba Allah zai rufe zuciyarsa Babu
wani alkhairi da zai shiga cikinta sai sharri da bala'i Sannan yazamto cikin
gafalallu, Wadanda Zasuyi Nadama Ranar Alkiyama. Allah yakiyayemu.
WALLAHU A'ALAMU.
Ku kasance damu cikin wannan
group domin ilimintarwa, Fadakarwa da Tunatarwa a Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
Barin sallar Juma’a ga mutum baligi, lafiyayye, wanda ta wajaba a kansa, ba tare da wani uzuri na shari’a ba, yana daga cikin manyan laifuka (Kaba’ir) a Musulunci.
Manzon Allah ﷺ ya yi gargaɗi
mai tsanani game da hakan.
Hadisai kan barin Juma’a
1. Allah zai kulle zuciyar wanda ya bar Juma’a saboda raini
Muslim ya rawaito daga Abu Huraira da Abdullahi ɗan Umar – Allah ya ƙara
yarda da su – cewa
Annabi ﷺ
ya ce:
“Ko dai mutane su daina barin zuwa
Juma’a, ko kuwa Allah zai kulle zukatansu, sannan su kasance cikin gafalallu.”
A wani hadisin kuma:
“Duk wanda ya bar sallar Juma’a uku
saboda ganganci, Allah zai toshe zuciyarsa.”
Wannan hukuncin zuciya ya fi duk wata hukuncin jiki tsanani
— domin rufe zuciya na nufin:
Rashin natsuwa
Rashin jin daɗin
ibada
Rashin fahimtar Alkhairi
Zama cikin gafala
Hukuncin Shari’a
Malamai sun ce:
Wajibi ne ga shugabanni su hukunta wanda ya yawaita barin
sallar Juma’a ba tare da uzuri ba.
Domin hakan saba wa doka ce ta addini, kuma ya jawo
lalacewar al’umma.
Nasiha ga Musulmi
Ya kamata kowa ya tsoraci barin abin da Allah Ya wajabta.
Ya tuna da uƙubar da ke tare da watsi da farilla.
Ya kiyaye wajibai domin samun lada da falalar Allah.
Sakamakon barin Juma’a
Wanda ya bar ta ba tare da uzuri ba:
Ya aikata babban laifi.
Idan bai tuba ba, Allah zai rufe zuciyarsa.
Zuciyarsa ba za ta karɓi
alkhairi ba.
Zai shiga cikin gafalallu.
Zai yi nadama a ranar Kiyama.
Allah Ya kiyaye mu daga barin wajibai, Ya sa mu kasance
cikin masu tsoronSa.
WALLĀHU A‘ALAM.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.