𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam Khamis. Don Allah wanne abubuwa ke sa mutum ya yi tayin addu'a amma Allah ba zai amsa masaba.?
DALILAN DA KE SA ALLAH YA ƘI AMSA ADDU'AR BAWANSA:
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuh
Kaɗan
daga cikin abubuwan dayasa mutum zaitayin addu'a amma baza'a amsa masaba.
1. CIN HARAM: Allah baya
amsar addu'ar maciyin haram, ko mara kula da alƙawari
da ƙarya da cin amana da kuma yawan zantukan
batsa.
2. RASHIN GASGATA ADDU'A:
Idan mutum zai yi addu'a kuma bai yi ta da ikhlasi ba to kamar bai gasgakata ta
bane. Ko kuma rashin furta lafuzzan daidai.
3. RASHIN TSARKIN ZUCIYA:
Babu yadda za ai zuciyarka ta cika da Hassada da baƙin-ciki da jin haushin wani kuma Allah
ya Amsa maka addu'arka.
4. RASHIN KULA DA IBADA:
Babu yadda za ai bawa ya yi watsi da abin da Allah ya wajabta masa kuma ya roƙi Allah, Allah yamasa abin da yakeso.
5. RASHIN KYAUTATA IBADA:
Babu yadda za ai bawa yana sallah ko wata ibada batare da nutsuwa da kyautata
ibadar ba, kokuma kana sallah amma zuciyarka tana cike da tunnin wani abu daban
ba sallar ba.
6. GIRMAN KAI: Allah baya
Amsa addu'ar masu girmankai, domin girman kai sifface ta yahudawa maƙiya addinin Allah.
7. RASHIN HIKAYO ABIN DA AKE
FAƊA ACIKIN ADDU'A: Idan mutum yana addu'a
kuma baya hikayo (hango ma'anonin) ababan dayake faɗi na
girmama Allah da ayoyinsa ayayin addu'ar da kuma kiyaye girman wanda yake roƙon to shi ma bazai sami biyan buƙataba.
8. CIN MUTUNCIN MUTANE: Babu
wani wanda zai zama mai cin mutuncin mutane yana wulaƙantasu kuma ya yi tsammanin za a amsa
masa addu'arsa.
9. GAGGAWA. Ɗan Adam akwaishi da gaggawa sha yanzu
magani yanzu, Allah ba ya son gaggawa, shi yasan lokacin dayafi dacewa ya baka
duk abin da kakeso. Shi yasan lokacin dayafi dacewa yabaka arzikinka. Ko mutum
yarinƙa cewa ni inata addu'a amma haryanzu
ba'a amsamin ba. Haka haihuwa. Haka ilimi. Haka lafiya ga mara lafiya. Haka
aure. Da sauaransu. Duk Allah ke badasu a lokacin dayaso.
10. RASHIN NACI AKAN ADDU'A:
Idan mutum baya naci akan addu'a shi ma wanann baya samun biyan buƙatarsa. Domin Allah yanason bawa mai
yawan naci acikin roƙon
ubangijinsa.
11. Rashin ƙasƙantar
da kai agaban Allah, da nuna gazawa agaban Allah, da nutsuwa agaban Allah.
12. Rashin kyautata zato ga
Allah da kwaɗaituwa a gareshi akan samun biyan buƙatu, da cire kokwanto acikik zuciya.
Yazo A Hadisi Cewa:
Abdullahi ɗan Abas (RA) Ya ce: Na kasance a bayan
Manzon Allah {Sallallahu Alaihi Wasallam} wata rana, Sai ya ce dani, Yakai
yaro. Zan sanar da kai wasu kalmomi: Ka kiyaye Allah sai ya kiya ye ka, Ka
kiyaye Allah zaka same shi a gaba gare ka, idan zakai roƙo to ka roƙi
Allah, idan zaka nemi taimako ka nemi taimakon Allah. Ka sani da al’umma zasu taru don su amfane
ka da wani abu, bazasu iya amfanar da kai komai ba, sai dai abin da Allah ya
rubuta maka. Idan kuma da al’umma
zasu taru don su cuceka da wani abu, bazasu cuceka da komai ba, sai da abin da
Allah ya rubuta agareka. An ɗauke alƙaluma, takardun kuma sun bushe. [
Tirmiziy:2516 ]
A wata ruwayar kuma wacce ba
ta Imam tirmiziy ba, Ka kiyaye dokar Allah, zaka samu Ubangiji a gabanka, Ka
nemi sanin Allah a lokacin da kake cikin yalwa zai san da kai a lokacin da kake
cikin tsanani. Kasani duk abin da ya kuskure maka to bai kasance zai same ka
ba, Duk kuma abin da ya same ka bai kasance zai kuskure maka ba. Ka sani lallai
cin nasara yana tare da haƙuri,
Yayewar musiba kuma tana tare da baƙin
ciki, kuma lallai a tare da tsanani akwai sauki.
Ya tabbata a hadisi cewa; An
Karɓo
daga Abu Hurayrah (R.A) Ya ce; Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam) Ya ce:
(Allah) yana karɓawa ɗayanku
(addu'arsa) matuƙar
baiyi gaggawa ba, (shi ne) ya ce na yi addu'a (amma har yanzu) ba'a amsamin ba.
(Bukhari, 5865. Muslim, 2735).
Manzon Allah (Sallallahu
alaihi Wasallam) Ya ce: "hakika ubangijinku mai kunya ne, mai karamci ne.
yana jin kunyar bawansa yayin da ya cira hannayensa ya rokeshi, a ce ya mayar
dasu ba tare da komai ba".
An karbo hadisi daga
Buraidata (r.a) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam) ya ji wani
mutum yana cewa:👇
اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ بِأَنِّي أَشْهَدُ أَنَّكَ أَنْتَ اللَّهُ لاَ إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ الأَحَدُ الصَّمَدُ الَّذِي لَمْ يَلِدْ وَلَمْ يُولَدْ وَلَمْ يَكُنْ لَهُ كُفُوًا أَحَدٌ
FASSARA: "Ya Allah
hakika ina rokonka, na shaida kai ne Allah, babu abin bautawa da gaskiya sai
kai, makaɗaici, madawwami, wanda ba ya haifuwa
kuma ba a haife shi ba, kuma babu wanda ya kai shi. Sai manzon Allah (Sallallahu
alaihi Wasallam) ya ce: “Lallai ka yi roƙo da
sunan da Idan aka yi roƙo da
shi ana bayarwa, kuma idan aka yi addu'a da shi ana amsawa". mutane huɗu
suka ruwaito shi, Ibn Hibban ya inganta shi.
Wannan hadisin na nuna mana
kenan ana saurin Amsa addu'ar Wanda ya yi amfani da waɗannan
sunayen kenan. Saboda haka idan mutum zai yi addu'a, sai ya fara ambaton waɗancan
sunayen, sannan sai addu'ar ta biyo baya.
Akwai wasu lokuta idan bawa
ya yi addu'a Allah na karɓa masa kai tsaye kamar yadda
ya tabbata a hadisi. Misali kamar sulusin dare na ƙarshe, lokacin saukar ruwan sama,
tsakanin Kiran sallah da tada iƙama,
Ranar juma'a daga sallar la'asar zuwa faduwar Rana, in an yi sujjada ansa goshi
aƙasa.
Waɗannan
duka lokuta ne da Allah ke karban Addu'a, Lokacin da mutum yake kan hanyar
tafiya. Allah yana karban Addu'a, Addu'ar Wanda aka zalunta Allah (S. W. T)
yana karba, Addu'ar iyaye wa yayansu Allah (S. W. T) yana karba. Addu'ar me
azumi lokacin budabaki wannan Addu'a Allah na karba, Addu'a lokacin dakaji
zakara yai cara idan Kai Addu'a dai dai lokacin dayake cara wannan Addu'ar
Allah (S. W. T) yana karbanta.
Allaah Ta’aala Yana saukowa
zuwa saman duniya a ƙarshen
dare Yana cewa: Wa zai yi addu’a gare ni in amsa masa? Kuma wa zai roƙe ni in ba shi buƙatarsa? Kuma wa zai nemi gafarata in
gafarta masa? (Al-Bukhaariy: 7494; Muslim: 758)
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.