𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum warahmatullah, Sheikh barka da kokari Allah ya saka da alheri, tambayata shi ne, me yake sa yawan bacin rai ga mutum musamman ga mace, sannan meye mafita? malam a taimaka min da addu'ar da zan dinga yi inna cikin damuwa. Allah ba da ikon amsamin.
ADDU'AR YAYE BAƘIN-CIKI
DA DAMUWA
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikum assalam. Daga
cikin abubuwan da suke jawo ɓacin-rai akwai:
1. ZUNUBAI: Saboda duk mai
aikata su, zai samu kunci a rayuwar shi, kamar yadda Ibnulkayyim ya faɗa !
2. Tunawa da mummunan abin
da ya gabata ko kuma fargabar abin da zai faru Nan gaba.
3. Yawan burace-burace.
4. Rashin yafiya da niyyar ɗaukar
fansa.
5. Yawaita alaka da mutane,
saboda duk wanda alakokinsa suka Yi yawa, ko masu binsa bashin nauyi za su
yawaita.
Yawaita Istigfari, da
cikakken dogaro ga Allah, da kuma takaita Mu'amala da mutane yana karanta
damuwa.
Rokon Allah da dogaro ga
Allah da yarda da Ƙaddara
mai kyau ko marar kyau, yana daga cikin mafi girma hanyar samun waraka da
damuwa da bakin-ciki da yake damun bawa.
Manzon Allah Sallallahu
Alaihi Wasallam ya koyar da mu addu'oin da yakamata mu yawaita karantawa dan
samun waraka daga dukkan wani bakin-cikin da damuwa da kuncin rayuwa nan duniya
da lahira da yardar Allah.
Manzon Allah Sallallahu
Alaihi Wasallam yana cewa: Adduar zinnun lokacin da ya roki Allah yana cikin
kifi:👇
ﻻ ﺇﻟﻪَ ﺇﻟَّﺎ ﺃﻧﺖَ ﺳﺒﺤﺎﻧَﻚ ﺇﻧِّﻲ ﻛﻨﺖُ ﻣﻦ ﺍﻟﻈﺎﻟﻤﻴﻦَ
"LA ILAHA ILLA ANTA
SUBHANAKA INNI KUNTU MINAZ ZALIMIN"
babu wani mutum da zai shiga
cikin damuwa kuma ya roki Allah da wannan adduar, face sai Allah ya fitar da
shi daga wannan damuwar).
Haka kuma an ruwaito daga
Abu Bakrah cewa Manzon Allah (tsira da aminci Allah su tabbata a gare shi) ya
ce addu'ar wanda ya shiga mawuyacin hali ita ce:👇
ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺭَﺣْﻤَﺘَﻚَ ﺃَﺭْﺟُﻮ ، ﻓَﻠَﺎ ﺗَﻜِﻠْﻨِﻲ ﺇِﻟَﻰ ﻧَﻔْﺴِﻲ ﻃَﺮْﻓَﺔَ ﻋَﻴْﻦٍ ، ﻭَﺃَﺻْﻠِﺢْ ﻟِﻲﺷَﺄْﻧِﻲ ﻛُﻠَّﻪُ ، ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻟَّﺎ ﺃَﻧْﺖ
"ALLAHUMMA RAHMATAKA
ARJU,FALA TAKILNI ILA NAFSI DHARFATA AININ, WA ASLIH LI SHA'ANI KULLAHU, LA
ILAHA ILLA ANTA"
[Abu Dawood (5090), Ahmad (27898)]
Manzon Allah Sallallahu
Alaihi Wasallam ya cewa Asma'u bntu Umais R.A: Shin bazan koya maki ba wata
addu'a da zaki karantata alokacin damuwa da bakin-ciki, ko lokacin kuncin
rayuwa?? Kice:👇
ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺭﺑِّﻲ ﻻ ﺃﺷﺮِﻙُ ﺑِﻪِ ﺷﻴﺌًﺎ
"ALLAHU ALLAHU RABBI LA
USHRIKU BIHI SHAI'AN"
Sa'annan kuma an ruwaito
daga Ɗan Abbas cewa Manzon Allah (tsira da
amincin Alllah su tabbata a garshi) ya kasance yana yin wannan addu'ar
alokacinda ya ji kansa a yana yin damuwa:👇
ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻟَّﺎ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺍﻟْﻌَﻈِﻴﻢُ ﺍﻟْﺤَﻠِﻴﻢُ ، ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻟَّﺎ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺭَﺏُّ ﺍﻟْﻌَﺮْﺵِ ﺍﻟْﻌَﻈِﻴﻢِ ، ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻟَّﺎ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺭَﺏُّ ﺍﻟﺴَّﻤَﺎﻭَﺍﺕِ ﻭَﺭَﺏُّ ﺍﻟْﺄَﺭْﺽِ ﻭَﺭَﺏُّ ﺍﻟْﻌَﺮْﺵِ ﺍﻟْﻜَﺮِﻳﻢ
"LA ILAAHA ILL-ALLAAH
AL-‘AZEEM UL-HALEEM, LAA ILAAHA ILL-ALLAAH RABB IL-‘ARSHIL-‘AZEEM, LAA ILAAHA
ILL-ALLAAH RABBIS- SAMAWAATI WA RABB IL-ARD WA RABBIL-‘ARSH IL-KAREEM"
[ Muslim (2730) ]
Manzon Allah Sallallahu
Alaihi Wasallam yana cewa: Babu wani Mutum da zai sami kansa a cikin damuwa da
bakin ciki, sai ya ce:👇
ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺇِﻧِّﻲ ﻋَﺒْﺪُﻙَ، ﺍﺑْﻦُ ﻋَﺒْﺪِﻙَ، ﺍﺑْﻦُ ﺃَﻣَﺘِﻚَ، ﻧَﺎﺻِﻴَﺘِﻲ ﺑِﻴَﺪِﻙَ، ﻣَﺎﺽٍ ﻓِﻲَّ ﺣُﻜْﻤُﻚَ، ﻋَﺪْﻝٌ ﻓِﻲَّ ﻗَﻀَﺎﺅُﻙَ، ﺃَﺳْﺄَﻟُﻚَ ﺑِﻜُﻞِّ ﺍﺳْﻢٍ ﻫُﻮَ ﻟَﻚَ ﺳَﻤَّﻴْﺖَ ﺑِﻪِ ﻧَﻔْﺴَﻚَ، ﺃَﻭْ ﺃَﻧْﺰَﻟْﺘَﻪُ ﻓِﻲ ﻛِﺘَﺎﺑِﻚَ، ﺃَﻭْ ﻋَﻠَّﻤْﺘَﻪُ ﺃَﺣَﺪًﺍ ﻣِﻦْ ﺧَﻠْﻘِﻚَ، ﺃَﻭِ ﺍﺳْﺘَﺄْﺛَﺮْﺕَ ﺑِﻪِ ﻓِﻲ ﻋِﻠْﻢِ ﺍﻟْﻐَﻴْﺐِ ﻋِﻨْﺪَﻙَ، ﺃَﻥْ ﺗَﺠْﻌَﻞَ ﺍﻟْﻘُﺮْﺁﻥَ ﺭَﺑِﻴﻊَ ﻗَﻠْﺒِﻲ، ﻭَﻧُﻮﺭَ ﺻَﺪْﺭِﻱ، ﻭَﺟَﻠَﺎﺀَ ﺣُﺰْﻧِﻲ، ﻭَﺫَﻫَﺎﺏَ ﻫَﻤِّﻲ”
"ALLAHUMMA INNIY
‘ABDUKA IBN ABDIKA IBN AMATIKA, NAASIYATIY BIYADIKA, MAADIN FIYYA HUKMUKA,
‘ADLUN FIYYA ƘADAA’UKA, AS’ALUKA
BIKULLI ISMIN HUWA LAKA SAMMAITA BIHI NAFSAKA, AU ANZALTAHU FIY KITAABIKA, AU
‘ALLAMTAHU AHADAN MIN KHALƘIKA,
AU ISTA’SARTA BIHI FIY ILMIL GAIBI ‘INDAKA AN TAJ’ALAL ƘUR’ANA RABIY’A ƘALBIY, WA NUURA SADRIY WA JALA’A HUZNIY
WA ZIHAABA HAMMIY"
Face sai Allah Ta’ala Ya
tafiyar masa da damuwar shi da bakinhcikin shi, kuma Ya musanya masa da
farin-ciki a maimakon su. Sai Sahabbai R.A suka ce: "Ya Manzon Allah
Sallallahu Alaihi Wasallam shin bazamu koyawa yan'uwanmu ba saboda mahimmanci
wannan adduara ba??" Sai ya ce: (Eh dukkan wanda ya ji wannan addu'ar to
yana da kyau ya koyar da wanda bai sani ba).
Duba littafin al-Kalimu
al-Dayyib na Sheikhul Islam Ibn Taimiyya, Rahimahullah, tahkikin Sheikh
Muhammad Nasiruddeen al-Albani shafi ba 72.
To ire-iren waɗannan
addu'o'in waɗanda suka tabbata daga Annabi (sallalahu
alaihi wasallam) sune ake son Musulmi ya lazimci yinsu a duk lokacinda ya
tsinci kanshi a cikin wani mawuyacin hali, bakin ciki, masifa ko damuwa.
ALLAH KA YAYE MANA DUKKAN
KUNCI DA DAMUWA DA BAKIN-CIKI DA MATSALAR RAYUWAR DUNIYA DA LAHIRA.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.