Shaikh Abdurrahman al-Mu'allimiy yana bayani a kan wasu abubuwa da ya kamata mutum yana yawan tunani a kansu, ya sanya su a gaban idonsa, daga cikinsu sai ya ce:
((Mutum ya yi tunanin yadda yake da son rai.
1- Ka gaddara cewa; labari
ya same ka cewa: wani mutum ya zagi Annabi Muhammad (saw), wani kuma ya zagi
Annabi Dawud (as), wani mutum na uku kuma ya zagi Sayyidina Umar (ra) ko Aliyu
(ra). Mutum na hudu kuma ya zagi Malaminka (shugaban Mazhabarka ko jagoran
Akidarka ko shugaban Kungiyarka ko shehin Darikarka), Mutum na biyar kuma ya
zagi Malamin wani, to shin fushin da za ka yi a kan wadannan mutane, da kokarin
da za ka yi na ganin an yi musu ukuba an ladabtar da su ya dace da abin da
Shari'a ta hukunta, sai fushinka ga na farko da na biyu su zama kusa da juna,
kuma su fi tsanani sosai a kan sauran, haka fushinka a kan na uku ya zama kasa
da na daya da na biyu, kuma ya fi tsanani a kan sauran na bayansa, haka
fushinka a kan na hudu da na biyar ya yi kusa da juna, kuma ba su kai wadanda
suka gabace su ba, kuma a samu tazara tsakaninsu?
2- Ka kaddara cewa; ka
karanta wata Ayar Alkur'ani sai ka lura da cewa; Ayar ta dace da ra'ayin
Malamin Mazhabarka, da ka karanta wata Ayar kuma sai ka lura cewa; ta saba ma
wani ra'ayinsa daban, to shin kallonka ga wannar Ayar zai yi daidai da ta
farkon, ta yadda ba za ka damu ba idan ya tabbata ta dace da abin da ka gano,
ko kuma ba ta dace ba, bayan ka gama bincike da tadabburi?
3- Ka kaddara cewa; ka samu
Hadisai guda biyu, ba ka san inganci ko rauninsu ba, amma daya daga cikinsu ya
dace da ra'ayin Malaminka, daya kuma ya saba masa, shin kallonka ga wadannan
Hadisai biyu zai yi daidai, ta yadda ba damuwarka ba ce kowanne daya daga cikin
Hadisan ya zama ingantacce ko mai rauni?
4- Ka kaddara cewa; ka yi
nazari a wata mas'alar da Malaminka yana da ra'ayi a kanta, wani Malamin daban
kuma ya saba masa, shin ba ka kasance ka karkata zuwa ga rinjayar da daya
ra'ayin a kan daya ba, kawai kai so kake yi ka san wanda ya fi rinjaye a tsakaninsu
ka bayyana shi a matsayin mai rinjaye?
5- Ka kaddara cewa; ga nan
wani mutumin da kake sonsa, ga can kuma wani da kake kinsa, sai suka yi jayayya
a kan wata mas'ala, sai ka yi Fatawa a kanta, alhali ba ka san hukuncin
mas'alar ba, kuma kana so ka yi nazari a kanta, shin zuciyarka ba za ta so cewa;
wanda kake so a cikin mutanen biyu ya zama shi ne a kan dadai?
6- Ka kaddara cewa; kai da
wani Malami da kake sonsa, da kuma wani wanda kake kinsa duka kun ba da fatawa
a kan wata mas'ala, sai ka ga fatawowinsu su biyun sai ka ga sun dace da
daidai, sai labari ya same ka cewa; akwai wani Malami can daban ya soki daya
daga cikin fatawowin naku guda uku, ya kausasa harshe a kanta, shin a wajenka
duk daya ne idan ya zama fatawarka ya soka, ko ta masoyinka, ko ta makiyinka?
7- Ka kaddara cewa; ka san
wani mutum da yake aikata mummunan aiki, amma ka ji ba za ka iya yi masa inkari
ba, sai labari ya same ka cewa; wani Malami ya yi inkari ma wannan mutumi
inkari mai tsanani, shin yabawanka ga wannan inkari zai zama daidai idan wanda
ya yi inkarin masoyinka ne ko makiyinka, wanda ya aikata mummunan aikin kuma
masoyinka ne ko makiyinka?
8- Ka binciki zuciyarka, ka
samu cewa; Allah ya jarabe ka da wani aikin sabo ko tawaya a Addini, kuma ka
samu Allah ya jarabi wani makiyinka shi ma da wani aikin sabo ko tawaya a
Addini, a Shari'a duk dadai kuke, shin kyamatarka ga halin da yake ciki zai yi
dadai da kyamatarka ga halin da kai ma kake ciki, har ya zama fushinka ga kanka
dadai yake da fushinka gare shi?
A dunkule, hanyoyin son
zuciya suna da yawa, ba za a iya iyakance su ba. Hakika na jaraba kaina, ta
yiwu na yi nazari a wata mas'ala ina jin cewa; ban yi son zuciya a cikinta ba,
har na fahimci wata ma'ana a cikinta na tabbatar da ita tabbatarwan da zai kayatar
da ni, sai kuma daga baya na lura da wata matsala mai suka ga wannar ma'ana,
sai na ji zan shirya ma wannar matsalar, sai na ji zuciyata tana ingiza ni ga
kwakwule-kwakwulen martani a kanta, tare da rufe ido a kan tattauna martanin.
Wannan ya faru ne saboda a lokacin da na tabbatar da waccar ma'ana da farko,
tabbatarwan ya burge ni, na kasance zuciyata ta karkata ga tabbatar da
ingancinta, duk da cewa; babu wanda ya san haka a tare da ni, to yaya kuma idan
sai da na watsa ta ne a cikin mutane tukun sai na lura da waccar matsalar?
To yaya kuma lamarin yake
idan ba ni na lura da waccar masalar ba, wani mutum ne daban ya ci gyarana?
Yaya kuma idan makiyina ne
ya ci gyaran nawa?
Wannan fa ba a tilasta wa
Malami cewa; kar a samu nau'i na son rai a zuciyarsa ba, saboda wannan abu ne
wanda ya fita daga ikonsa. Kawai abin da yake wajibi a kansa shi ne ya rinka
bincikar zuciyar tasa game da son ran da ke cikinta don ya san da shi, sai kuma
ya yi kokarin kiyayewa, ya rinka lura da gaskiya matuka, a matsayinta na
gaskiya. Idan ya bayyana masa cewa; ya saba ma son ransa to sai ya fifita
gaskiya a kan son ran nasa. Wannan shi ne ma'anar Hadisin nan - Allah shi ne
mafi sani - wanda al-Nawawiy ya ambace shi a cikin "al-Arba'un", kuma
ya ce; Isnadinsa ingantacce ne, Hadisin shi ne: ((Dayanku ba zai yi cikakken
imani ba har sai son ransa ya zama mai bin da abin da na zo da shi)).
Malami zai iya gazawa wajen
kiyayewa ga son ransa, ya bar ran nasa ta karkata ga barna har ya taimaki
barnar, yana zaton bai fita daga gaskiya ba, kuma bai yi gaba da ita ba, wannan
kam babu mai tsira daga gare shi sai Ma'asumi. Malamai sun banbanta a cikin
haka, a cikinsu akwai wanda yake yawaita sake zuciyarsa ta bi son ransa, ya yi
barna har wanda bai san dabi'un mutane ba, bai san girman tasirin son rai a kan
zuciya ba ya dauka cewa; mai ganganci ne. A cikinsu akwai wanda yake k'aranta
sake zuciyar tasa ga son rai sai ya yi sauki. Duk wanda ya bibiyi littatafan
Marubuta wadanda ba su dogaro a Ijtihadinsu a kan Alkur'ani da Sunna zai ga
abin mamaki kwarai da gaske, sai dai hakan ba zai bayyana masa ba sai a wuraren
da ba shi da son rai a cikinsu, ko ya kasance son ran nasa ya saba ma abin da
ke cikin littatafan, saboda ya sake ma son ransa sai ya ga cewa; wadanda suka
dace da ra'ayinsa ba su da son rai, wadanda suka saba masa kuma gaba dayansu
masu bin son ransu ne.
Hakika a cikin Salaf akwai
wanda ya kasance yana kaiwa matuka wajen kiyaye zuciyarsa daga son rai har ya
kai ga zaluntar dan'uwansa, misalinsa kamar wanda yake tafiya ne a kan hanya,
ya kasance a damansa akwai wajen tuntube, sai ya guje masa, ya nisance shi, sai
kuma ya fada wani wajen tuntuben a hanun hagunsa bai sani ba)).
القائد
إلى تصحيح العقائد (ص: 30 - 33)
Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.