A yau babu abin da al'ummar Musulmi take bukata face hadin kai. Sai dai kash! kan ba zai hadu ba, dole sai kowa ya jefar da Akidarsa, ya zo an hadu a kan Akidar Sunna. Don babu abin da zai hada kan Musulmi sai ingantacciyar Akida ta gaskiya, wacce ta zo cikin Alkur'ani da Hadisi, Akidar da Sahabbai da Tabi'ai da A'imma suka rayu a kanta.
In dai da gaske hadin kan ake so,
to sai Sufaye sun bar Akidunsu, sun yi watsi da Shehunai da Waliyyansu.
Haka 'Yan Shi'a sai sun bar
Akidarsu, sun jefar da Marji'o'i da Mahdinsu.
Su ma Khawarijawa dole sai sun
bar Akidarsu, sun ajiye bindigogi da bama-bamansu.
Asha'ira da Aqlaniyyun, su ma
wajibi ne su ajiye akidunsu, su yi watsi da dagutun "Majaz" da
gurbatattun hankulansu.
Kowa sai ya watsar da tarkacensa,
ya zo ya bi Alkur'ani da Hadisi kamar yadda Sahabbai da Tabi'ai suka fahimta.
Duk wanda yake zaton zai hada kan
mabanbanta Akida, ya yi siyasa, ya kafa Gomnati ta Muslunci to mafarki yake yi.
Wannan fa ba ina magana ne da
Zindikai cikin 'Yan Shi'a da Sufaye ba, a'a, ina magana ne da wadanda da gaske
suna son Addinin.
Wajibi ne mu hada kai a kan
Akidar Alkur'ani da Sunna, mu tinkari Zindikai da 'Yan Boko Akida, wadanda suka
yi damarar rushe Addini, da sauran abokan gaba.
Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.