Ticker

6/recent/ticker-posts

Takaitaccen Tarihin Annabi Idris (AS)

TAƘAITACCEN TARIHIN ANNABI IDRIS (AS)

Sunansa na ainihi shi ne: Ukhnuukhu ɗan Shithu ɗan Adamu (AS).

An fara ambatonsa a cikin Alƙur’ani Maigirma a Sura ta 19, aya ta 56-8:

“Ka tuna a cikin littafi labarin Idris (AS). Shi ya kasance mai gaskatawa ne kuma Annabin Allah (SWT). Mun ɗaukaka shi (zuwa gare mu kuma yana) a kan wani matsayi maɗaukaki.”

Daga nan sai a Sura ta  21, aya ta 85:

“Da Isma’ila da Idrisa da Zal Kifl, kowane yana daga cikin managartan bayinmu.”

Sai kuma a Sura ta 96, a aya ta 4:

“(Allah shi ne) wanda ya sanar (da mutum) da alƙalami (wato, wanda ya ba mutum ilimi da rubutu da karatu). (Mamman, 2014:241).

Ya kasance mai gaskatawa ne kuma annabin Allah (SWT).

Shi kakan Nuhu (AS) ne. An haife shi a zamanin da Annabi Adamu (AS) yake raye, kafin ya mutu da shekara ɗari (100).

An ba shi annabta da misalin shekaru ɗari biyu (200) bayan wafatin (mutuwar) Annabi Adamu (AS). Annabi Idris ya rayu bayan an ba shi annabta har tsawon shekaru ɗari da hamsin (150).

Ibn Ishaƙ ya ce, Annabi Idris ya tarar da wani ɓangare na rayuwar Annabi Adamu da shekaru ɗari uku da tamanin (380).

A wani bayanin, ɗaukacin shekarunsa a duniya su ne ɗari huɗu da hamsin (450).

Ya kasance tsakaninsa da rayuwar Annabi Nuhu kimanin shekaru dubu ɗaya (1000).

An yi masa laƙabi da Idris domin shi ne wanda ya fara karanta littafi, domin Allah (SWT) ya saukar masa da littattafai guda talatin (30).

An ce farkon wanda ya fara rubutu da alƙalami da kuma na ram(a)li shi ne Annabi Idris (AS). Shi ne kuma wanda ya  fara ɗaukar makami ya yaƙi kafirai da shi. Shi ya fara yin nazarin ilimin taurari da na lissafi (hisabi).

Masana sun ce wannan ya samar da abin faɗakarwa kan falalar rubutu don amfaninsa mai yawa ga ɗan Adam, kamar wajen:

- Gane wasu lamurran suka ɓoye.

- Aje ilimi (sannai) daban-dabam.

- Taskace hikimomin ɗan Adam.

- Gane labarun mutanen farko da halayensu da tarihinsu da zantukansu.

Masana sun nuna ba don rubutu ba, da lamarin addini (ko wani na duniya) bai tsaya daidai ba.

Allah (SWT) ya aike shi zuwa ga ɗiyan  ƙabila, wanda shi ne ɗaya daga cikin ‘ya’yan Annabi Adamu (AS).

Mai yawan ibada ne, musamman ta yin azumi. An ce yawan ladar aikinsa a kullum ta kai ta talikan zamaninsa kuma sai Allah ya yabe shi don ya ƙara duƙufa ga bautarsa.

Allah ya ɗauke shi zuwa wani matsayi a sama ta huɗu ko a gidan aljanna, kuma a raye yake ko a halin yanzu yana ta bautar Allah (SWT) tare da mala’iku a can sama.

An ce ya shiga aljanna bayan an ɗanɗana masa mutuwa a wani ɗan lokaci sannan aka tashe shi kuma da ya shiga bai fito ba. Mala’ikan mutuwa ne ya kai shi a bakin ƙofar wuta ya gan ta sannan sai kuma ya kai shi aljanna. Da aka kai shi ya samu ya shiga sai ya ƙi fitowa, da izinin Allah (SWT).

Bayanin Manzon Allah (SAW) a cikin wata doguwar ruwaya ta hadisinsa, game da tafiyar dare (isra’i) da aka yi da shi, daga masallaci mai alfarma da ke Makkah zuwa masallaci mai nisa da ke birnin Ƙudus, da kuma hawa sama (mi’iraji) da aka yi da shi don ganawa da Allah (SWT), ya tabbatar da cewa Annabi Idris (AS) yana a sama ta huɗu ne, kamar haka:

“...sai aka hau da mu (shi da mala’ika Jibrilu) zuwa sama ta huɗu. Da Jibrilu ya  nemi a buɗe ƙofar sai aka ce da shi, “Wane ne kai?” Sai ya ce, Jibrilu ne.” Sai aka ce, “Wa ke tare da kai?” Sai ya ce, “Muhammad ne.” Sai kuma aka ce, “An yi aike zuwa gare shi?” Sai Jibrilu ya ce, “I, an yi aike zuwa gare shi.” Daga nan sai aka buɗe mana, sai ga ni ga Idris. Ya yi mani maraba ya kuma yi mani addu’a ta alheri...” (Hashiyyatus Saawiy..., Juzu’i na II, shafi na 418).

An ce Annabi Idris shi ne ya fara ɗunka tufafi. Kafin nan, mutanensa sun kasance fatu suke yafawa a jikinsu. Allah ya yabe shi kuma ya ba shi siffa ta siddiƙantaka (ban gaskiya ga lamarin Allah a kodayaushe).

Don ƙarn bayani, duba littafin:

1. Suyuti, J. da Muhalli, J. (2017). Hashiyyatus Saawiy ala Tafsiril Jalalaini. Juzu’i na II, shafi na 418; Juzu’i na III, shafi na 49 da na 105; Juzu’i na IƁ, Shafi na 447. Madaba’atu Darul Fikr, Beirut, Lebanon.

2. An Nisaburiy, A.I. (1954). Ƙisasul Anbiya’i: Ara’isul Majalis. Maktabatu Mustapha Alhalbiy, Misra, Egypt. Pp. 49-50.

3. Ibn Katheer, I. (2002). Ƙisasul Ambiya’i. DarulGadeed al Jadid, Al ƙahira, Egypt. Pp. 59-61.

4. Mamman, M. (2014). Fassarar Alƙur’ani Mai Girma Cikin Harshen Hausa.  Ahmadu Bello University Press Ltd, Zaria.

Tushe: Zauren WhatsApp na www.amsoshi.com

Tarihin Annabi Sulaiman

Post a Comment

0 Comments