HUKUNCIN MATAR DA KE SATAR KUƊAƊEN MIJINTA
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Dan Allah malam inada tambaya ne shin ya halatta macce ta ɗauki kuɗin mijinta batare da saninsa ba? domin biyan wasu 'yan bukatu nata kanana da be biya mata su na cikin gida haka da nata dana yaranta kuma malam yanada kuɗi amma inka tambaya sai yace bedashi, kuma malam bayarwa ne beyi sannan ko kyautar kuɗi aka bata ko yaranta sai ya karɓe kuma malan ko kitso zasu inta tambaya sai yace beda.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Haramun ne mace ta ɗauki wani abu daga dukiyar mijinta ba tare da izininsa
ba. Sai dai idan abinci ne ba ya ciyar da ita yadda zata Qoshi da ita da
'diyanta. Ko sutura idan ba ya basu, ma'ana ya barsu cikin tsiraici.
Akwai hadisin da Imamul Bukhariy ya ruwaito ta
hanyar Hindu bintu Utbah, matar Abu Sufyan tazo ta tambayi Manzon Allah
Sallallahu Alaihi Wasallam cewa mijinta yana da dukiya amma ba ya bata abinda
zata ci.. Shin ya halatta ta ɗauki wani abu ba
tare da saninsa ba, domin ta ciyar da kanta da 'ya'yanta??.
Sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yace
mata "KI ƊAUKI GWARGWADON
ABINDA ZAI ISHEKI DAKE DA 'YA'YANKI (BA TARE DA ƁARNA KO TA'ADI BA).
Amma Kamar kuɗin kitso, Kuɗin kayan
kwalliya, kuɗin biki, wannan ba
wajibi bane, sai dai yana cikin kyautatawar da Allah yayi umurni a yiwa mata.
Yace :"KU ZAUNA DASU TARE DA KYAUTATAWA".
Ibnu Jareer da Ibnu Abi Hatam da Abu Dawud sun
ruwaito hadisi daga Sayyiduna Abu Hurairah (ra) yace Manzon Allah Sallallahu
Alaihi Wasallam Yace: "MAFIFICIYAR MACE ITA CE WACCE IDAN KA KALLETA ZATA
SANYAKA FARIN-CIKI, IDAN KA UMURCETA ZATAYI MAKA BIYAYYA, IDAN KUMA BAKA NAN
ZATA KIYAYE MAKA AMANAR KANTA DA DUKIYARKA".
To kinga anan idan kika zamto kina yi masa satar
kuɗaɗensa, ba kya
cikin matayen kirki awajen Allah, sai dai kina cikin sahun maciya amana da kuma
masu yin zamba cikin aminci. Kuma idan baki nemi yafewarsa ba, lallai sai Allah
ya karɓa masa hakkinsa aranar Alqiyamah aranar hisabi.
Kiji tsoron Allah ki tuba ki dena sata, domin
hakika Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya tsine wa ɓarayi (kuma kina cikinsu har sai kin tuba tukunna). Kuma
yace ɓarawo ba mumini bane har sai ya tuba".
Allah ya shiryeki tare damu, ya shiryi dukkan
mataye masu irin wannan halin. Ameen.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.