Citation: Maikwari, H.U. & Dalhal, I. (2024). Zumunta a Waƙoƙin Baka Na Hausa: Nazari Daga Waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru. Four Decades of Hausa Royal Songs: Proceedings from the International Conference on the Life and Songs of Makaɗa Sa'idu Faru, 3(3), 117-126. www.doi.org/10.36349/tjllc.2024.v03i03.016.
ZUMUNTA A WAƘOƘIN BAKA NA HAUSA: NAZARI DAGA WAƘOƘIN MAKAƊA SA’IDU FARU
Daga
Haruna Umar Maikwari
Department of Hausa Language,
Federal College of Education (Technical), Gusau
Ƙibɗau: maikwariharuna@gmail.com
Lambar Waya:07031280554
Da
Ibrahim Dalha
Government Day Secondary School Birnin
Kudu,
Ministry of Education Science &
Technology, Dutse,
Jigawa State
Ƙibɗau: Ibrahimdalha1@gmail.com
Lambar Waya: 08060574254
Tsakure
Ga ɗabi’ar ɗan’adam, tunaninsa da hikimarsa sukan saje da juna da na
wani mutum da yake kusa ko kuma nesa da shi. Don haka al’adar ɗan’adam ta tabbatar da haɗuwar ra’ayi ta fuskokin addini ko sana’a ko kuma wani
lamari na rayuwa kan haifar da ɗorewar dangantaka ta musamman a tsakanin al’umma. Wannan bincike yana da
manufar gudanar da nazari domin ƙyallaro wani abu dangane da samuwar zumunta a wasu daga
cikin ɗiyan waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru da kuma na wasu Mawaƙan ƙasar Hausa na
fada. Binciken ya yi amfani da hanyoyin da suka haɗa da: Sauraren waƙoƙin baka daga
bakin maƙagansu ta hanyar amfani da memori da tuntuɓar wasu masana da suke da masaniya game da waƙoƙin nasu. Haka
kuma, nazarin bai kawar da kai ga leƙa wasu wallaffun ayyuka
da aka gudanar ba. Ayyukan da aka mayar da hankali a kansu sun haɗa da, wallafaffun matanonin waƙoƙin baka da kuma
nazarce-nazarcen da wasu manazarta da ɗalibai suka gudanar. An yi amfani da Bahaushen tunanin da
ke cewa: “Da abokin daka akan sha gari” a matsayin hanyar da aka ɗora binciken a kanta. Binciken ya fito da sakamako tare
da bayar da wasu shawarwari da za su ƙara wa Borno dawaki.
Wasu daga cikin sakamakon da nazarin ya gano su ne: Mawaƙan baka na fada suna amfana da fasahohin junansu inda
sukan yi amfani da kalmomi masu alaƙa wajen waƙe iyayen gidansu.
Har wa yau, nazarin ya gano cewa, akwai bambanci a tsakanin satar fasaha da waƙeƙeniya da kuma
zumuntar fasaha. Binciken ya bayar da shawarar cewa, waɗanda suke da
ilimin kwamfuta a cikinmu da su ɓullo da wasu manhajoji da za a riƙa jin muryoyin mawaƙanmu na baka irin su Sa’idu Faru, Salihu Jankiɗi, Ibrahim Narambaɗa da kuma Musa Danƙwairo da Aliyu Ɗandawo Shuni da sauransu da dama.
1.0 Shimfiɗa
Haɗuwar tunanin wani
rukuni na al’umma yakan yi amo a fasahohinsu na baka da kuma na sarrafa
albarkatunsu na yau da kullum. Irin wannan haɗuwar tunani takan
samu a dalilan zama wuri guda da tarayya da juna wajen gudanar da wasu sana’o’i
da kuma gamuwar ra’ayi. Idan aka yi duba da kyau, akwai hasashen cewa, samun
yawaitar ƙungiyoyi da jam’iyyun siyasa a wannan ƙarni na 21 yana da alaƙa da dalilin zumuntar tunanin wasu al’ummu da suke da manufa iri guda. Ga
al’adar ɗan’adam, tunaninsa yakan saje da na abokin zamansa ko kuma wanda suke hulɗar sana’a iri ɗaya. Idan aka samu
irin wannan sajewar tunani, ƙauna da zumunci
sukan ƙullu ta yadda akan zama tamkar abu ɗaya har abin ya
zama zumunta. Hakan kuma shi ne yakan sanya a riƙa amfani da kalmomi iri guda na sadarwa. Wani lokaci ma wani yakan yi
amfani da kalmomin da wani ya saba magana da su domin ya bayyana wani abu na
tunaninsa. Idan kuma aka samu akasi tunaninsu da ra’ayoyinsu suka saɓa, shi ne hakan yakan
haifar da wasu bambance-bambance ta fuskar ra’ayoyi inda har ake samun waƙeƙeniya a tsakanin mawaƙa. Kamar yadda masu sana’o’i na ƙira da noma da wanzanci da dangoginsu suke da zumunta a tsakaninsu[1],
haka su ma mawaƙan ƙasar Hausa sukan yi ƙoƙarin ganin zumuncinsu ya ƙullu da abokan sana’arsu ta fuskokin
fasahohinsu na waƙa da dangoginsu. Wannan yanayi na
sajewar tunani a tsakanin al’umma shi ne wannan bincike yake kallonsa a
matsayin zumuunci a waƙoƙin baka. Wannan
bincike yana da manufar nazarin zumuntar da ake samu a tsakanin waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru da
sauran takwarorinsa mawaƙan baka na fada[2].
An yi wannan tunani ne domin a nuna irin yadda yanayin zamantakewar Hausawa
yake ɗamfare da juna ta fuskokin al’adunsu na mu’amalarsu da kuma abubuwan da
suka shafi waƙoƙinsu.
1.1 Fashin Baƙin Ƙusoshin Taken Bincike
A wannan muhalli, an mayar da hankali wajen
fayyace ma’anonin muhimman kalmomin da aka gina taken wannan bincike da su.
Wato fitillun kalmomin da suka haska wannan take, waɗanda suka haɗa da: su ne:
Zumunci da kuma waƙar baka.
1.1.1 Zumuci
CHNN, (2006:136) ya bayyana ma’anar
zumunci da cewa: “Kyakkyawar dangantaka ta jini ko ta aure ko kuma ta abota
tsakanin mutum da mutum, d-d da zumunta.” Wannan ma’ana ta haska wa wannan
bincike cewa, zumunci kalma ce da take da ma’anar zaman tare wanda yake haifar
da kwaikwayar juna wajen gudanar da wata magana ko aiki ko kuma duk wata
fasaha.
1.1.2 Waƙar Baka
Wani zance ne shiryayye cikin hikima da
azanci da yake zuwa gaɓa-gaɓa bisa ƙa’idojin tsari da daidaitawa a rere cikin sautin murya da
amsa-amon kari da kiɗa da amshi, (Gusau, 2003:xiii). Bisa
wannan ma’ana da aka bayar, wannan takarda tana da ra’ayin cewa, waƙar baka ita ce, shiryayyen zance ne da ake ƙulla shi cikin hikima wanda kuma ake rerawa ta hanyar bin
raujin wani kiɗa.
1.2 Farfajiyar
Bincike
Kaucewa abin da Hausawa suke cewa:
“Wuce makaɗi da rawa.” Shi ne ya sanya aka ga dacewar yi wa wannan maƙala kadada. Sakamakon haka, takardar ta taƙaita ga laluben wuraren da aka samu zumuntar fasaha a waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru da
na sauran takwarorinsa mawaƙan fada. Mawaƙan da takardar ta mayar da hankali a kan fito da
zumuntarsu ta fuskar waƙa a tsakanisu da Sa’idu Faru sun haɗa da: Makaɗa Salihu Jankiɗi da Ibrahin
Narambaɗa da Musa Ɗanƙwairo Maradun da kuma Ahmadu Mailauni Bakura. Bugu da ƙari, kasancewar masana suna ganin mafiya yawancin waƙoƙin fada ana gina su ne a kan wasu
tubalai guda goma (10) [3].
Takardar ta mayar da hankali a kan uku daga cikin tubalan da ake gina waƙoƙin fada da su inda aka bayyana wuraren
da aka samu zumuntar a tsakanin Makaɗa Sa’idu Faru da ta sauran mawaƙan da aka lissafo a baya. Ke nan, maƙalar ta taƙaita ga laluben zumuntar da ake samu a
waƙoƙin baka a tsakanin
Sa’idu Faru da takwarorinsa mawaƙan fada a tubalan
waƙoƙin fada da suka haɗa da: Yabo da zuga
da kuma roƙo. Domin haka ba a tsammanin a ga kutsen
waƙar wani mawaƙi da ba na fada ba.
1.3 Hanyoyin Bincike
Kamar yadda Hausawa suka haƙiƙance da cewa: “Sanin wurin bugu shi ne ƙira.” Haka masana suka tabbatar da cewa, nagartaccen
bincike yana ƙunshe da ingantattun hanyoyin tattara
bayanai. Sakamakon haka, wannan maƙala ta yi amfani
da waɗannan hanyoyi a matsayin dabarun da suka samar da bayanan da ake nema.
Hanyoyin da aka yi amfani da su kuwa su ne:
i.
Da farko, an fara da samun waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru tare
da sauraren su ta wayar hannu saboda neman bayanan da ake lalube. Hakan ya sa
aka fara nazartar wasu ɗiyan waƙoƙinsa da suke a rubuce, musamman na
cikin Diwanin Waƙoƙin Baka wanda Gusau (2009) ya wallafa.
ii.
Sauraren wasu hirarraki da aka gudanar
da Maigirma Alhaji Ibrahim Muhammad (Ɗanmadamin Birnin
Magaji) a gidan Rediyon Tarayya na Kaduna (FRCN Kaduna) a kan rayuwa da tarihin
Makaɗa Sa’idu Faru a shekarar 2018-2019.
iii.
Leƙa ɗakunan karatu, musamman na Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato da na Jami’ar
Bayero, Kano inda aka yi katarin samun wasu ayyuka masu alaƙa da binciken da aka gudanar.
iv.
Shiga cikin rukunin shafin sada zumunta
na whatsApp (WhatsApp group) wanda a
ka ƙirƙire shi musamman domin yayata shirye-shiryen wannan taro. Wannan shafi ya ƙara wa wannan takarda ƙwarin gwiwa saboda muhimman bayanan da aka amfana da su daga wurin
ma’ilmanta na kusa da na nesa.
v.
Baya ga haka, maƙalar ba ta kawar da kai da tuntuɓar masana al’adun Hausawa ba. Wannan
dalili ya sa aka tuntuɓi Farfesa Ibrahim Abdullahi Sarkin
Sudan da Farfesa Yakubu Aliyu Gobir da kuma Dr. Nazir Ibrahim Abbas duka a
Jami’ar Usmanu Danfodiyo. Haƙiƙa tuntuɓar waɗannan masana ya ƙara wa wannan takarda armashi tare da yi mata jagora a
kan inda ta dosa.
1.4 Hanyar Ɗora Aiki
Masana da manazarta sun tabbatar da ɗora ayyukan
bincike a kan tunanin magabata yakan taimaka wajen yin jagora ta yadda ba za su
kauce daga kan turba ta ilimi ba. Sakamakon haka, wannan maƙala an ɗora ta a kan tunanin Hausawa da yake
cewa: “Da abokin daka akan sha gari.” An yi wannan tunani ne saboda ganin yadda
mawaƙan baka suke amfani da fasahohin
junansu wajen ƙulla ɗiyan waƙoƙinsu. Ke nan, a wannan takarda, abokin
daka shi ne, mawaƙi. Gari kuma shi ne, waƙoƙin da ake samu a bakunan mawaƙan baka waɗanda sukan haska wa junansu hanyoyin ƙirƙirar wasu sababbin
ɗiyan waƙoƙin da za su rera
wa masu gidansu da kuma masu ƙaunar sana'arsu ta
kiɗa da waƙa. Wannan ya nuna amfanuwar da mawaƙa suke yi da junansu ya yi daidai da abin da Hausawa suke
cewa: “Yaro da gari abokin tafiyar manya ne.”
2.0 Waiwayen Tarihin Sa’idu Faru a Taƙaitace
Babu shakka, akwai ayyukan magabata da
suka fayyace tarihin rayuwar Makaɗa Sa’idu Faru kafin wannan bincike. Kaɗan daga cikinsu sun
haɗa da: Gusau (1996:117) da Furniss (1996:176) da kuma Ɗanmadamin Birnin Magaji (2019). Don haka, ambaton wani abu daga cikin
tarihin Makaɗa Sa’idu Faru a wannan takarda tamkar cikon
sunna ne makaho da waiwaye. Duk da haka, Sa’idu Faru dai an haife shi a garin Faru da ke yankin ƙasar Maradun ta Ƙaramar Hukumar
Mulki ta Talatar Mafara da ke tsohuwar Jihar Sakkwato a shekarar 1932 kamar
yadda Gusau (1996:117) ya tabbatar[4].
Sunan mahaifinsa Makaɗa Abubakar ɗan Abdu. Kakansa
wanda ya haifi babansa sunansa Alu Maikurya. Ke nan, makaɗa Sa’idu Faru ɗan gado ne a fagen
kiɗa da waƙa. Makaɗa Sa’idu ya
gudanar da yawancin ƙuruciyarsa a garin mahaifiyarsa da ke
garin Banga ta Ƙauran Namoda. Kodayake bayan da ya tasa
ya baro gaban kakannin nasa inda ya koma gaban mahaifinsa. Sa’idu Faru ya yi karatun allo a ƙuruciyarsa, amma bai yi karatun boko da na littattafai ba. Bayan ya dawo
gaban mahaifansa ne sai sabgar kiɗa da waƙa suka shige masa gaba. Makaɗa Sa’idu ya koyi waƙa a wurin mahaifinsa Makaɗa Abubakar. Ya
fara bin sa waƙa tun bai fi shekara goma ba. Sa’idu ya
zama mawaƙi mai cin gashin kansa bayan rasuwar
mahaifinsa. Ga al’adar Sa’idu Faru ba ya yi wa kowa waƙa sai wanda ya jiɓinci sarauta. Haka kuma, yana amfani da
kotso a matsayin kayan kiɗansa. Yakan shirya waƙarsa a gida kafin ya bayyana ta a gaban wanda zai rere
wa. Sa’idu Faru ya rera waƙoƙi da dama, amma waɗanda ya yi wa mai
gidansa Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo su ne suka fi yawa da shahara, saboda
biyayyarsa da ƙaunar da yake yi masa. Kodayake Allah
bai nufe shi da riskar lokacin da Mai’alfarma Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo ya zama Sarkin
Musulmi ba. Makaɗa Sa’idu Faru ya rasu a shekarar 1987 ya bar mata da ‘ya’ya da jikoki da
dama, (Danmadamin Birnin Magaji, 2019). Yanzu haka (2024) ɗansa Ibrahim
Sa’idu Faru ne ya gaje shi wajen gudanar da sabgoginsa na kiɗa da waƙa.
3.0 Dalilan Samuwar Zumuntar Waƙoƙin Baka na Hausa
Al’adar mawaƙan baka ta ƙulla zumuntar waƙa a tsakaninsu ba za ta rasa alaƙa da wasu dalilai
ba. Wannan ne ya sa wannan maƙala take da
ra’ayin cewa, waɗannan su ne dalilan da suka sanya ake samun zumunta a waƙoƙin baka na fada:
i.
Mafiya yawancin mawaƙan baka na fada sun fito ne daga yanki guda, wato ƙasar Zamfara. Don haka karin harshensu da al’adunsu da
fasahohinsu suna da alaƙa da juna.
ii.
Salon waƙoƙinsu da kayan kiɗansu duka suna da
alaƙa da juna. Misali, makaɗan fada ga al’ada
sun fi amfani da kotso da taushi a matsayin kayan kiɗansu.
iii.
Tsarin mulkin sarakunan da suke wa waƙa kusan abu ɗaya ne, saboda dukkaninsu zuriyar gidan
Shehu Usmanu Danfodiyo ne da ta almajiransa. Don haka akan ji nason addini da
na jarumtar yaƙi da na nasaba da kuma na tarihi a
cikin ɗiyan waƙoƙinsu.
iv.
Kalmomin da ake yabon sarakuna ko ake
amfani da su a fada keɓantattu ne na musamman. Kafin-Hausa,
(2002:249) ya rawaito Sa’idu Faru da kansa ya bayyana musu cewa, dalilin da ya
sa ba ya yi wa wanda ba shi da muƙamin sarauta waƙa, saboda ba shi da kalmomin da zai tsara musu waƙa. Wannan dalili ya sa duk wani mawaƙi da yake kiɗan fada da kalmominsu na mulki yakan yi amfani. Don haka ba kowane mawaƙi ne yake iya waƙoƙin fada ba, saboda tanadin kalmominsu da tattalin yadda
ake amfani da su sai wanda ya san yadda suke da kuma yadda ake amfani da su.
v.
Zumuntar da ke tsakanin gidajen
sarakunan ta auratayya da ta addinin da kuma ta jini ta yi amo sosai wurin mawaƙan kowane sarki. Wannan ya ba da hasken samun zumuntar waƙa a wurin mawaƙansu.
4.0 Zumuntar Waƙoƙin Sa’idu Faru da Wasu Takwarorinsa
Mawaƙan Fada
Wannan takarda tana da ra’ayin cewa, zumuntar mawaƙan baka tana da bambanci da satar waƙa. Dalili kuwa, a zumuntar waƙoƙi an fi mayar da hankali a kan ƙulla alaƙa da manufar mawaƙa ta fuskokin kalmomin ɗiyan waƙa. Saɓanin satar fasaha da akan saci raujin murya da na kiɗa da kuma kayan
cikin waƙa gaba ɗaya. Hakan ne ya
sa Makaɗa Musa Ɗanƙwairo Maradun yake bayyana wa al’umma cewa, akwai wani makaɗi da yake sace
masa waƙa idan ya talitta ta. Inda yake cewa:
Jagora : Makaɗin ga mai ruwan
gahiya.
Yara: Gayyatai ba
ta da sa’a,
Jagora : In nai waƙa ya sace,
Yara : Ya zam babban ɓarawo
Gindi : Mai ban
tsoro Sadauki,
: Hassan ɗan Shehu Malam.
(Musa Ɗanƙwairo Maradun: Waƙar Hassan Usman Ciroman Katsina).
Kasancewar waƙoƙin baka na fada suna da faɗi musamman idan
ana buƙatar a fayyace abubuwan da suka ƙunsa a farfajiyar nazarin al’adun Hausawa. Don haka aka
ga dacewar mayar da hankali a kan wasu tubalai da mawaƙan suke amfani da su. Wannan dalili ya sa aka taƙaita nazarin a kan tubalan yabo da zuga da kuma na roƙo.
4.1 Yabo
Yahya, (1997:117) yana da ra’ayin cewa,
jigon yabo yana da fuskoki guda shida (6) da mawaƙi kan bi ya gina saƙonsa. Waɗannan jigogi kuwa
su ne: Addini da jarumta da mulki da asali da kyauta da kuma hali na gari. Wannan
magana da ta yi daidai da tunanin Gusau (2008:376) a inda yake fayyace yabo da
cewa: “Ambaton kalmomin sambarka da nuna amincewa da hali ko wani abin da mutum
ya yi na gari.” Kodayake Gusau, (2008:376) yana da ra’ayin cewa, akan gina
turken yabo ta hanyar amfani da tubalai waɗanda suka haɗa da addini da
asali da nasaba da kyauta da karimci ko baiwa da iya mulki da jarumtar yaƙi da hali da ɗabi’a da kirari da roƙo da habaici da kuma zambo ga wani. Waɗannan bayanai na
masana sun tabbatar da cewa, waƙoƙin baka na fada kusan ana iya cewa, tubalin yabo ya kere
kowane a cikinsu. Don haka wannan takarda ta fi mayar da hankali a kansa.
4.1.1 Yabo ta Fuskar Addini
Addini a wannan takarda yana nufin
tafarkin Musulunci. Mawaƙan baka na fada
suna dubin tushen fadojin da suke wa waƙoƙi da cewa sun kafu ne a dalilin jihadin Shehu Usmanu
Danfodiyo da almajiransa. Wannan dalili ya sa kowane lokaci sukan yi ƙoƙarin su ga cewa, sun gina waƙoƙinsu da tubalin yabo ta fuskar addini.
Sukan yi haka ne da manufar nusar da al’umma inda aka fito, da kuma wurin da
aka dosa. Baya ga haka, yin hakan yakan ƙara zama wani
hannunka-mai-sanda dangane da tushen waɗanda suka gada, saboda kada su bari
wuta ta mutu a hannunsu.
Ga al’adar mawaƙan baka na fada, bayan sun yabi sarkinsu da daraja da kuma buwaya, sukan yi
ƙoƙarin fito da
halayensa domin su tabbatar wa da al’umma cewa, ba banza ba ƙuda a kan warki. Wato, buwayar da ɗaukakar da yake da
ita suna da alaƙa da ɗabi’u da halayensa
na bin addini. Kasancewar Sarakunan ƙasar Hausa suna ƙarƙashin daular Shehu
Usmanu Ɗanfodiyo, makaɗan sukan yi ƙoƙarin fito da halayensu ta fuskar bin
addinin Musulunci sau-da-ƙafa. Don haka a
kowane lokaci sukan bayyana ƙoƙarinsu na kauce wa ayyukan da addinin Musulunci bai
aminta da su ba. Misali, Sa’idu Faru yana yabon Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo da ƙin aminta da mu’amala da barasa (giya) da taba sigari da
sauran ayyukan ɓarna. Ga abin da yake cewa:
Jagora: Da biskit da minti da taba sigari,
Yara: Biskit da
minti da taba sigari,
: Da lemu da soda
da kwalbat sitawut,
: Bai ya da aza su
ko sau guda ba,
: Ya ɗau wasiccin da
Usmanu yac ce,
: Abincinsu ba
namu ne ba,
: Yawanci abinci
daɗi gare shi,
: Kowanenmu ne yai
ta ci ba ruwanai,
: Wancan na ci sai
ta ci bai ci can ba.
Gindi: Bajimin
gidan Bello Mamman na Yari,
: Sarkin Kudu
Macciɗo ci maraya.
(Sa’idu Faru: Waƙar Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo).
Makaɗa Musa Ɗanƙwairo Maradun ya
yi amfani da wannan hikima inda ya ƙulla wasu ɗiyan waƙa da suke da zumunta da zaren tunanin fasahar Sa’idu Faru
dangane da ɗabi’un Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo na riƙo da addinin Musulunci inda yake cewa:
Jagora : Macciɗo shiryayyen ɗan sarki,
Yara : Ba ya kaba’ira Mamman,
:
Sannan ba ya shan giya,
: Ƙarya ka ganai yana caca,
: Ƙarya ka ga nai yana karta,
: Daga alheri sai fa addini.
(Musa Danƙwairo Maradun: Waƙar Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo).
A wata waƙa ta daban kuma
yana cewa:
Jagora : Mamman ba ya yin batun banza,
Yara: Maganar da duk ya faɗa ma ta zauna.
Jagora/Yara: Mamman ba ya caca ba ya
riya,
: Kuma ba ya ‘yan shaye-shayen zamunna.
Gindi : Jikan Hassan Sarkin Kudu,
: Gagarau mai jiran daga Mamman.
(Musa Ɗanƙwairo Maradun : Waƙar Sarkin Musulmi
Muhammadu Macciɗo).
4.1.2 Yabo ta Fuskar Zuga
Wannan nau’i na yabo yana ɗauke da wasu
kalmomi da sukan nuna wanda ake yi wa waƙa sama yake da duk
takwarorinsa. Sakamakon haka Yahya, (1997:131) ya nuna irin wannan yabo yana
sosa zuciyar basarake har ta kai shi ga jin ya fi kowa kuma mai aikata abin da
ya ga dama ne ba tare da samun wani mai iya tare shi ba. Misalin irin wannan
nau’i na yabo a zumuntar mawaƙa shi ne:
Jagora : Dandikko yana can yaj jiya,
: Wannan magana ta tabbata,
: Duk inda rana ta fita Gabas,
: Har inda rana taka faɗuwa,
: Dut ɗai na jikan
Danhodiyo,
: Babu wurin da mulkinai yats tsaya.
Gindi:
Kana shire baban ‘yan ruwa,
:Na Bello jikan Ɗanhodiyo.
(Sa’idu Faru: Waƙar Sarkin Musulmi
Muhammadu Macciɗo).
A wannan ɗan waƙa, makaɗa Sa’idu Faru ya nuna duk duniyar
Musulmi tana ƙarƙashin mulkin Sarkin Muslmi Muhammadu Macciɗo. Don haka kowane
Sarki yana ƙarƙashin ikonsa ne, wato tamkar hakimi ne a wurinsa. Makamancin wannan yabo na
zuga dai Makaɗa Musa Ɗanƙwairo Maradun da Amadu Mailauni Bakura sun yi shi a wasu daga cikin ɗiyan waƙoƙinsu. Danƙwairo ya yi wa Sarkin Musulmi Macciɗo irin sa, yayin da shi kuma Amadu
Mailauni Bakura ya yi wa Sarkin Musulmi Ibrahim Dasuƙi. Ga bin da suke cewa:
Jagora : Ɗan Sardauna jikan Hasan,
Yara : Ci banza ubangijin Yari.
Jagora : Da inda rana ke fitowa,
: Har inda rana taka faɗuwa,
: Gabar da Yamma dama da hauni,
: Mamman mulkinku ya kai can,
Jagora/Yara : Indai akwai masu yin
salla.
Gindi : Ɗanmaigayya na Jekada,
: Mamman ya wuce reni.
(Musa Ɗanƙwairo Maradun: Waƙar Sarkin Musulmi
Muhammadu Macciɗo).
Shi kuma Makaɗa Amadu Mailauni Bakura yana cewa:
Jagora:
Dam mahitar rana,
: Har a kai mafaɗa,
: Baba dun ga naku na,
: In dai maisalla ne,
: Baba kai Allah yab ba.
Yara
: Babu yanzu duw wani mai mulkinmu ban da kai.
Gindi : Ibrahim Jikan Mujadadi,
: Kai kag gaji Hassan da arziki.
(Amadu Mailauni Bakura: Waƙar Ibrahim Jikan Mujaddadi)
A waɗannan ɗiyan waƙoƙi da aka kawo, duka mawaƙan guda biyu, sun yi zumunta da Sa’idu Faru ta fuskar
yabo mai ɗauke da zuga, inda suke nuna tun daga mahudar rana har zuwa faɗuwar ta suna ƙarƙashin mulkin Sarkin
Musulmi. Wannan yana da manufar suna son su nuna gaba ɗaya duniyar
Musulmi yake mulka ba iya daular Shehu Usmanu Danfodiyo ba. Hakan ya sa suka yi
amfani da kalmar mahudar rana, wato gabashin duniya, zuwa mafaɗar ta, wato
yammacin duniya ke nan.
A ɓangare ɗaya kuma, makaɗa Sa’idu Faru ya
yabi Sarkin Musulmi Macciɗo ta hanyar zuga kamar yadda Salihu
Jankiɗi ya yi wa Sarkin Musulmi Abubakar na III. Haƙiƙa an samu zumunta idan aka dubi yadda
makaɗan suka tsara ɗiyan waƙoƙin yabon nasu inda suke nuna irin
buwayar da Allah ya yi wa iyayen gidan nasu ta hanyar lissafo wasu abubuwa da
suka keɓanta da su. Ga yadda suke cewa:
Jagora: Wanna ɗan sarki yak
kammala bai kai ga Macciɗo,
Yara:
Girma Allah yai ma da yawa baba duniya.
Jagora: Kashi bakwai kak kwasa ‘yan
sarki na kallo.
Yara:
Gidan gwani kai kak kai ga irin wagga maslaha.
Jagora: Ga ka ɗan mai daraja,
:
Ga ka jikan Usmanu Kurɗabi na Hodiyo,
:
Ga ka Sarkin nasara,
: Ga ka Alhaji Macciɗo,
: Ga jikka ta yi dubu,
: Ga ka mallami kake,
: Ga ka mummuni kake,
: Ga ka ba ka za’ida,
: Abin da du Allah kai wa mutum,
: Baba yai maka.
(Sai’du Faru: Waƙar Sarkin Musulmi
Muhammadu Macciɗo).
Shi kuwa makaɗa Salihu Jankiɗi a waƙarsa ta Sarkin Musulmi Abubakar na III yana cewa:
Jagora:
Wa ka dambe da mai ƙarhi tara?
Yara: Kai na Allah kai na Ma’aiki,
: Ga jihadi ga alheri,
: Ga hanƙuri ga ƙarhin arzuki,
: Ga muhibba inda Abubakar,
: Rabbu Allah yai ma ɗaukaka.
Gindi : Abubkar ɗn Shehu Baƙadire,
: Na Bello sai Madi ko ba a so.
(Salihu Jankiɗi: Waƙar Sarkin Musulmi Abubakar na III).
Bugu da ƙari, mawaƙan baka na fada sukan yi amfani da wasu
abubuwa a matsayin kinaya domin fito da darajar iyayen gidansu. Misali, Makaɗa Sa’idu Faru ya
yi amfani da gizago[5] wajen zuga Sarkin Zazzau
Alhaji Shehu Idris. Ga abin da yake cewa:
Jagora: Shehu gizago ba ka da sabo,
Yara:
Mai sassaƙa tsare hannunka,
: Don ka da a sassaƙe ma hannu.
Gindi: Gagara gasa bajimin Marafa,
: Shehu halaliyar gidan Sambo,
: Allah ya biya maka buƙata,
: Kai ab babba ga gidan Sambo.
(Sa’idu Faru: Waƙar Sarkin Zazzau
Shehu Idris).
Makaɗa Musa Ɗanƙwairo Maradun ya
yi amfani “gizago” a matsayin abin da ya yi kinaya da shi wajen yabon Sarkin
Zazzau Shehu Idris kamar yadda Sa’idu Faru ya yi, inda yake cewa:
Jagora : Gizago ba ka da sabo wandara,
: Mai sassaƙa tsare hannunka,
Yara : In ka ƙiya ya jima,
: Mis sha min kai.
Gindi
: Ba maza kashi tilas su bi ka,
: Malam ɗan Idirisu.
(Musa Ɗanƙwairo Maradun: Waƙar Sarkin Zazzau).
Ga al’adar mawaƙan baka na fada, sukan zuga sarakunansu ta hanyar kamanta su da zuma ko maɗi da sauransu.
Kodayake a kowane lokaci sukan mayar da sarakunan nasu zuma wasunsu kuma maɗi ko kuma maɗaci. Misali,
Jagora: Kuma in batun zaƙi a kai,
Yara: Kowa naz zuba ruwan zuma,
: Ba shi ko ta batun maɗi
Gindi: Farin cikin Musulmin duniya,
:
Mai martaba na Abubakar,
: Ci banza Alhaji Macciɗo.
(Sa’idu Faru: Waƙar Sarkin Musulmi
Muhammadu Macciɗo).
Haka shi ma Makaɗa Ibrahim Narambaɗa ya yi amfani da
wannan zuga, inda ya kamanta Sarkinsa (Sarkin Gobir Amadu) da zuma da damen
gero da rago. Abokan hamayyarsa kuma ya kamanta su da maɗi da kwandon wake
da kuma ɗan akuya[6]. Ga abin da yake cewa:
Jagora: Maɗi bai kai ga zuma
ba,
Yara: Kowal lasa shi ka hwaɗi.
Jagora: Kwandon wake bai kai ga damen
gero ba,
: Ɗan akuya ko ya yi ƙahonai,
: Ya san bai yi kamar rago ba.
Gindi: Gogarman Tudu jikan Sambo,
: Maza su ji tsoron ɗan mai Hausa.
(Narambaɗa: Waƙar Gogarman Tudu).
4.1.3 Magori Wasa Kanka da Kanka (Bugun Gaba)
Mawaƙan baka wani lokaci idan waƙa ta yi musu daɗi sukan yi wata
‘yar gayauna su yabi kansu saboda hikimar da suke da ita. Sukan yi haka ne
domin su gwada wa maigidansu (Sarkinsu) cewa ta ɓangarensu na waƙa su ma ba kanwar lasa ba ne. Don haka, sukan bayyana
baiwar da Allah ya yi musu ta fasaha a cikin ɗiyan waƙoƙinsu a lokacin da suke yabon iyayen
gidansu. Makaɗa Sa’idu Faru ya bi sahun mawaƙan baka na fada wajen
bayyana fasaharsa tare da yabon kansa kamar yadda mawaƙan da suka gabace shi suka yi. Ga abin da yake cewa:
Jagora: Sa’idu Malamin waƙa,
Yara: Mai kwana ɗumi na Mamman na
Balaraba.
Jagora: Ban wuce gonata da irina ba,
Yara: Inda sarkin Kudu nitc tsaya.
Gindi: Farin cikin Musulmin duniya,
:
Mai martaba na Abubakar,
: Ci banza Alhaji Macciɗo.
Al’adar kowane mawaƙin sarakuna ne ya ambaci kansa da malamin waƙa, saboda a tunaninsu nan ne magaryar tuƙewar darajar da ake so a kai a wannan fage. Don haka
Sa’idu Faru ya yi amfani da hikimarsa wajen samo ɗiyan waƙar da za su amsa wannan guri nasa kamar yadda makaɗan da suka gabace
shi suka yi. A dai wannan hauji, ga abin da makaɗa Ibrahim Narambaɗa yake cewa:
Jagora: Ke tahi
Jekadiya hwaɗa mishi baƙonsa ya zaka,
Yara: Ba samna ba
ne Narambaɗa na Malamin kiɗi,
: In ya ce maraba
mui ta kiɗi har mu kwan bakwai.
Gindi : Ɗan Isiyaku Makaye,
: Jafaru mai halin
mazan jiya zamna da lafiya.
(Ibrahim Narambaɗa: Waƙar Sarkin Zazzau Jafaru).
Haka abin yake ta fuskar zumunta a
wurin mawaƙan baka. Shi ma makaɗa Musa Ɗanƙwairo Maradun a
wannan batu na matsayin malamin waƙa yana cewa:
Jagora : Na shigo Daura Ɗanƙwairo,
: Ana ta murna ana ta taɗi.
Yara: Sun ga Ɗanƙwairo uban ɗumi.
Jagora: Na shigo Daura mai guru ,
: Ana ta murna ana ta taɗi,
Yara: Sun ga Ɗanƙwairo uban ɗumi.
Jagora/Yara: Malamin Waƙa Ɗanƙwairo,
:
Sabon hwaihwai na sunka wallafa.
Gindi:
Shirinka ba ɗai da nasu ba,
: Na Audu giwa abin biya.
(Musa Ɗanƙwairo: Waƙar Sarkin Daura)
4.1.4 Roƙo
Kasancewar roƙo ɗaya daga cikin tubalan da ake gina waƙoƙin baka na fada da su, don haka ba a cika ƙare waƙa ba tare da an ji
motsinsa ba. Da yake buƙatar dara kasawa, mawaƙan baka suna talitta waƙoƙinsu ne da manufar roƙon biyan wasu buƙatunsu a wurin
iyayen gidansu. Don haka, CNHN (2006:374) ya fassara roƙo da: “Sana’ar maroƙa ta yi wa mutane kirari ko yabo a yi
musu kyauta, ko kuma nenan kyauta daga wani.” Mawaƙan baka sukan ƙulla zumunta ta sigar zaɓen kalmomin da
sukan roƙi wani abu daga iyayen gidansu.
Kasancewar ba kowane lokaci mawaƙin baka yake roƙon abu kai tsaye ba, sukan gina tubalin roƙo ta hanyar bayar da labari da dangoginsa. Misali, Sa’idu
Faru ya yi amfani da wata hikima da Musa Ɗanƙwairo Maradun ya yi amfani da ita a lokacin da yake roƙon mota a waƙarsa ta Janar
Hassan Usman Katsina. Ga abin da Sa’idu Faru yake cewa:
Jagora : Manyan ma’aikatan gwamnati,
: Manyan ma’aikatan NA
: Almajirinku na an nan,
: Nan bisa gare ku Allah yas shirya
muna abinci,
: Na roƙe ku in da hali don shirya muna,
: Kujera ta mu je hajji.
Yara : Na yi mafarki nai salla makka
nai ɗawafi,
: kuma na rungumo mahwarki firami da
bagaruwa,
: An ce mini Alhaji Baitul hajji naz
zaka.
Jagoa: Wanga mafarki ya Allah yan nufa
: A shirya shi ya zan haka.
Gindi : Farincikin Muslmin duniya,
:
Mai martaba na Abubakar,
: Ci fansa Alhaji Macciɗo.
(Sa’idu Faru: Waƙar Sarkin Musulmi Muhammadu Macciɗo).
A cikin waɗannan ɗiyan waƙa, Sa’idu Faru ya yi amfani da wata al’ada ta ɗan’adam ta mafarki
wadda takan bayyana masa wani abu da yake da burin samu ko kasancewa a cikin rayuwarsa.
Shi ma Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya yi amfani da mafarki inda ya roƙi mota a wurin Janar Hassan Usman Ciroman Katsina. Ga abin da yake cewa:
Jagora : Ɗanƙwairo na yi mafarki,
Yara
: Ina jin ƙarar inji ko mota za a ba ni.
Jagora : Ƙwairon an ba ka mota,
: An koma an ba ka mota,
: Sai Alhaji Bukar Mandara
: Ya ce ya ba ka mota
Gindi : Baban dodo sadauki,
: Hassan ɗan Shehu Malam.
(Musa Ɗanƙwairo: Waƙar Hassan Usman Ciroman Katsina).
5.0 Sakamakon Bincike
Wannan bincike ya gano wasu sakamako a ƙarshensa. Wasu daga cikin sakamakon da wannan bincike ya iya
ganowa sun haɗa da:
i.
Mawaƙan baka na fada suna amfana da waƙoƙin junansu inda sukan sarrafa kalmomi masu alaƙa da juna wajen waƙe iyayen gidansu.
ii.
Nazarin ya gano cewa, akwai bambanci a
tsakanin satar waƙa da waƙeƙeniya da kuma zumuntar waƙa. Satar waƙa ta rataya a kan
kwashe abin da wani mawaƙi daban ya rera ba
tare da nuna naƙaltar waƙar aka yi daga gare shi ba. Ita kuma waƙeƙeniya takan mayar da hankali ne ga
mayar da martani a tsakanin mawaƙa. Saɓanin zumuntar waƙa, wadda ita kuma ta dogara ne ga amfani da wasu tsirarun
kalmomi ko kuma salailai da wani mawaƙi ya yi amfani da
su a waƙar da ya rera.
iii.Haka kuma, binciken ya gano cewa, ƙunshiyar tunanin al’umma zai iya zama guda ɗaya, musamman idan aka lura da yanayin
waƙoƙin makaɗanmu na fada.
Wannan dalili ya sa wannan takarda take hasashen al’umma za su iya haɗa kansu su zamanto
masu murya guda inda za su iya bayyana abin da suke buƙata a wurin shugabanninsu.
iv.Bugu da ƙari, binciken ya gano tabbacin maganar Hausawa da ke cewa: “Wurin da saniyar gaba ta sha ruwa, ta baya ma nan za ta
sha.” Sakamakon da yawa daga cikin mawaƙanmu na baka sukan
dafi kafaɗun magabatansu wajen samun hasken tsara tasu waƙar. Wannan ya nuna cewa, dole sai mun yi biyayya ga magabatanmu kafin mu
iya fito da wani abu na fasaharmu.
v.
Waƙoƙin mawaƙanmu na fada tamkar wata fitila ce da ke haska mana tsarin iko da halayen
magabatanmu na jiya waɗanda muke fata su zama ababen koyinmu a
yau. Don haka nazarin ya gano cewa, kowane mawaƙin fada yana ƙoƙarin fito da
kyawawan halayen maigidansa na karamci da haƙuri da riƙo da addini da dangoginsu. Ƙoƙarin kwatanta abubuwan da suka ƙunsa zai iya zama hanyoyin warware matsalolinmu a yau.
5.1 Shawarwari
Gaskiyar Hausawa da sukan ce: “Mai
shawara aikinsa ba ya ɓaci, sai dai ba shi da rufin asiri.”
Wannan maƙala tana da tunanin bayar da sharwarin
da suka haɗa da:
i.
Akwai buƙatar ƙara faɗaɗa bincike a kan
fito da batutuwan da suka shafi al’adun Hausawa da suke ƙunshe a waƙoƙinmu na baka.
ii.
Wannan takarda tana ƙara bayar da shawara ga magabatanmu a tashi tsaye wajen ƙara sanya fasahohin mawaƙanmu na baka a cikin manhajojin makarantunmu tun daga firamare har ya zuwa
Jami’o’inmu[7].
iii.
Muna kira ga waɗanda suke da
ilimin kwamfuta a cikinmu da su ɓullo da wasu manhajoji da za a riƙa jin muryoyin mawaƙanmu na baka irin
su Sa’idu Faru, Salihu Jankiɗi, Ibrahim Narambaɗa da kuma Musa Danƙwairo da Aliyu Ɗandawo Shuni da
sauransu da dama.
iv.
Ci gaba da haɗa irin wannan taro
ta hanyar zaƙulo mawaƙanmu na baka tare da baje kolin fasahohinsu kamar yadda aka yi a yau, shi
ma abin a yaba ne, kuma ana bayar da shawarar a ci gaba da haka.
5.2 Naɗewa
Wannan takarda ta mayar da hankali ne ga fito
da zumuntar waƙa da ke tsakanin Makaɗa Sa’idu Faru da
takwarorinsa mawaƙan fada. Maƙalar ta lura da cewa, adawa a tsakanin mawaƙa ita ce takan haifar da waƙeƙeniya. Kamar yadda rashin fasaha ga mawaƙi kuma kan haifar da satar waƙa. A ɓangare ɗaya kuma, kyakkyawar zamantakewa da mu’amalantar juna cikin girmamawa da
aminci ita ce takan haifar da zumunta a tsakanin mawaƙa. Hakan kuma shi ne yake jawowa sukan yi amfani da wasu kalmomi da suka
fito a waƙoƙin junansu domin ƙulla tasu waƙar. Don haka,
wannan bincike yake ganin kasancewar mawaƙan nahiya ɗaya da dacewar
ra’ayi da kuma ta sana’a su ne suka haɗu suka samar da zumuntar mawaƙa. Don haka ba abin mamaki ba ne idan an samu zumuntar waƙa a tsakanin Sa’idu Faru da mawaƙan fada takwarorinsa, musamman ta fuskar tubalan da ake gina waƙoƙin fada da su waɗanda suka haɗa da: Yabo da zuga
da kuma roƙo.
Manazarta
Bunza, A. M. (2006).
Gadon Feɗe Al’ada. Lagos: Tiwal Nigeria Limited.
Bunza, A. M. (2009). Narambaɗa. Lagos:
Al-Ibrash Publication Plc.
C.N.H.N.
(2006). Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero. Zaria: Ahmadu Bello University
Press.
Ɗangambo, A. (1984). Rabe-raben
Adabin Hausa da Muhimmancinsa ga
Rayuwar Hausawa. Kano: Triumph.
Furniss, G. (1996). Poetry, Prose and
Popular Culture in Hausa. Edinburgh: Edinburgh University Presss Limited.
Gusau,
S. M.
(2005). Makaɗa da Mawaƙan Hausa. Kano: Benchmark Publishers.
Gusau,
S. M.
(1993). Jagoran Nazarin Waƙar
Baka.
Kaduna: FISBAS Media Services.
Gusau, S. M. (2002). Sarkin
Taushi Salihu Jankiɗi. Kaduna: Baraka Publishers Limited.
Gusau, S.M. (2008). Waƙoƙin Baka a
Ƙasar Hausa: Yanaye-Yanayensu
da
Sigoginsu. Kano: Benchmark
Publishers Limited.
Gusau,
S. M.
(2009).
Diwanin Waƙoƙin Baka Zaɓɓun Matanoni na Waƙoƙin Baka na Hausa.
Kano: Century Research
and Publishing
Limited.
Ibrahim, M. S. (2003). Kowa ya sha kiɗa (Abokin Hira na 2). Lagos: Longman Nigeria Plc.
Kafin-Hausa, A. U. (2002). Koma-baya a
Waƙoƙin Hausa: Waƙoƙin Sarauta. Cikin Bichi, A. Y. Da wasu.
Studies in Hausa Language, Literature and
Culture the Fith Hausa International Conference Pp.241-255. Centre for the
Study of Nigerian Languges, Bayero Uniersity, Kano. Kano: Benchmark Publishers.
Muhammad, D. (1980). Zumunta Tsakanin
Marubuta Waƙoƙin Hausa da Makaɗa. Cikin Yahaya,
I. Y. da wasu (editoci) Harsunan Nijeriya
na X Pp. 85-102. Centre for the Study of Nigerian Languages, Bayero
University, Kano.
Muhammad, M.S.
(1997). Zumuncin Bahaushe. Kudin Digiri na Ɗaya (B.A). Sakkwato: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Tsoho, M. Y.
(2004). Waƙeƙeniya Ko Yaƙeƙeniya: Nazari Kan Yaƙi da Waƙa a Waƙoƙin Baka. Harshe Journal of African languages, Vol. 2 Pp.86-99. Department of
Nigerian and African Languages, Ahmadu Bello University, Zaria. Zaria: Ahmadu
Bello University Press.
Yahya,
A. B. (1997).
Jigon Nazarin Waƙa. Kaduna: Fisbas Service.
Yahya, A. B. (2001). Salo
Asirin Waƙa. Kaduna: Fisbas Service.
Waƙoƙi da Abubuwan da Aka Saurara
1.
Waƙoƙin Makaɗa Sa’idu Faru
2.
Waƙoƙin Makaɗa Salihu Jankiɗi.
3.
Waƙoƙin Makaɗa (Dr.) Ibrahin
Narambaɗa.
4.
Waƙoƙin Makaɗa Musa Ɗanƙwairo.
5.
Waƙoƙin Amadu Mailauni Bakura
6.
Waƙoƙin Makaɗa Sani Aliyu Ɗandawo.
7.
Waƙoƙin Abdu Nabiddigau Maigambara.
8.
Sauraren Hirar da Rediyon Tarayya na
Kaduna (FRCN, Kaduna) ta yi da Alhaji Ibrahim Muhammad Ɗanmadamin Birnin Magaji a kan Tarihin Rayuwar Makaɗa Sa’idu Faru a
shekarar 2019.
[1] Makaɗa Abdu Naburdugau mai gambara yana cewa:
Jagora: Sarkin noman gari shi da maƙerin gari,
Wanzamin gari, wa za ya raba su?
[2] Domin ƙarin bayani, a dubi Muhammd, D. (1980), Zumunta Tsakanin Marubuta Waƙoƙin Hausa da Makaɗa. Cikin Harsunanan Nijeriya na X , Jami’ar Bayero, Kano. Maƙalar ta fito da zumuntar da ke tsakanin marubuta waƙoƙi da makaɗa, inda aka kawo misalai daga waƙoƙi 30 waɗanda wasu mawallafa 12 suka ari kari daga makaɗan baka. Maƙalar ta nuna cewa, ba da karin Larabci kaɗai Mawallafa suke tsara waƙoƙinsu ba, suna arowa daga makaɗan baka.
[3] Hira da Alhaji Ibrahim Muhammad Danmadamin Birnin Magaji a Gidan Rediyon
Tarayya na Kaduna (FRCN Kaduna) a shekarar 2019.
[4] Yanzu (2024) garin Faru yana ƙarƙashin Ƙaramar Hukumar Mulki ta Maradun da ke jihar Zamfara.
[5] Abin sassaƙar turmi, (CHNH, 2006:168).
[6] Don neman ƙarin bayani a dubi, Bunza, A. M. (2009:171), Narambaɗa. Lagos: Ibrash Islamic Publication Centre.
[7] Wannan takarda ta sani akwai manyan malamai da suke ta wannan ƙoƙari, amma dai muna roƙonsu da suka ƙara ƙaimi wajen wannan aiki nasu, saboda kada wuta ta mutu a
hannunmu.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.