TAMBAYA (230)❓
Assalamualaikum. Dan Allah INa da tambaya tambaya na shi ne mene ne hukunci Wanda ya sa kayan sata Amman daga baya sai ya zo ya yi nadama shin Malam ya matsayin to tubarsa
AMSA❗
Waalaikumus
salam, warahmatullahi, wabarakatuhu
Allaah
Azzawajallah yana yafe kowanne irin laifi in dai ba wanda mutum ya mutu yana
shirka ba da kuma laifin dake tsakanin bawa da bawa
Wannan hakki
ne kuma idan ba a biya mai shi anan duniyar ba to ranar lahira za a biya mai
kayan da sallah, azumi ko sadakar wannan wanda ya danne masa hakkin
Idan kuma
ladan ba su kai na hakkin ba to za a dauki zunubban mai kayan a jibgawa wanda
ya dannewa hakkin
Don haka a
shawarce a gaggauta mayarda kayan ga mamallakin sa
Idan kuma ba
a san inda za a same shi ba sai ayi sadaka da niyyar Allaah ya sa ladan a
mizanin mai kayan
Wallaahu
taala aalam
Amsawa:
Usman
Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.