𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Malam ya karatu ya dalibai, Malam tambaya ce idan Maniyyi ko maziyyi ya zuba atufa ko jiki najasa ne ko ba najasa bane? Allah Kara ilimi.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa
alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Farko
dai akwai saɓanin malamai game da hukuncin shin maniyyi najasa ne, ko ba najasa
bane?
Kuma
saɓanin ya samo asali ne daga fahimtar da malamai suka yiwa wasu hadisai guda
biyu waɗanda aka riwaitosu duk daga Nana A'ishah (rta).
Tace
: "Na kasance ina wanke janabah (wato maniyyi) daga tufafin Manzon Allah
Sallallahu alaihi Wasallam sai ya fita zuwa sallah alhali gurbin ruwan yana
jikin tufafinsa".
Da
kuma hadisin da tace "Na kasance ina kankareshi (da farcena) daga tufafin
Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam kuma yayi sallah acikinsa".
Duk
wadannan hadisan akwaisu cikin Bukhariy da Muslim da wasu litattafan.
Maluman
Mazhabin Shafi'iyyah da Hanbaliyyah da kuma Sufyanuth Thauriy da Abu Thaur
sunce maniyyi ba najasa bane. Hujjarsu ita ce Nana A'ishah tace tana kankareshi
daga tufafin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam. Kuma da ace maniyyi ba
tsatsarka bane, da kankarewa Kaɗai bazata isar ba. Kuma wannan ita ce fatawar
manyan Sahabban Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam irin su Sayyiduna Aliyu
bn Abi Talib, da Abdullahi bn Abbas, da Abdullahi bn Umar, da Sa'adu bn Abi
Waqqas da ita kanta Nana A'ishah (Allah ya yarda dasu baki ɗaya).
Imam
Malik da Imam Abu Hanifah (Allah ya jikansu) sun ce maniyyi najasa ne. Hujjarsu
ita ce hadisin da Nana A'ishah (ra) tace tana wankeshi daga tufafin Manzon
Allah Sallallahu alaihi Wasallam. Kuma sun ce saboda yana fita ne daga mafitar
fitsari. Kuma tunda fitsari najasa ne, don haka shima najasa ne.
Amma
gaskiya waccen fatawar ta farko (fatawar Shafi'iyyah da Hanbaliyyah) tafi
Qarfin hujjah mai karfi tare da cewa ta samu tushe daga sahabbai (Allah ya
yarda dasu).
Amma
babu saɓani cikin wajibcin yin wanka saboda fitarsa ta hanyar mafarki ko a
farke ta dalilin jima'i ko motsuwar sha'awa ko shafa, ko kallo.
Shi
kuwa maziyyi, dukkan maluman fiqhu sunyi ittifaki akan cewa najasa ne shi. Kuma
idan ya taɓa tufafi wajibi ne sai an wankeshi.
Don
karin bayani aduba littafin Ta'aseesul Ahkam na Shaikh Ahmad bn Yahya Annajmiy
(juzu'i na daya shafi na 86 zuwa na 87)da kuma shafi na 62 - 63.
WALLAHU
A'ALAM.
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
HUKUNCIN SUTURAN DA MANIYYI YA TAƁA
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
malan
da fatan kana lafiya tambayace dani tambayata itace ya masayin suturan da
manniyi yataba wanne irin wanke akeyi mata ruwa ba sabulu ko ba omo?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
To
ɗan uwa shi kansa maniyyin Malamai sun samu saɓani dangane da hukuncinsa ma'ana
Shin maniyyin Najasane ko ba najasa bane?
Wasu
malaman sun tafi akan cewa naniyyi najasa ne, inda kuma Wani ɓangare na malamai
sukace maniyyi ba najasa bane, amma dai fahimtar da muke kai ita ce fahimtar
malaman da suka tafi akan cewa Maniyyi ba najasa bane.
sabida
haka idan miniyyi ya taɓa tufafi ya halatta ayi sallah da tufafin mustahabbi ne
a wankeshi Amma dai ba najasa bane, Saidai kuma fitarsa ta hanyar Jima'i,
Mafarkin suduwa ko wasa yana wajabta wanka. Sabida haka idan mutum ya wanke
maniyyin to shine yafi, sai ba dole ne sai an sanya sabulu ko omo yayin
wankewar ba idan an wanke da ruwa ya wadatar
Domin
neman karin bayani dangane da hukuncin maniyyin Sai a duba Al'mugni na Ibn
qudama (1/736)
WALLAHU
A'ALAM
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
SHIN MANIYYI YANA FITO WA MACE
TAMBAYA (184)❓
Mace BUDURWA maniyyi yana fito mata?
AMSA❗
Tambaya Mai muhimmanci
Kamar yanda Namiji yake fitarda: Maniyyi, Mazy da Wady haka itama mace
take fitarda wadannan abubuwan guda 3
Indai Mazy da Wady suka fita daga gabanta to wanke gabannata zatayi
kawai
(Fatawa al-Lajnah al-Daa’imah.)
(Fatawa al-‘Ulamaa’ fi ‘Ushrat al-Nisaa’, p. 37)
Shaikh Saleh al-Fawzaan yace: Idan wani abu ya fito daga gaban mace
silar kissing da Mijinta zaiyi Mata ko Kuma Wasa da ita to anan bazatayi wanka
ba, a inda zatayi wanka shine idan maniyyi ya fito
(Fatawa al-Mar’ah al-Muslimah, 1/222)
Shan maniyyi ba Haramun bane ba saidai abin qyama ne laakarida
yanayinsa Kamar majina yake Kuma an qyamaci Shan majina saboda ko yarone kikaga
Yana Shan majina zakice Kai kaidai kam ka fiya qazanta
Ballantana Kuma Miji ya Sha na Matarsa dukda dai cewar Shan sa din ba
Haramun baneba a Shari'ah saboda ba Najasa baneba
Ibn Qudamah yace: Shan Najasa Haramun ne
(al-Mughnee': vol. 1, p. 378)
Wallahu taala aalam
Muna muku tallar sabuwar makaranta Online mai suna: "MU'AMALAR
AURATAYYA A MUSULUNCI". Wanda yake da ra'ayin shiga yayi magana ta Private
hukumar makaranta zata turo masa tsare - tsare da dokokin shiga
(WhatsApp: 07035387476)
Subhanakallahumma wabi hamdika ash-hadu anla'ilaha illa anta
astaghfiruka wa'atubi ilayk
Amsawa:
Usman Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.