𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam Alaikum. Ko zan iya
taya kiristoci murnar bikin kirsimati, ko da a rubuce ne kamar ta sanyawa a
status da sauran kafafen sada zumunta?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul
Laah.
Kirsimeti biki ne na addini a
wurinsu, ba na al’ada ne kamar na aure ko suna ko na samun ƙarin
girma da makamantan hakan ba. Don haka ba daidai ba ne, kuma kuskure ne a haɗa a tsakaninsu a wurin
hukunci. Kuma abin da ya halatta a cikin bikin al’ada ba lallai ya halatta a
cikin bikin addini ba.
Daga nassin Alqur’ani mun ji
cewa, duk kafiran da ba su yaƙe mu a cikin addini ba, ba su fitar da mu
daga cikin garuruwanmu ba, kuma ba su taimaka a kan fitar da mu ɗin ba, waɗannan Allaah bai hana mu
sadar da alheri da kyautatawa gare su ba, kuma bai hana mu yi musu adalci ba.
لَا يَنْهٰٮكُمُ اللّٰهُ عَنِ الَّذِيْنَ لَمْ يُقَاتِلُوْكُمْ فِى الدِّيْنِ وَلَمْ يُخْرِجُوْكُمْ مِّنْ دِيَارِكُمْ اَنْ تَبَرُّوْهُمْ وَ تُقْسِطُوْۤا اِلَيْهِمْۗ
اِنَّ اللّٰهَ يُحِبُّ الْمُقْسِطِيْنَ ٨ اِنَّمَا يَنْهٰٮكُمُ
اللّٰهُ عَنِ الَّذِيْنَ قَاتَلُوْكُمْ فِى الدِّيْنِ وَاَخْرَجُوْكُمْ مِّنْ دِيَارِكُمْ وَظَاهَرُوْا عَلٰۤى اِخْرَاجِكُمْ اَنْ تَوَلَّوْهُمْۚ وَمَنْ يَّتَوَلَّهُمْ فَاُولٰۤٮِٕكَ هُمُ الظّٰلِمُوْنَ ٩
Allah bã Ya hana ku, daga waɗanda ba su yãƙe ku
ba sabõda addini kuma
ba su fitar da ku ba daga gidãjenku,
ga ku kyautata musu kuma ku yi musu ãdalci.
Lalle Allah Yanã son mãsu ãdalci. Allah Yanã
hana ku kawai daga waɗanda
suka yãke ku sabõda addini kuma suka fitar da ku daga gidãjenku, kuma suka
taimaki jũna ga fitar da ku, karku jiɓince
su, kuma wanda ya jiɓince
su, to waɗannan sũ
ne azzãlumai. (Surah: Al-Mumtahana, Ayat: 8-9)
Abu ne a fili kuwa cewa a ƙarƙashin
sadar da alheri ga irin waɗannan
ɗin akwai taya su
murnar samun aure da haihuwa, ko kuma ƙarin girma. Haka kuma taya su baƙin
ciki a lokacin asarar dukiya ko ta rayuwa, kamar lokacin mutuwar danginsu
kafirai da makamantan hakan, muddin dai hakan bai ci-karo da wata ƙa’ida daga cikin ƙa’idojin addininmu ba.
Amma kuma lallai mu yi
taka-tsantsan in ji malamai, a wurin yi musu ta’aziyya tun da shi abu ne da
yake da alaƙa da addini. A nan ba a yarda mu roƙa wa mamacinsu gafarar
Allaah ko rahamarsa ba. Sai dai kawai mu yi wa rayayyunsu addu’a, kamar ta neman Allaah ya
ƙara
musu haƙuri
da juriya, da ƙarfin zuciyar ɗaukar
nauyin rashin mamacin, da kuma fatar Allaah ya musanya musu abin da suka rasa
da wanda ya fi shi alheri.
Kamar haka Kirsimeti - da sauran
bukukuwan da suka shafi addininsu - ya ke. Taya su murna ta kowace irin hanya,
kamar ta magana ko ta rubutu ta hanyar saƙon waya na kar-ta-kwana, ko ta cikin
tashoshin social media ko gidajen rediyo da talbijin, ko ta hanyar kunna wuta
da buga abubuwan fashewa da dare, da ziyartarsu a ɗakunan bautarsu da wuraren bukukuwan, da
taimaka musu da kyaututtukan furanni ko kayayyaki ko kuɗaɗe
da makamantan hakan, waɗannan
duk haramtattun abubuwa ne. Saboda ana ɗaukar
aikata hakan kamar goya musu baya da amincewa ne da irin abin da ke cikin
mummunar addininsu da aƙidarsu ta Allantar da Annabi Isa (Alaihis Salaatu Was Salaam),
da kuma cewa Allaah (Tabaaraka Wa Ta’aala)
yana da ɗa. Wannan
kuma zagi ne mummuna gare shi (Subhaanahu Wa Ta’aala), kamar yadda hadisai
sahihai suka tabbatar. Al-Imaam Al-Bukhaariy (4974) ya riwaito da isnadinsa
sahihi har zuwa ga Abu-Hurairah (Radiyal Laahu Anhu), daga Annabi (Sallal Laahu
Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) cewa, shi ya ce
« قَالَ اللَّهُ: كَذَّبَنِى ابْنُ آدَمَ وَلَمْ يَكُنْ لَهُ ذَلِكَ ، وَشَتَمَنِى وَلَمْ
يَكُنْ لَهُ ذَلِكَ ، فَأَمَّا تَكْذِيبُهُ
إِيَّاىَ فَقَوْلُهُ لَنْ يُعِيدَنِى كَمَا بَدَأَنِى ، وَلَيْسَ أَوَّلُ
الْخَلْقِ بِأَهْوَنَ عَلَىَّ مِنْ إِعَادَتِهِ ، وَأَمَّا شَتْمُهُ
إِيَّاىَ فَقَوْلُهُ اتَّخَذَ اللَّهُ وَلَدًا ، وَأَنَا الأَحَدُ
الصَّمَدُ لَمْ أَلِدْ وَلَمْ أُولَدْ وَلَمْ يَكُنْ لِى كُفْأً أَحَدٌ ».
Allaah ya ce: Ɗan’adam yana ƙaryata
ni amma hakan bai kamace shi ba. Sanan yana zagi na, kuma hakan ma bai kamace
shi ba. Amma ƙaryatawarsa gare ni ita ce maganarsa cewa: ‘Allaah ba zai iya mayar da
ni kamar yadda ya fare ni ba.’
Alhali sauƙin
fara halitta a gare ni bai fi na maimaitawa ba. Amma zaginsa gare ni kuwa shi
ne maganarsa wai ‘Allaah
yana da ɗa.’ Alhali
ni ne Makaɗaici,
Wanda ake nufi da buƙatu. Ban haifi kowa ba, ba a haife ni ba. Kuma wani ɗaya bai zama tamkar ni
ba.
Allaah ya kare mu da zuriyarmu
daga dukkan hanyoyin hallaka.
A ƙarƙashin wannan babin ne kuma waɗansu malaman suka sako
batun cin abincin na Kirsimeti. Sun nuna rashin halaccin cin sa, domin shi ma
kamar goya musu baya da taya su murna ne a kan ɓatarsu
da ɓarnarsu.
Sai dai kuma dayake an samu waɗansu riwayoyi masu nuna
cewa waɗansu daga
cikin magabatan wannan al’ummar mai albarka sun ci, kuma har sun yi umurni da cin
irin abin da ba yankakken nama daga arnan zamaninsu ba, shiyasa waɗansu daga cikin malaman
musulunci suka yarda cewa za a iya cin na irin waɗannan
ɗin su ma.
Akwai ma waɗanda suka zaɓi cewa babu wani bambanci
a tsakanin yankarsu da Alqur’ani ya halatta (Surah Al-Maa’idah: 5) da abin da
ba shi ba na abincin wannan bikin na su. Suka ce saboda ayoyin da suka halatta
cin yankarsu ba su bambance a tsakanin na bikin addini da waɗanda ba su ba.
Amma kuma yana da kyau a riƙa
lura da hali ko yanayi na kowane zamani da wuri kafin a ɗabbaka irin waɗancan
nassoshin da yadda magabata suka yi aiki da su. Duk mun san cewa nassin da ya
halatta cin yankan Ahlul-Kitaab a haɗe
ya ke da wanda ya halatta auren matansu
اَلْيَوْمَ اُحِلَّ لَـكُمُ الطَّيِّبٰتُۗ وَطَعَامُ الَّذِيْنَ اُوْتُوْا الْكِتٰبَ حِلٌّ لَّـکُمْۖ وَطَعَامُكُمْ حِلٌّ لَّهُمْۖ وَالْمُحْصَنٰتُ مِنَ الْمُؤْمِنٰتِ وَالْمُحْصَنٰتُ مِنَ الَّذِيْنَ اُوْتُوا الْـكِتٰبَ مِنْ قَبْلِكُمْ اِذَاۤ اٰتَيْتُمُوْهُنَّ اُجُوْرَهُنَّ مُحْصِنِيْنَ غَيْرَ مُسَافِحِيْنَ وَلَا مُتَّخِذِىْۤ اَخْدَانٍۗ وَمَنْ يَّكْفُرْ بِالْاِيْمَانِ فَقَدْ حَبِطَ عَمَلُهٗۖ وَهُوَ فِى الْاٰخِرَةِ مِنَ الْخٰسِرِيْنَ
A yau an halatta muku abũbuwa
mãsu dãɗi kuma
abincin waɗanda aka
bai wa Littãfi halal ne a gare ku, kuma abincinku halal ne a gare su, da mãtã
mãsu kãmun kai daga muminai da mãtã 'yã'ya daga waɗanda aka bai wa Littãfi a gabãninku idan kun
je musu da sadãkõkinsu, kuna mãsu yin aure, ba masu yin zina ba, kuma bã mãsu
riƙon
abõkai ba. Kuma wanda
ya kãfirta da ĩmãni to, lalle ne aikinsa yã ɓãci,
kuma shĩ, a cikin Lãhira, yanã daga mãsu hasãra. (Surah: Al-Maaida, Ayat: 5)
Kuma magabatanmu sun yi aiki da
su gaba-ɗaya a sadda
da yadda suka dace ba tare da matsala ba. Amma me ya sa a yau kuma a cikin
al’ummarmu malamai suke ƙyamatar da musulmi daga irin wancan auren na matansu? Ba domin
illoli da ɓarnar da
suke ganin yana aukuwa a ƙarƙashin hakan ba ne?! Gidajen musulmi nawa ne irin wannan auren
ya ruguza ya lalata?! Gidaje nawa ne da ake neman samun zuriya ɗayyaba amma sakamakon
irin wannan auren ya koma samar da ’ya’ya kafirai zalla masu aiki da kulawa da
coci?! Laa haula walaa quwwata illa bil Laah.
Wannan ya sa na ce: Ni dai a ɗan ƙaramin
fahimtata, ba ruwana da duk kiristan da aka san yana daga cikin waɗanda ake haɗa baki da su har kuma ake
ta ƙulla
mana makirce-makircen da suka haɗa
da
(1) Ɗaukar nauyin waɗanda suke cigaba da koyon
addininmu domin lalata shi da gurɓata
shi, don ƙyamatar
da jama’arsu daga
kyakkyawar koyarwarsa, kamar su Maitatsine…!
(2) Koya wa matasanmu mummunar aƙidar
suka ko zagin sahihin addini, da zagin wanda ya zo da addinin, da wanda ma ya
aiko da addinin, kuma duk wai da sunan addinin…!
(3) Zuga matasanmu ga yin watsi
da koyarwar addinin da kyawawan halaye da ɗabi’u,
da koya musu shan ƙwayoyi da sauran hanyoyin holewa da morewa a cikin rayuwar
duniya kawai…!
(4) Kunna wutar fitinar yaƙe-yaƙe da
kashe-kashen babu-gaira-babu-dalili a cikin al’ummominmu na-kusa da na-nesa, domin hallaka jama’armu da lalata mana
dukiyoyi…!
(5) Tsare hanyoyi a yankunan da
suka fi yawa, ana fitar da masu surar musulmi daga cikin matafiya, ana karkashe
su, ana jefa gawarwakinsu da motocinsu a cikin kududdufai…!
(6) Bin mutanenmu a ƙauyuka
da rugage ana karkashewa, ana yi wa mata fyaɗe,
ana kwashe dukiyoyi da dabbobi, ana yin garkuwa da waɗansu domin neman kuɗin fansa…!
(7) Sace mana jarirai da yara ƙanana
ana haurewa da su zuwa yankin kudu, domin a tashe su a cikin wata al’ada da addinin da ba nasu
na asali ba, ko kuma a dasa musu ƙiyayyar addinin musulunci…!
(8) Zuwa gidajen marayu na
gwamnati ana karɓar
yaranmu ƙanana
da sunan ɗaukar
nauyin marayu da taimakonsu, a ƙarshe kuma a dasa musu ƙyamar
addininsu na asali…!
(9) Kai ziyara gidajen kurkuku da
asibitoci domin bayar da gudunmawa da taimako ga mabuƙata a fili, a ɓoye kuma ko a fakaice ƙoƙarin
sauya musu addini…!
(10) Ɓuya a ƙarƙashin
gina wa almajirai makarantu da ba su taimako domin wai a kyautata rayuwarsu, a
fakaice kuma ƙoƙarin amfani da su domin aiwatar da wata agenda a nan gaba…!
(11) Lalata mata da matasa ta
shigar musu da ƙwayoyi, da yaudararsu da ’yan kuɗaɗe ko samar musu da aikin
yi, ko magani ko kuma samar wa ’ya’yansu makarantu da nufin sauya musu addini!!
(12) Kashe majinyatanmu a cikin
asibitoci, ko dai ta hanyar barinsu hakan nan ba tare da kulawa ba, ko kuma ta
yi musu allurori ko kuma ba su maganin da zai ƙarasa su, da makamantan hakan.
Duk wanda na fahimci yana da hanu
wurin aikata irin wannan ta’addancin ga musulmi, ko yana taimakawa ko kuma yana
murna da farin ciki saboda an aikata irin hakan, to kuwa babu yadda zuciyata za
ta natsu da shi, har kuma in iya zama in ci abincinsa kowane iri, kuma a kowane
wuri da kowace irin ma’ana kuwa.
Ban haramta halal ba. Amma ba ni
tsammanin irin waɗannan
mugayen arnar ne Alqur’ani ya ce a ci yankansu ko a auri matansu. Kuma ban
amince cewa irin su ne magabata suka ci yankansu ko suka auri matansu ba.
WALLAHU A'ALAM
Sheikh Muhammad Abdullaah
Assalafiy
Ga masu tambaya sai su turo ta
WhatsApp number: 08021117734
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.