Ticker

6/recent/ticker-posts

Rubuta Alqur’ani Da Haruffan Boko

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As-Salaam Alaikum. Malam don ALLAH, me Malamai suka ce a kan Transliteration na Al-Qur’an?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah.

Abin da na sani dai shi ne

(i) Sahihiyar hanyar koyon Alqur’ani ba shi ne ɗalibi ya zauna a gaban malami ya biya masa, shi kuma ya ɗauka baki da baki ba?

(ii) Maimakon a tsaya koyo da koyar da Alqur’anin ta transliteration da haruffan boko din, domin wai a taimaka wa wanda ba ya gane haruffa larabci, ba gara ya zauna a koya masa da larabcin kawai ba?

(iii) Haruffan Larabci kamar harafin: (خ) da (ص) da (ض) da (ط) da (ظ) da (ع) da (غ) da (ق) da makamantansu ba su da waɗanda suka yi daidai da su a cikin haruffan boko. Idan aka je transliteration dole sai an yi bayani yadda ake furta su a larabci, a yi ƙoƙarin haɗa su waɗansu alamu ko haruffan boko domin su zama kusa da yadda ake furta su a larabci. To idan kuwa har mutum zai tsaya ya koyi duk wannan, me ya sa ba zai tsaya a koya masa na asalin ba kawai?

(iv) A mafi rinjayen fahimtata, mutane ne suka ƙare rayukansu wurin koyon boko zalla har sai da suka girmama suka tasamma tsufa, ba tare da sun iya karatun larabci ba. Kuma shiga makarantun Islamiyyah a matsayinsu ya zama musu da nauyi ko abin kunya. Shi ne suka zaɓi bin wannan hanyar. To amma kuma wannan mafita ce?

(v) Sannan tsakani da Allaah! A cikin transliteration ta yaya za a nuna ma irin wannan dattijo ko tsohon har kuma ya iya gane waɗansu muhimman ƙa’idojin tajweed, irin su idghaam da iqlaab da ikhfaa’ da hukunce-hukuncen muduud da rarrabuwansu da sauransu? A tsawon lokacin da za a ɗauka ana masa bayaninsu ba gara a koya masa da larabcin ba kawai?!

(vi) Da Allaah Maɗaukakin Sarkin ya ce:

وَلَقَدْ يَسَّرْنَا الْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ

wannan bai zama kamar zugawa ko ƙara ƙaimi ne ga wanda bai iya karatun da larabci ya je ya koya ba?

(vii) Kuma idan har baturiya za ta muslunta a halin tana da shekaru hamsin, kuma ta hardace Alqur’ani a wannan shekaru, me ya hana bahaushe ko bayerabe ko banufe ko babarbare koyo da iya karatun da larabci, ko da kuwa yana da shekaru sittin ko saba’in ne a rayuwa?!

(viii) Yanzu bai zama abin kunya mai girma ga musulmi ɗan shekaru talatin ko arba’in ko ƙasa ko sama da haka, a ce ya iya karatun dukkan littaffai da jaridu da wasiƙun turanci, har ma yana iya cin gyaran duk wani kuskuren nahawu da aka yi a ciki, amma wai bai iya karatun Littafin Allaah da larabci ba?!

(ix) Kuma mu da Allaah ya ce mana

وَمَا خَلَقْتُ الْجِنَّ وَالْإنْسَ إلَّا لِيَعْبُدُونِ

zai yiwu mu gama tsawon rayuwarmu a duniyar nan muna cin abincin Allaah, muna shan ruwan Allaah, muna shaƙar iskar Allaah amma kuma mu yarda mu mutu ba mu iya karatun littafinsa yadda yake so ba?!

(x) Yanzu a shekarunsa na wanda yake shirin gangarawa Lahira yana jin idan aka kira wani mutum a filin taron Alqiyamah kamar yadda Alqur’ani ya faɗa, aka ce masa

 قْرَأْ كِتَابَكَ

(Karanta Littafinka) yana jin da turanci ne zai ga rubutun? Kuma yana jin hujjar cewa bai iya larabci ba a ranar za ta kuɓutar da shi? Wannan kaɗai bai isa zama mai ƙara iza musulmi zuwa ga koyon karatun Alqur’ani da Larabci ba?!

Allaah ya ƙara mana ƙoƙari da ƙarin himma.

WALLAHU A'ALAM

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

Ga masu tambaya sai su turo ta WhatsApp number: 08021117734

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments