Ticker

6/recent/ticker-posts

Mijina Ba Ya Son Haihuwa, Ko Ya Halatta Na Hana Shi Kaina?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum. Malam ina da matsala tsakanina da mijina, baya son haihuwa ko saduwa muka yi saidai ya zubar da maniyinsa a waje, Ga shi kuma yarinyar mu ɗaya, ita ma bai damu da ita ba, ina da laifi In na hana shi kaina ??

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikum assalam To 'yar'uwa yana da kyau ki Sani cewa ya Halatta a samu tazara a tsakanin iyali, abin da musulunci ya hana shi ne kin haihuwa kwata-kwata, saboda babbar manufar aure shi ne hayayyafa, don a samu wadanda za su bautawa Allah.

 Zubar da maniyyi a wajan Farji ya halatta saboda hadisin Jabir wanda yake cewa "Mun kasance muna yin azalo (zubar da maniyyi a waje yayin saduwa) a lokacin da Qur'ani yake sauka, kamar yadda Bukhari ya rawaito a hadisi mai lamba ta: 4911.

Hadisin da ya gabata yana nuna cewa: Bai halatta mace ta hana mijinta kanta ba saboda hujjar yana AZALO, tun da Alqur'ani bai haramta ba.

Saduwa rukuni ne babba a aure, Wannan yasa Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce: (Mace ta amsa kiran mijinta ko da tana kan kaskon tuya ya kira ta, sannan la'ana ta tabbata ga wacce mijinta ya yi fushi da ita, saboda ya neme ta ba ta ba shi hadin-kai ba.

Kula da abin da mutum ya haifa wajibi ne, ciyar da su kuma sadaka ne, Wannan yasa za ki dinga yiwa mijinki nasiha cikin ladabi don ya fahimci gaskiya .

Allah ne mafi sa ni

Amsawa🏻

DR. JAMILU YUSUF ZAREWA

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/CQ9TMXMrWDx1y7sYye2znU

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments