Ticker

6/recent/ticker-posts

Me Yake Jawo Yawan Mafarkin Saduwa?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum da fatan Malan ya wuni lpy Allah yasa haka ameen. Tambaya ta anan shine: me ke jawo yawan mafarki na saduwa ko na kallo na maniyyi da sauransu akai akai? misali asati sau uku ko sau Huɗu ko sama da haka asati? yawan yin mafarkin nan jinya ce ko ba jinya ba? idan jinya ce wani magunguna ne a addinince Wanda za'ayi amfani dasu wajan samun sauki. Yawan yin bacci akai akai.Yawan yin fitsari akai akai. Meke janyosu? Nagode ya sheikh ataimaka min da amsan waɗannan tambayoyin nawa.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Shi irin wannan mafarkin wani lokacin yakan zo ne ta sanadiyyar rashin kwanciya da alwala ko kuma rashin yin azkar kafin kwanciya. Wasu lokutan kuma, abinda ka sanya azuciyarka harma kake yawan yin tunaninsa, shine kafi ganinsa a barci. Wato idan kana yawan son kallon tsiraici Ko tunanin Jima'i acikin ranka, to babu mamaki don kayi mafarkin abinda ke zuciyarka.

To awasu lokutan kuma yawan yin hakan yana da alaqah da shafar Shaiɗanun Aljanu. Wato Aljanun soyayya (JINNUL AASHIQ) masu shiga jikin Namiji ko mace ta sanadiyyar wai sonsu sukeyi.

Shi kuwa yawan jin barci ko kuma yawan yin fitsari, akwai Chutuka masu janyo irin wannan matsalolin. Misali chutar Diabetes da kuma sauran chututtukan dake da alaqah da Bladder ko Qodar Ɗan Adam. Hakanan zazzabin Malaria ma awasu lokutan yakan haifar da haka. Shi yasa nake baka shawarar kaje babban asibiti su auna jikinka sosai. In shã Allahu zasu gano chutar dake damunka.

Amma idan sun kasa ganowa, to zaka iya tuntubar wannan lambar domin samun shawarwari ko magungunan da suka dace (07064213990).

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments