Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Wanda Janaba Ya Sameshi A Lokacin Sanyi

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum warahamtullahi wabarkatuhu!! Da fatan Malam yana cikin koshin lafiya Allah yasa, Malam tambayata itace : Ni inada jin sanyi koda sanyi kaɗan akeyi to ni inaji sosai har wasu sukance wai banida lafiya to Malam nakan tashi da asuba lokacin sallah wani lokacin Sai in tashi inji nayi mafarki kuma har na fidda maniyyi to a lokacin sanyi Malam bazan iya yin wanka ba zan iya yin taimama inyi sallah Malam in yaso daga baya inyi wanka???. Wassalamu Alaikum. Malam.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.

Ya halasta ga mai janabah yayi taimama a Waɗannan yanayin

1. idan har bai samu ruwan da zai yi wanka ba,  kuma babu alamar samun ruwan har gari ya kusa wayewa.

2. Idan ya zamanto yana tsoron kamuwa da jinya, ko Qaruwar wata jinya ajikinsa idan har yayi amfani da ruwan sanyi, kuma gashi awajen da janabar ta sameshi babu ruwan dumi, kuma babu damar dafawa ko samowa ruwan dumin kafin wayewar gari.

3. Idan ya zamanto yana da wata larurar da ba zata yiwu ya taɓa ruwa ba ( koda na zafi ne).

4. Idan ya zamanto yana cikin tafiya atsakiyar daji, da ruwa awajensa amma idan har yayi wanka dashi, bazai samu wanda zaisha ba, kuma rashin ruwan shan zai iya zama barazana ga rayuwarsa.

To amma kai tunda kasan kana da wannan larurar jin sanyin, mai zai hana ka rika tanadin ruwan zafi a plask ka ajiye a ɗakinka ko water heater ko gas cooker wanda zaka rika dafa ruwan dashi?.

Domin hakika yin taimama bazai halatta gareka awannan halin ba,  mutukar dai akwai yiwuwar samun ruwan dumi a inda kake, ko dumamashi kafin fitowar rana.

WALLAHU A'ALAM.

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇 https://chat.whatsapp.com/GcU1I5wjOB18K4PA6eURQQ

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments