𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam Alaikum. Mijina yana
mu’amala da mata a waje, don in yi maganin hakan sai na yi amfani da wani layin
waya ina tura masa saƙon wa’azi
ba tare da ya san ni ce ba. Da ya fara zaton wataƙila ni ɗin
ce, sai ya ce: Idan ni nake turawa, to a bakin aurena idan ban bari ba! Ni kuma
sai da na sake turawa har sau biyu sannan na bari. Daga baya dai ya tura ni
gidanmu har sai da na yi watanni huɗu
sannan ya biyo ni da saƙon saki ta waya, alhali da ma akwai saki ɗaya. Bayan na gama idda
sai kuma ya dawo aka sake ɗaura
mana sabon aure. Malam, wai yaya matsayin wannan auren na yanzu?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul
Laah.
A kan wannan mas’alar mun amsa
Tambaya ta A188 inda muka ce:
Sakin aure na’uka ne mabambanta
in ji malamai: Akwai Saki Naajiz akwai kuma Mu’allaq. Naajiz shi ne wanda mai
yin sakin ke nufin aukuwar shi a daidai lokacin da ya faɗe shi kawai, bai rataya shi ga aukuwar wani
abu ba.
Shi kuwa Mu’allaq shi ne sakin da
ya rataya aukuwarsa ga wani sharaɗi,
kamar wanda ya ce wa matarsa: In kika fita zuwa wuri kaza, to kin saku!
Hukuncin wannan sakin a wurin
malamai ya kasu kashi biyu:
(i) Akwai Al-Mu’allaqul-Qasamiy,
wanda mai faɗinsa
yake nufin ƙarfafa maganarsa ce kawai. Watau so ya ke ya hana matar aikata
wani abu, ko kuma ya ɗora
ta kan aikata wani abu. Amma ba nufinsa aukuwar sakin ba ne! Malamai sun nuna,
a nan ba a cewa sakinsa ya auku, ko da kuwa abin da ya rataya maganar a kansa
ya auku, watau ko da matar ta aikata wannan abin da ya faɗan. Hukuncinsa kawai sai
ya yi kaffarar rantsuwa: Ciyar da miskinai guda goma, ko tufatas da su, ko kuma
’yanta baiwa. Idan kuma bai samu ikon hakan ba sai ya yi azumin kwanaki uku.
(ii) Akwai kuma
Al-Mu’allaqus-Shartiy, wanda mai faɗinsa
yake da nufin aukar da sakin tun daga zuciyarsa. Wannan kam sakinsa ya auku a
daidai lokacin da matar ta aikata abin da ya rataya sakin a kansa.
Don haka a nan ana buƙatar
sanin menene manufar mai faɗin
irin wannan sakin, kafin ya yanke hukunci a kansa.
Daga nan ya fito fili kenan cewa
(i) Idan ya tabbata daga mijin
cewa, da ma sakin ta yake nufi tun daga zuci a lokacin da ya faɗi waccan maganar, to
sakinta da ya yi na ƙarshen ya kammala saki uku kenan. Don haka ba zai yiwu su sake
yin aure da shi ba, sai daga bayan ta auri wani mijin na-daban kuma ta rabu da
shi bayan cikakkiyar saduwa ta auku a tsakaninsu, kamar yadda aya ta tabbatar.
(Surah Al-Baqarah: 230).
فَإِنْ طَلَّقَهَا فَلَا تَحِلُّ لَهُ مِنْ بَعْدُ حَتَّىٰ تَنْكِحَ زَوْجًا غَيْرَهُ ۗ فَإِنْ طَلَّقَهَا
فَلَا جُنَاحَ عَلَيْهِمَا أَنْ يَتَرَاجَعَا إِنْ ظَنَّا أَنْ يُقِيمَا حُدُودَ اللَّهِ ۗ وَتِلْكَ حُدُودُ
اللَّهِ يُبَيِّنُهَا لِقَوْمٍ يَعْلَمُونَ
Sa´annan idan ya sake ta (na
uku), to, bã ta halatta a gare shi, daga bãya, sai tã yi jima´i da wani miji
waninsa. Sa´annan idan (sãbon mijin, watau na biyu) ya sake ta, to, bãbu laifi
a kansu ga su kõma wa (auren) jũna, idan sun (mijin farko da matar) yi zaton
cewa zã su tsayar da iyãkõkin Allah, kuma waɗancan
dõkõkin Allah ne Yana bayyana su ga mutãne waɗanda
suke sani. (Surah Al-Baqarah: 230).
(ii) Idan kuwa ba sakin yake nufi
ba, kawai dai tsoratar da ita yake nufi to wannan auren da suka ƙulla
a yanzu ya yi. Kuma saura igiyarsa ƙwara ɗaya
tal. Sai su kiyaye.
Allaah ya ƙara mana shiriya.
WALLAHU A'ALAM
Sheikh Muhammad Abdullaah
Assalafiy
Ga masu tambaya sai su turo ta
WhatsApp number: 08021117734
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da
Sunnah. Ku kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/JLojawdOWYsEOeSHZMNdjf
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓��𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.