Ticker

6/recent/ticker-posts

Tarbiyyar Bahaushe a Mahangar Ruwan Bagaja

Published in HUMANITIES IN THE SUB-SAHARAN WORLD (University of Cairo/ Umaru Musa Yar’adua University, Katsina, Special Research in Humanities) RUWAN BAGAJA IN PERSPECTIƁES: (Eight Decades of a Hausa Masterpiece in Prose 1933-2013), page 393 – 410

Tarbiyyar Bahaushe a Mahangar Ruwan Bagaja

English Rendition as, “Hausa Moral Behaviour as viewed from the Eyes of Water of Cure 

Dr. Bashir Aliyu Sallau
Department of Nigerian Languages
Umaru Musa Yar’adua University, Katsina – Nigeria
sarkingaska@yahoo. com

Tsakure

Kafin shigowar Larabawa da Turawa ƙasar Hausa hanyar da Hausawa suke bi wajen koyar da tarbiyya da adana ta, ita ce ta hanyar adabinsu na baka. Shigowar Larabawa da kuma karɓar addinin Musulunci da Hausawa suka yi, ya taimaka wajen samuwar rubutu da karatu. Haka kuma, shigowar Turawa ƙasar Hausa da kafuwar mulkin mallaka a cikin ƙarni na goma sha tara ya taimaka wajen samuwar rubutun boko wanda ake yi da haruffan Romanci. Domin samar da littattafan da za su taimaka wa makarantu su sami abin karantawa, a cikin shekara ta 1933, Hukumar Talifi ta shirya gasar rubuta litattafan karatun zube. A gasar, marubuta sun rubuta littattafai masu yawa waɗanda daga ƙarshe aka zaɓi littafin ‘Ruwan Bagaja’ wanda Alhaji Abubakar Imam ya rubuta a matsayin na ɗaya. Sai kuma littafin ‘Shehu Umar’ wanda Alhaji Abubakar Tafawa Ɓalewa ya rubuta ya zama na biyu da sauransu. Maƙasudin wannan takarda shi ne, ta yi nazarin littafin ‘Ruwan Bagaja’ domin duba yadda marubucin ya kalli tarbiyyar Hausawa a cikinsa. Dalili kuwa shi ne, a wannan littafi an kalli manyan ginshiƙan tarbiyyar Hausawa waɗanda suka shafi gaskiya da riƙon amana da yin biyayya ga iyaye da shugabanni da kiyaye dokokin addini da riƙo da sana’o’i da nuna kara da yin zumunci da sauransu.

 

1.0    Gabatarwa

Bisa ga tsarin ilimi na zamani kowace al’umma tana da ire-iren hanyoyin da take bi domin adana tarihinta da al’adunta da muradunta yadda za su tafi daidai da zamani. Kafin shigowar Larabawa da Turawan mulkin mallaka ƙasar Hausa, hanyar da Hausawa suke bi wajen cim ma wannan buri ita ce, ta hanyar adabin bakan su. Idan muka waiwayi tarihi, za mu fahimci cewa, al’ummar Hausawa sun sami hanyar rubutu da karatu ne sakamakon shigowar Larabawa da Turawa ƙasar Hausa. Da farko a iya cewa, shigowar Larabawa ƙasar Hausa cikin ƙarni na goma sha huɗu, waɗanda daga cikinsu akwai Larabawa ‘yan kasuwa na Masar waɗanda su ne suka fara zuwa, sai kuma wasu Larabawa Malamai na Morocco da Bagadaza da Masar waɗanda suka kawo addinin Musulunci, ya taimaka wajen koya wa Hausawa rubutu da karatu cikin haruffan Larabci. Sannu a hankali wannan ilimi na addinin Musulunci ya ƙara samun bunƙasa da karɓuwa a wurin Hausawa. Ta dalilin haka ne, wasu daga cikin Hausawa waɗanda suka sami ƙwarewa a fannin suka ƙirƙiro rubutun Ajami. Wannan al’amari ya ƙara taimakawa matuƙa gaya wajen bunƙasar ilimin addinin Musulunci a tsakanin Hausawa. Haka kuma, ta wannan hanya ce malaman addinin Musulunci Hausawa suka riƙa rubuta waƙoƙin addini, da kuma yi wa sarakunan da manyan ‘yan kasuwar ƙasar Hausa magatakarda. Ba a nan al’amari ya tsaya ba, don kuwa waɗannan malamai sun riƙa rubuta wasiƙu tsakaninsu, waɗanda har a wannan zamani akwai ire-iren su da ake samu a gidajen ajiye kayan tarihi da kuma gidajen ire-iren waɗannan malamai da suka gabata.

Kashi na biyu da za a iya cewa, Hausawa sun koyi hanyar rubutu da karatu, a iya danganta ta shigowar Turawan mulkin mallaka ƙasar Hausa a cikin ƙarni na goma sha tara. Bayan duk wata yarjejeniya da tataɓurza da yaƙe-yaƙe da suka gudana tsananin sarakunan ƙasar Hausa da Turawan mulkin mallaka na Ingilishi. Daga ƙarshe, a cikin shekarar 1903 dukkan ƙasar Hausa ta koma ƙarƙashin mulkin Turawan Ingilishi. Bayan cim ma wannan buri na kafa mulkin mallaka a ƙasar Hausa, babban abin da ke gaban Turawan, shi ne su sami ‘yan ƙasa waɗanda za su riƙa taimaka musu wajen tafiyar da mulki a ofisoshi kamar yadda ake yi a Ingila. Waɗannan mutane ba za su samu ba, dole sai an kafa makarantun da za su horar da su. Wannan ne ya sa Gwamna Lugga, wanda shi aka ba ikon tafiyar da mulkin Arewa wadda ƙasar Hausa take ciki, ya ɗauki matakin da ya kai ga kafa makarantar Ɗan Hausa a Nasarawa Kano, amma ba ita ce makarantar boko ta farko ba a Arewa. An kafa wannan makaranta a cikin shekarar 1909 aka kuma ba wani Bature mai suna Sir Hans Ɓischer, wanda saboda yadda yake jin Hausa ake yi masa laƙabi da Ɗan Hausa.

 

2.0     Ƙoƙarin Samar da Littattafan Karatun Zube na Hausa Daga Shekarar 1929 – 1933

Bayan buɗe makarantar Ɗan Hausa a Kano, har zuwa lokacin da aka ƙara buɗe wasu makarantu a wasu garuruwa na ƙasar Hausa babu wasu tsayayyun littattafan da aka rubuta da boko don koyarwa. Mafi yawancin rubuce-rubuce da littattafan da Turawa suka rubuta cikin harshen Hausa, sun tsara su ne don koyar da Hausa ga Turawa a can ƙasashensu. A nan ƙasar Hausa kuwa, littattafan Larabci da kuma wasu rubuce-rubucen da aka yi cikin Hausa rubutun Ajami ne waɗanda mafi yawancinsu waƙoƙi ne (Yahaya, 1988:93).

Bisa tsarin koyarwa a waɗannan makarantu, Sir Hans Ɓischer, watau Ɗan Hausa tare da taimakon wasu malamai da suke koyarwa a waɗannan makarantu suka samar da littattafan da suka riƙa amfani da su wajen koyarwa. Daga cikin littattafan akwai Karatu Hausa, da Littafi Na Koyon Karatu, sai Littafin Koyon Lissafi da kuma Lararin Ƙasashen Afirka waɗanda dukkansu a Ingila aka buga su.

 

2. 1 Kafa Hukuma Fassara

Sakamakon bunƙasar ilimin zamani da kuma ƙaruwar makarantun boko a ƙasar Hausa, ya sa ma’aikatar ilimi ta fahimci akwai babban ƙalubale a gabanta na samar da littattafan Hausa da za a yi amfani da su wajen koyarwa. Wannan dalili ne ya sa Gwamnati ta kafa Hukumar Fassara (Translation Bureau) a cikin shekarar 1929. Da farko a ƙarƙashin wani Bature mai suna Mr. C. E. J. Whitting, kuma a gidan Ɗan Hausa da ke Nasarawa a Kano aka fara buɗe mata ofis. Bayan shekara biyu da kafa wannan hukuma, watau 1931, sai aka mayar da ita Zariya inda aka buɗe mata ofishinta na dindindin. Shekara ɗaya bayan dawowar wannan Hukuma Zariya, watau 1932, sai aka miƙa shugabancinta a hannun wani haziƙi, kuma mashahurin masanin Hausa, mai suna Dr. R. M. East.

Domin cim ma burin kafa wannan hukuma, an ɗora mata nauyi kamar haka:

                           i.             Fassara littattafai daga waɗansu harsuna, musamman Larabci da Turanci zuwa Hausa.

                         ii.            Wallafa littattafai cikin harshen Hausa.

                      iii.             Shirya littattafai manya da ƙanana don karantatawa a makarantu.

                       iv.             Taimaka wa ‘yan ƙasa su dinga wallafa littattafai (Yahaya, 1988:93-94).

A karon farko a iya cewa, kafa wannan Hukuma ya taimaka wajen samar da littattafan da aka fassara musamman daga Larabaci zuwa Hausa. Haka kuma, da wasu daga Turanci zuwa Hausa kimamin goma sha huɗu, waɗanda suka haɗa da:

a)             Dare Dubu da Ɗaya – Larabci zuwa Hausa

b)             Labarun Hausawa da Maƙwabtansu – Larabci zuwa Hausa

c)              Labaru na Da Da na Yanzu – Larabci zuwa Hausa

d)            Littafi na Bakwai na Leo Africanus – Turanci zuwa Hausa

e)             Siɗ Hausa Plays – Turanci zuwa Hausa

 

2. 2. Kafa Hukumar Talifi

Hans Ɓischer (Ɗan Hausa), ya gabatar da wani shiri a cikin shekarar 1933, don gudanar da gasar rubuta ƙagaggun labarai na rubutun zube. Domin cim ma wannan buri, sai aka sauya sunan Hukumar Fassara zuwa Hukumar Talifi, don ta gudanar da wannan gagarumin aiki. Dalilin sauya wannan suna shi ne, a ƙara faɗaɗa aikin wannan hukuma daga fassara ayyuka daga wasu harsuna zuwa harshen Hausa.

Domin gudanar da wannan aiki. An bai wa Hukumar Talifi ƙarƙashin shugabanci Dr. R. M. East nauyin gudanar da gasa. Daga nan ne, sai shi Dr. East da kansa ya zagaya manyan garuruwan ƙasar Hausa don tallata wannan gasa, inda ya sadu da malamai masu gaurayen ilimin zamani da na Arabiya ya yi musu bayani kan ire-iren littattafan da ake so su rubuta. Ya kuma ƙara bayyana musu cewa, dukkan wanda ya ƙago wani labari a rubuce, za a karɓa a shirya shi a buga shi, domin a sami abin karantawa, kuma za a ba shi na goro. Wannan talla ta jawo hankalin marubuta da yawa. Sakamakon ta aka sami rubuta littattafai masu yawa da suka shiga cikin gasar. Daga ƙarshe, bayan an tace waɗannan littattafai, an zaɓi biyar da suka yi nasara:

                           i.             Ruwan Bagaja M. Abubakar Imam

                         ii.            Ganɗoki Malam Bello Kagara

                      iii.             Shaihu Umar M. Abubakar Tafawa Ɓalewa

                       iv.             Idon Matambayi Malam Muhammadu Gwarzo

                         v.            Jiki Magayi Malam John Tafida da Dr. R. M. East

Daga cikin waɗannan littattafai, littafin Ruwan Bagaja na M. Abubakar Imam shi ya fi ɗaukar hankalin masu gudanar da gasar da kuma karɓuwa ga masu karatu. (Yahaya, 1988:95).

Haka kuma, wannan dalili ne ya ɗauki hankalin mu, inda muka ga ya dace, domin murnar cika shekara tamanin (80 watau 1933 – 2013) da yin wannan gasa,  a yi wani aiki kan wannan littafi don fito da waɗannan manyan jigajigan fannonin nazarin Hausa. A fito da su fili kamar yadda wannan mawallafi ya shirya su cikin wannan littafiba tare da tunanin sa na cewa, wata rana wasu manazarta za su yi nazarin wannan littafi ba, wani ba zai ce dukkan abubuwan da ya shirya a cikin littafin ya yi su ne da irin wannan tunani.

 

3. 0 Yadda aka Fito da Tarbiyyar Hausawa Cikin Littafin Ruwan Bagaja

Domin cim ma burin da aka yi bayani a baya,  a matsayina na ɗalibin al’adun Hausawa na ga ya dace in dubi tarbiyyar Hausawa a mahangar littafin. Tarbiyya kuwa, ta shafi kiyaye dokokin addini, da biyayya ga shugabanci, da gaskiya da riƙon amana, da sadar da zumunci da taimakon juna, da riƙo da sana’a, da kara da alkunya da nuna jarunta da juriya. Wannan kuwa ya faru ne saboda mawallafin wannan littafi Alhaji Abubakar Imam cikakken Bahaushe ne wanda ya yi ƙuruciya, ya girma har Allah Ya amshi rayuwarsa a ƙasar Hausa. Haka kuma, ya sami koyarwa da tarbiyyar Hausawa wadda addinin Musulunci da zamananci suka yi naso cikinta.

 

3. 1 Kiyaye Dokokin Addini

Tsarin tarbiyyar Bahaushe ya fara tun daga irin yadda yake kiyaye dokokin abin da yake bauta wa. Addinin farko na mutanen ƙasar Hausa shi ne addinin gargajiya, watau bauta wa Iskoki ko mutanen ɓoye. Sakamakon daɗewa ana yin wannan bauta ya sa ko da al’ummar Hausawa suka karɓi addinin Musulunci, addininsu na gargajiya ya yi naso cikin addinin Musulunci. A iya gani haka a dukkan rayuwar Bahaushe. Saboda tarbiyyar kiyaye dokokin addini da Hausawa suke da shi ya sa, idan mutum ya fuskanci wata matsala yake zuwa wurin malamai don a taimaka masa. Irin wannan taimako ya haɗa da addu’a da duba wadda ta samo asali daga addinin gargajiya na Hausawa da sauran hanyoyi.

Ta wannan fuska, marubucin littafin Ruwan Bagaja ya fito da irin yadda al’ummar Hausawa suka kiyaye dokokin addini. Misali, a shafi na 4, za a ga inda saboda kiyaye dokokin addini, ya sa da Saƙimu ya yi mafarkin wani abu ya fito daga zakarin mijin mahaifiyarsa da ya kashe ya sa shi neman malaman duba don su yi masa duba su gano masa ma’anar wannan mafarki da ya yi, kamar haka:

“Ana nan, bayan ‘yan kwanaki da rasuwar malamin, sai Saƙimu ya yi mafarki, ya ga malamin a tsaye. Sai ga wani ɗan abu, kamar ɗan dabino, ya fito daga zakarin malamin. Sai ya ga abin nan yana ta girma har ya kai kamar zaki. Da ya kai haka, sai abin ya faɗa masa ya kashe shi. Wannan mafarki fa ya dugunzumad da ransa. Da gari ya waye, sai ya tara malamai don su masa duba”.

Haka kuma, daga shafi na 4 – 5, saboda yarda da ire-iren ayyukan malaman duba ya sa Saƙimu ya riƙa ba matan wannan malami da ya ya kashe guba wadda ta yi sanadiyyar mutuwarsu. Malaman nan sun gaya masa cewa, daga cikinsu akwai wadda za ta haifi ɗan da zai kashe shi.

“Dukan malamai, kowa ya duƙufa ya zana ya shafe, ya zana ya shafe. Daga nan sai babbansu ya ce, “Za a haifi wani yaro a gidan nan, cikin matan tsohon nan da ya rasu shi ne zai kashe ka”.

Duk da kasancewar da farko Saƙimu bai amince da sakamakon da waɗannan malamai suka ba shi ba. Ya kore su, amma daga baya saboda nason da addinin gargajiya ya yi a wurinsa wanda ya haifar da kiyaye dokokin addini a wurinsa, ya sa shi sauya tunaninsa a cikin shafi na 4 – 5 kamar haka:

“Da tsakad dare, Saƙimu ya tashi ya ƙulla wannan ya ƙwance, yana ta juyayi cikin zuciyarsa, yana cewa, “Allah abin tsoro, malami abin tsoro! Abin da ya fi kyau sai in halaka matan nan huɗu duka masu takaba, don kada maganar masu dogwayen geman nan ta zama gaskiya. ”

Haka kuma, a shafi na 6, an bayyana irin yadda wasu daga cikin al’ummar Hausawa suke kaɗaicewa don kiyaye dokokin addini da yin bautar Allah, Maigirma da ɗaukaka. A wannan shafi an bayyana cewa, Alhaji Imam ya tarar da wani tsoho wanda ya bayyana masa cewa:

“Ni mutum ne ɗan’uwanka, shekarata saba’in a nan ina ibada ban taɓa ganin wani mahaluƙi ba sai fa kai. ”

A cikin wannan littafi na Ruwan Bagaja, an ƙara bayyana irin yadda al’ummar Hausawa suke kiyaye dokokin addini. A iya ganin haka a shafi na 8 inda Alhaji Imam ya isa wani gari na jahilai mai suna Saburi, da kuma irin karɓar da aka yi masa ta matsayin babban malami, kamar haka:

“Da zuwana na sami wata doguwar tasbaha, na nufi wajen Sarki, na ce ni malami ne.

Ya ce, “Daga ina?”

Na ce, “Daga ƙasashen Larabawa. ”

Da Sarki ya ji haka, ya yi murna da zuwana, ya ce, “To ina za ka?”

Na ce, “Nan na zo in riƙa yi muku salla don za a su ku aljanna ku duka domin adalcinka, ya Sarki. ”

A shafi na 17 ma an ƙara bayyana irin yadda Bahaushe yake kiyaye dokokin addini, inda aka bayyana cewa:

“Bayan an yi asalatu, sai na tashi na fito waje, na yi alwalla, na tafi masallaci na bi Liman don neman falalar jam’i. Da aka ƙare, na yi ‘yan wurudda na gama, na komo gida. ”

Wannan al’amari na kiyaye dokokin addini kamar yadda aka fito da su a cikin littafin. Ba su tsaya a nan ba, don kuwa a shafi na 23 – 24, an ƙara bayyana irin yadda Bahaushe yake kiyaye dokokin addininsa, kamar haka:

“Tun da tsakad dare, na tashi ina bin gari ina wa’azi har safe, kowa garin ya ji na kwana hadisi. ”

Haka al’amarin ya ci gaba, inda a shafi na 28, aka ƙara bayyana wannan batu da muke bayani a kan sa, inda aka bayyana cewa:

“Ina cikin tafiya, har na kai wani gari wai shi Miska, na sauka gidan wani malami wanda ake ce masa Daula. Don ibadarsa har mutane su kan yi masa kirari, suna cewa, “Na-Malam Iro masu kwana salla!”

Saboda kiyaye dokokin addini ya sa al’ummar Hausawa suke girmama malamai kuma suna ba su ƙima sosai. A cikin wannan littafi an fito da irin wannan ƙima da Hausawa suke ba malamai a shafi na 30 – 31. A waɗannan shafuka, an bayyana irin martaba, da ɗaukaka, da girmamawar da aka yi wa Alhaji Imam saboda ɗaukarsa da aka a matsayin babban malami. Misali, a shafi na 31 buwaya wadda mutanen wannan gari suka ɗauka karama ce ta waliyyai da ya nuna musu lokacin da ɗiyar Sarki ta rasu, ya isa a ƙara fahimtar irin girmamawar da Hausawa suke ba malamansu na addini. Ga kaɗan daga cikin ire-iren abubuwan da suka sa mutanen Nasarawa ba Alhaji Imam girma:

“Sai na wuce su, na yi ta yi, har na tarad da wani tabki, na tsaya na yi wanka, raina ya komo. Sa’an nan na isa garin, na tambayi gidan aka nuna mini na shiga masallacin ƙofar gidan, ina jan tasbaha. Jimawa kaɗan sai suka iso. Da na ji sun iso sai natashi na fita daga masallacin da tasbaha a hannuna, na ce, “Sannunku da zuwa!”

Waziri da mutanensa, kowa ya rasa abin da zai ce. Duk sai na ga sun faɗi a gabana sun yi mini sujada.

Na ce, “Kash! Subhana lillahi! Ai sai Ubangiji a ke wa haka. ”

Saboda kiyaye dokokin addini ya sa idan Bahaushe ya aikata laifi yake neman gafara daga wurin Allah, Maigirma da ɗaukaka, don ya yafe masa. Wannan dalili ne ya sa marubucin ya fito da irin wannan tarbiyya ta Bahaushe a cikin wannan littafi. Ya bayyana cewa, kasancewar Alhaji Imam da Malam Zurƙe sun daɗe suna ɓarna da tu’annati da saɓa wa Allah. Domin kiyaye dokokin addini ya sa, a lokacin da suka isa birnin Baitul Muƙaddas, sai Malam Zurƙe ya shawarci Alhaji Imam da su tuba. Ga bayanin abin da suka tattauna;

“A wannan gari mai albarka Malam Zurƙe ya ce mu tuba da irin ayyukammu na saɓo hakanan. Na yarda da magana tasa, muka tara malamai aka yi mana addu’a don kada Shaiɗan ya sake wasa da zukatammu. ”

Yana daga cikin tarbiyyar Bahaushe, idan yana neman biyan wata buƙata, ko idan ya shiga cikin tsanani ya roƙi Allah don Ya biya masa bukatunsa. A cikin Ruwan Bagaja, an fito da irin wannan tarbiyya a shafi na 38 – 39, kamar haka:

“Da ka shiga garin ka yi ta rera wannan waƙa: ‘Wa yaf’alu fi hukmihi ma yasha’u. Ta’alal ilahu wa jallal hikam, ’ har ka ɗebo ruwan ka fito. ”

 

3. 2 Biyayya ga Shugabanci

Tun kafin shigowar addinin Musulunci ƙasar Hausa, Hausawa suna da kyakkyawan tsari na shugabanci, inda na ƙasa yake yin biyayya ga na gaba da shi. Haka kuma, talakawa suna yin biyayya ga sarakunansu. Idan muka duba cikin Ruwan Bagaja, za a ga wurare masu tarin yawa inda aka yi bayani a kan irin yadda yake ba nuna cikakkiyar biyayya ga shugabanci.  A farkon wannan littafi marubucin ya buɗe shi da irin tsarin Bahaushe na yin biyayya ga shugabanni. Dalili kuwa shi ne, a tsarin tarbiyyar Bahaushe, idan baƙo ya sauka a wani gari wanda ba a san shi ba, sai ya je gidan sarki, ko hakimi, ko dagaci, ko mai’unguwar garin ko ƙauyen don a saukar da shi. A wancan zamani da ake bin irin wannan tarbiyya an sami zama lafiya da kwanciyar hankali. A iya ganin haka, a shafi na 1 inda aka bayyana cewa:

“Yana cikin bin ƙasashe, har ran nan Allah Ya sa ya isa wani gari wai shi Kwantagora, wani babban birni a cikin ƙasar Sudan. Ya isa wajen Sarkin garin, aka kai shi masauki”.

Irin wannan tsari na biyayya ga shugabanci, wanda yake bayyana idan baƙo ya sauka a wani gari da ba a san shi ba, ya fito a wurare da dama.

A dai wannan shafi an ƙara bayyana irin yadda na ƙasa yake yin cikakkiyar biyayya ga shugabansa, inda zai zauna tsawon lokaci yana jiran shugabansa.

“Koje Sarkin Labari ya ce musu, “Yana fitowa yanzu?” Suka ce, “Wa zai fito da shi yanzu tun azahar ba ta yi?” Koje ya share wuri, ya zauna kan azahar ta yi”.

Idan muka nazarci wannan jawabi da ya gabata, a iya fahimtar cewa, barorin Alhaji Imam da shi Koje Sarkin Labari, saboda tarbiyyar biyayya ga shugabanci, sun zauna a ƙofar gidan Alhaji Imam, har sai da azahar ta yi lokacin da zai fito.

Bisa tarbiyya al’ummar Hausawa mutane ne masu matuƙar biyayya ga shugabanninsu, suna bin umurninsu ta yadda duk irin aikin da suka sa su za su aikata ko da kuwa irin wanda za a ci mutuncin wani ne. A shafi na 9, saboda irin wannan tarbiyya ce, ya sa Alhaji Imam ya sa yara suka yi wa Malam Zurƙe ature suka kore shi daga wannan gari. Ga yadda al’amarin ya faru.

“Na dubi Malam Zurƙe, na ce wa yara, “Ku yi masa eho da ature. ” Suka bi shi Eho! Eho! Eho! Daga nan ko ta kan littattafansa bai biya ba, ya yi wajen gari, yara na jifa. Ya tsere da kyar. ”

 

3. 3 Gaskiya da Riƙon Amana

Hakika, dukkan al’ummar da take da gaskiya da riƙon amana za ta zauna lafiya. Wannan dalili ne ya sa a wancan zamani, saboda gaskiya da riƙon amanar Hausawa suka zauna lafiya. Wannan kuwa ya faru ne, saboda kowa ya tsare gaskiyarsa. Haka kuma, idan ka kawo ajiya ka ba mutum, ko shekara nawa ka ɗauka, a ranar da ka bukaci kayanka, za ka tarar da su kamar yadda ka ba da ba tare da wani abu ya ɓata ba. Domin bayyana muhimmancin gaskiya da riƙon amana, marubucin littafin Ruwan Bagaja, ya nuna inda Alhaji Imam ya yi ta gamuwa da matsaloli iri daban-daban saboda rashin gaskiyarsa da ƙin riƙe amanar da aka ba shi. Misali, a iya ganin haka a shafi na 7, inda ya bayyana wa wani attajiri cewa, shi babban farke ne kamar haka:

“Idan shanuna sun zo ba ni sayar wa sai shi kaɗai, ya kama ko wane sa ya karya yadda yake so, don ni ke da abina. ”

Saboda ire-iren waɗannan romon baka da ya riƙa yi wa wannan attajiri ne, da kuma irin yadda ya ba shi gaskiya, ya sa Alhaji Imam ya damfari wannan attajiri, har ya ranci kuɗinsa jaka ɗaya da nufin idan shanunsa sun zo zai sayar masa da araha. Daga ƙarshe, saboda ba shi da gaskiya, ya gudu ya bar garin.

Haka kuma, a shafi na 11 – 12, na wannan littafi an bayyana muhimmanci riƙon amana da kuma irin abin da kan sami wanda ya ci amana. A wannan shafi, an bayyana inda Alhaji Imam ya haɗu da wani baƙauye kamar haka:

 “. . . . . . . . . . . . Ina cikin tafiya cikin daji, sai na gamu da wani baƙauye, da jaka ɗaya da sule ɗaya da kwabo biyar. Na yi tambayarsa, duk ya gaya mini labarin yadda ya sami kuɗin, da yadda ya kashe sule ɗaya da kwabo biyar ɗin. Da zai tsaya ratsi, sai ya ba ni in riƙe masa, wai shi da abokin tafiya.

Ko da ya fito, ya ce, “Ba ni mu tafi. ”

Sai ni kuwa ba kunya ba tsoro na ce, “Im ba ka me? Ni da kuɗina. ”

Idan muka nazarci wannan bayani dangane da irin hirar da ta shiga tsakani wannan baƙauye da Alhaji Imam, za a fahimci cewa, wannan baƙauye, saboda irin tarbiyyar da ya tashi da ita ta gaskiya da riƙon amana ne ya sa ya ba Alhaji Imam ajiyar waɗannan kuɗi nasa. Dalili kuwa shi ne, a cikin zuciyarsa ba ya tsammanin fuskantar wata matsala idan zai amshi ajiyarsa. A maimakon haka, sai Alhaji Imam, ya bure idonsa da toka, ya bayyana wa wannan baƙauye cewa, sam shi bai ba shi ajiyar wasu kuɗi ba. Wannan kuɗi na hannunsa da ma nasa ne. A nan ne marubucin wannan littafi ya bayyana mana cewa, tarbiyyar Hausawa ta gaskiya da riƙon amana ta fara lalacewa, wanda al’amarin har ya fara shafar yadda ake gudanar da sha’anin shari’a a ƙasar Hausa. Ya ƙara da bayyana cewa, duk irin gaskiyar ka, matuƙar ba ka ba Alƙali wani abu ba, idan mara gaskiya ya ba da wani abu, sai Alƙalin ya juye gaskiyar daga mai gaskiya ya ba marar gaskiya. Ga yadda riwayar take:

“Wasa wasa dai har abin ya yi girma, ya kai mu muka runtuma gidan Alƙali. Da ma na ji Alƙalin mai bakin cin rashawa ne. Da muka je ya tambaye ni, na mai da jawabi kamar gaske. Ya tambayi baƙaushe, mamaki ma ya hana shi ya faɗi wani abin kamawa”.

“Alƙali ya ce masa, “Kana da shaidu?”

Ya ce, “A’a, sai Allah da Ma’aiki. ”

Sa’an nan Alƙali ya juyo ya ce mini, “Kai kana da shaidu, samari?”

Na ce, “I, Allah ya gafarta malam, ina da su da yawa. ”

Ya ce, “Su wa da wa gare ka?”

Na ce, “Malam Ɗalhatu da ɗan’uwansa suna sun shaida, Malam Sule da ɗan ƙanensa Malam Hashimu sun shaida. Bari ta su ma, har autansu Malam Muhtari yana nan aka yi. Waɗansu mutane ma kamar ɗari masu zuwa da tsakad dare duk za su shaida!”

“Ko da malam ya ji haka sai ya fahimta da magana ta. Malam Ɗalhatu da ɗan’uwansa dala biyu ke nan. Malam Sule da Malam Hashimu kuwa sule da sisi ke nan. Malam Muhtari kuwa taro ke nan, mutane ɗari masu zuwa da tsakad dare kuwa sule ɗari ke nan. ”

“Watau da tsakad dare zan kawo masa sule ɗari da shida ba taro idan ya ba ni gaskiya. To, yanzu zamani ne dai na wanda ba mai gaskiya sai mai sule. Nan da nan mai bakin cin rashawa ya birkita maganar, ya ba ni gaskiya. Aka ɗaure baƙauye wata uku don ya sa mini sata. Da dare na kawo wa Alƙali waɗannan, na koma na shiga shagali da sauran”.

Allah ba azzalumin kowa ba ne. Bari mu ga irin sakamakon da wannan baƙauye zai samu dangane da cin amanarsa da Alhaji Imam ya yi kamar haka a shafi na 12.

“Ran nan na fita waje, garin shan iska, sai na tsinto wani murjani. Ashe na ‘yar Sarki ne aka sace ya faɗi. Na kawo kasuwa sayarwa. ko da aka gan ni da shi sai aka kama ni, aka kai ni gidan Alƙali. Na yi juyin duniyan nan, aka ce ni na sace shi. Aka yi mini bulala ashirin, aka kai ni gidan yari wata uku. Na tarad da baƙauyen can da na yi wa rikicin kuɗi na sa aka ɗaure shi shekaran jiya. Ko da muka yi arba ya ce, “Allah Sarki!Alhaki rima. ”

 

3. 4 Sadar da Zumunci

Bahaushen mutum kafin zuwan wannan zamani a duk inda ya sami kansa mutum ne mai ƙoƙarin sadar da zumunci. Wannan kuwa ya faru ne sakamakon irin tarbiyyar da ya tashi da ita wadda ta koya masa ziyartar ‘yan’uwa da abokan arziki. A nan ma marubucin ya yi ƙoƙarin fito da wannan ginshiƙi na tarbiyyar Hausa. Misali, a shafi na 37 – 38 na wannan littafi, an fito da muhimmancin sadar da zumunci wanda yana daga cikin abubuwan da suka ƙara taimaka wa Alhaji Imam samun Ruwan Bagaja. A nan an bayyana cewa:

“Da farko ma in faranta maka zuciya. Wan Liman ɗin nan da ka tarad da shi a kogon yana ibada, abokina ne.

Abin da ya gama mu kuwa, wata rana ne uwata ta tafi yawo har can ƙasar Sudan tana goyona. Ƙishirwa ta kama ni har fara kuka. Sai uwata ta tarad da uwar su uban nan naka, Liman, tana ɗibar ruwa. Watau uwar tsohon nan na dutse da ka gani. Da uwarsu ta ji ina kuka sai ta ce wa uwata, “Tsaya mana, ki ba yaro ɗan ruwa ya sha. ” Ta tsaya, uwarsu ta ɗauke, ta ba ni ruwa da kanta.

“Da uwata za ta tashi, sai uwar su liman ɗin nan ta kawo hure, da goro, da hannun ruwa, ta ba ta. Ta kawo kwabo biyu ta ba ni, na riƙe kwabo a kowane hannu ina wasa. Tana tsammani uwata mutum ce. Ba ta san aljana ba ce.

Da uwata za ta wuce, ta tambaye ta gidansu, ta nuna mata. Bayan kwana uku sai uwata ta zo mata da dare, ta bayyana mata ko ita wace ce, suka yi abuta. Uwar Liman kuwa tana goyon tsohon nan da ka gani a kogon dutse.

Iyayenmu suka gama mu abota da muka girma har yanzu kuwa muna biya juna. Kowane daren Jumma‘a ni kan tafi wurinsa mu raba dare muna hira. Yau shekarunmu tamanin tamanin ke nan muna ibada cikin kogo da ni da shi”.

 

3. 5 Taimakon Juna

A tsarin tarbiyyar Hausawa, taimakon juna yana daga cikin abubuwan da ke ƙara taimaka wa al’umma ta sami ci gaba da bunƙasa. cikin wannan littafi na Ruwan Bagaja, an yi bayani kan muhimmanci aikin taimakon juna. Dalilin irin wannan aiki ne ya ƙara wa Alhaji Imam ɗaukaka a lokacin da yake riƙe da sarautar Wawan Sarki. Ga yadda wannan al’amari yake:

“Ana nan ana haka, ran nan sai babban ɗan Sarki ya tara mu, watau manyan fadawa, ya ce yana gayyatarmu mu je mu yashe wa iyalansa masai, don watau bai yarda da kowa ya shiga gidansa ba sai mu yardaddun ubansa. Saboda haka muka ɗunguma, muka je gidan, muka fara aiki. Kowa yana yi yana zubad da yawu, don wari. Ni kuwa ina ta waƙa. Cikin waƙan nan tawa na ke zubad da yawu, ba wanda ya gane abin da nake yi!

Da fa ɗan Sarkin nan ya ga fadawa na zubad da yawu haka, sai zuciyarsa ta ɓaci. Ya ce musu, “In kashin ya faye wari, ku bar shi mana ku huta. Wace irin shegantaka ce haka a sa ku aiki kuna zubad da yawu? Da abinci ne Sarki ya kawo muku da yanzu kuna nan kuna hannu baka hannu ƙwarya!

Da fa ɗan Sarkin nan ya tunzura haka, sai ya tafi ya gaya wa ubansa abin da fadawa suka yi masa. Ya ce ni kaɗai ne ban zubad da yawu ba, sai waƙa na yi ta yi. Da Sarki ya ji haka, sai ya fusata. Ya sa aka kirawo su duka, ya bi su da ɗai ɗai ya sulluɓe uwa uba. Na ƙwace su da ƙyar. Wannan abin da na yi fa ya ƙara mini girma ga Sarki da ‘ya’yansa. ”

 

3. 6 Riƙo da Sana’a

Bahaushe mutum ne wanda yake ba sana’ar da ya gada matuƙar muhimmanci. Wannan dalili ne ya sa a wancan zamani ya zauna lafiya. Saboda muhimmanci sana’a ne ya sa Bahaushe yake da karin magana da salon magana waɗanda suke nuna matsayin sana’a a wurin kowace al’umma kamar haka:

                           i.            Sana’a sa’a rashin sana’a sata

                        ii.             Sana’a maganin zaman banza

                      iii.            Sana’a goma maganin mai gasa

   da sauransu.

Bisa la’akari da irin wannan tarbiyya ta riƙo da sana’a ne a wurin Hausawa, ya sa marubucin wannan littafi ya hango muhimmancinsu har ya fito da su cikin wannan littafi a shafi na 15 kamar haka:

“Duk ‘yan abin hannuna suka ƙare, na rasa abin da zan yi in sami abinci ma. Da dai na ga abin ya kawo ga haka, sai na fara zuwa su, don tun ina yaro na iya. ”

Haka al’amarin yake, don kuwa a lokacin da Alhaji Imam ya kai wani gari mai suna Miska, da ɓarayi suka matsa masa don ya sami sauƙin su, sai ya bar masaukinsa na farko ya koma gidan Sarkin Gardin Kuraye. Ga irin yadda al’amarin ya kasance a shafi na 28 – 29, kamar haka:

“Da dai na ga ɓarayi sun dame ni da shigowa, sai na bar unguwar. Na koma gidan wani Sarkin Gardin Kuraye na sauka. Ina da babban dalilin da ya sa na sauka gidan Sarkin Gardin nan.

Da dai na ji Sarkin Gardin nan ya ce a ba ni ɗaki in sa kayana, sai na ce masa, “A’a, ni na fi so in riƙa kwana da kai, in dai kurayenka suna da takunkumi. ”

Ya ce, “Af! Ai ni ma nan tare da su mu ke kwana. Me ya sa ka ke son kwana da kuraye?”

Na ce, “Ai tun garinmu na ke sha’awar kwana da su. Ai ni ma ko gida, gidan Sarkin Gardi na ke barance, shi ya sa na sauka wurinka. ”

Ya ce, “Madalla. Ashe na gida ne. ”

Bisa la’akari da tarbiyyar Hausawa, an fahimci cewa, kiwo yana da babban matsayi. Wannan dalili ne ya sa a kowane gida za ka tarar suna kiwon dabbobi ko tsuntsaye na gida, ko a je daji a kamo domin sayarwa a sami abin biyan bukatun rayuwa na yau da kullum. Wannan al’amari ya fito sosai a cikin littafin Ruwan Bagaja, wanda ya ƙara bayyana mana cewa, wannan littafi yana ƙunshe da tarbiyyar Hausawa wadda ta shafi riƙo da sana’a. A iya ganin haka a shafi 32, kamar haka:

“Da na tashi daga nan ban zame ba sai wani ƙauye ana ce masa Sarai. Na tarad da mutanen ba su da wata tabi’a sai tarkon aku. In sun kama, sai su yi ta koya masa magana, su yi ta bin gari suna sayarwa. ”

 

3. 7 Juriya da Jarunta

A tsarin tarbiyyar Bahaushe yana koya wa ‘ya’yansa juriya da jarunta yadda a lokacin da ya girma zai iya kare mutuncinsa da na al’ummarsa da ma na ƙasarsu gaba ɗaya. Idan muka nazarci wannan littafi na Ruwan Bagaja, za mu ga wuraren da marubucin wannan littafi ya fito da irin wannan tarbiyya ta juriya. Misali, a shafi 36, kamar haka:

“Na ƙwaƙwata rairayi, na shiga. Na yi na yi im mutu, Allah bai nufa. Na nemi wani abu da zan kashe kaina da shi, na rasa. Ina nan cikin ramin nan ina jiran mutuwa, . . . ”

Idan kuma muka juya wajen jarunta, a nan ma za mu ga mawallafin wannan littafi ya fito da ita a wurare daban – daban cikin wannan littafi. Misali, a shafi na 6 cikin wannan littafi, an bayyana irin jaruntar da Alhaji Imam ya nuna lokacin da ya zo wurin wani dutse cikin ƙungurmin daji, bayan ya yi tafiyar kwana saba’in cikin a kan hanyarsa zuwa Tambutu. Ga irin jaruntar da Alhaji Imam ya yi, kamar haka:

“Na tasam ma dutse haiƙan, ko da na isa gindin dutse, sai na ga wani babban kogo, na yi tsammani ba a rasa ruwa cikinsa. Saboda haka, na kutsa kaina ciki, na shiga. Can na yi zurfi da tafiya, sai na ji an ce, “Kai! Mutum ko aljan?” Da jin hakanan, sai na kaɗu, hantata ta ɗauki rawa.

Na yi ta maza dai na ce, “Mutum ne. ” Daga nan fa sai na ga wani tsoho ya taso mini tukuf da shi, yana da tasbaha a hannunsa. Ya tambaye ni labarina, na kwashe masa duk, tun daga farko har ƙarshe. ”

Haka kuma, a shafi na 36 na wannan littafi Alhaji Imam ya ƙara nuna jarunta a lokacin da yake cikin rairayi lokacin da wasu aljannu suka ɗauko wani ɗan Adam, kamar haka:

“. . . sai na ga waɗansu aljannu guda biyu sun ɗauko wani ɗan Adam. Suka suka sauke shi nan kusa da ni kaɗan, suka tona rairayi kamar shan ɗaki. Sai na ji babban ya ce, ”Bi hurmati Sulaimanu Ibnu Dawuda, iftah!” Sai na ga ƙasa ta buɗe, suka shiga da mutumin. . . . . . . . . . Can sai na ga sun fito, sun ce ”Bi hurmati Sulaimanu Ibnu Dawuda, igliƙSai na ga ƙasa ta rufe.

Wucewarsu ke da wuya sai na fito, na tafi wurin, na share rairayin da suka mayar, na ce, ”Bi hurmati Sulaimanu Ibnu Dawuda, iftah!” Sai na ga ƙofa ta buɗe, na kutsa kai na shiga. Ko da mutumin nan da aka rufe ua gan ni, sai ya taso ya faɗi gabana, ya ce, “Don Allah ka yi mini rai!” Na tambaye shi sunansa da kuma inda ya fito, duk ya kwashe ya gaya mini. Sai na ji ashe dai wannan nan nawa ne Saƙimu, agolan ubammu, wanda ya kashe shi, ya sa kuma a kashe iyayemmu mata don mafarkin can da na gaya muku ya yi na ɗan dabino. ”

“Ko da na gane haka, sai maganar fassarar mafarkin malaman nan ta faɗo mini. Na duba gaba gare mu kaɗan sai na ga wani takobi mai kuben zinari. Na ɗauka na zare shi, sai na ga an rubuta kalmar shahada a gefensa. Na dubi mutumin nan na gaya masa ni ko wane ne. Na ce masa ya tuna da fassarar mafarkin da ka yi masa? Na kuma gaya masa yadda aka yi har aka haife ni, da yadda na tashi duka. Ko da ya ji haka sai ya zaburo mini. Na sa takobin nan na ɗauke kansa. Na ce, “Kafin a zo a kashe ni na rama wa baba. ”

 

 

3. 8 Kara da Alkunya

Bisa al’ada da kuma tarbiyya an fahimci cewa, Bahaushe mutum ne mai nuna matuƙar kara da alkunya a dukkan al’amarin rayuwa, domin kuwa yana yin dukkan biyayya ga abokin mahaifinsa, ko abokin wansa, da dukkan wanda ya girme shi. Shi kuma babba yana iya riƙƙannensa da ‘ya’yansu da ‘ya’yan dangi na kusa da na nesa, da ma waɗanda ba a gama kome da su ba. Idan kuma wata hidima ta shafe shi ko wani na kusa da shi, ko kuwa don neman suna, yana iya shiga bikin da bai shafe shi ba ya yi ruwa ya yi tsaki don a san da shi. Haka kuma, saboda kunya, za a tarar a wasu lokuta wasu abubuwa waɗanda ka iya cuta masa, amma sai ya kauda kai daga gare su. Marubucin littafin Ruwan Bagaja, ya yi ƙoƙarin fito da wannan ginshiƙi na tarbiyyar Hausawa a cikin wannan littafi. Misali, a shafi na 3, saboda kara ta sa Malam Na-Bakin-Kogi mahaifin Alhaji Imam, ya riƙe Saƙimu wanda agola ne a wurinsa, kamar haka:

“Amma ko da shi ke malamin nan ba shi da ɗa na cikinsa, yana da wani agola, shaiɗani, ana kiransa Saƙimu, kome uban nan nawa ya yi masa uwar ba ta godewa, shi yaron ba shi godewa. ”

Saboda muhimmanci kara ga Bahaushe ne ya sa ƙarami yake ɗauke wa manya bugu, ko kuwa ya yi musu aikin da ba sa iya yi, ko da suna iya yi saboda alkunya sai ya karɓa ya yi musu. Idan kuma na fita kunya ne, sai ya sayar da ƙarfinsa don ya fitar da su kunya. An fito da irin wannan tarbiyya ta Hausawa cikin wannan littafi a shafi na 6, inda saboda tozartawar da Sarki ya yi wa Liman wanda shi yake auren mahaifiyar Alhaji Imam kuma ya ɗauke shi kamar ɗan da ya haifa da cikinsa, ya sa Alhaji Imam ya sayar da ransa, ya kuma ɗauki niyyar sai ya samo Ruwan Bagaja don ya fitar da Liman daga wannan kunya da ya ji kamar haka:

“Ko da na ji baba ya ce haka, sai raina ya ɓaci, hankalina ya tashi. Da komawata gida, sai na ɗauki ‘ya sandata, shiga gida, nanemi gafara ga iyayena, na ce za ni yawon duniya. ”

Don ƙara ƙarfafa wannan niyya tasa ta yi wa Liman kara, duk da kasancewar an bayyana wa Alhaji Imam irin matsaloli da wuyar da zai fuskanta wajen neman Ruwan Bagaja wanda ba hannun mutane yake ba, a hannun aljunnu yake, bai nuna kasala ba. Daga ƙarshe ma a shafi na 6 – 7, ya bayyana cewa, sai dai ya mutu wajen neman Ruwan Bagaja, kamar haka:

“Da ya gama labarinsa na ce, “To, tun da dai akwai shi a duniya, sai im mutu gun nemansa. Don Liman ba shi ya haife ni ba, ba ni bari a kunyatad da shi. ”

Haka kuma, a shafi na 10 cikin wannan littafi, irin wannan al’amari ya faru inda aka bayyana cewa, saboda irin yadda Alhaji Imam ya shiga cikin hidimar bikin ɗan Sarkin Yamel ya sa ya sami ɗaukaka sosai a wannan gari, ya kuma ƙulla abota da ɗan Sarki wanda aka yi wa biki, kamar haka:

“Bayan na ƙara ‘yan kwanaki sai na isa wani gari mani’imci wai shi Yamel. Ko da na fuskanto garin sai na yi ta jin ganguna da kalangai suna tashi, su kakaki, da farai, da algaitu, sai busa su a ke yi. Shagali dai ba kama hannun yaro. Ina tafiya sai na ga wani yaro yana ta gudu za shi wurin biki. Na kira shi na ce. “Kai samari, yau garin lafiya?”

Yaron ya ce, “Mowar Sarki aka kawo wa mata yau. ”

Na ce, “Daga ina?”

Yaron ya ce, “Yar sarkin Ƙaryatun Ni’ima ce aka gama su. ”

“Ko da na shiga garin, ban ko zauna ba sai ƙofar fada wajen da a ke biki. Na shiga biki, na yi ruwa na tsaki, kamar ƙanena aka sa a lalle. Nan da nan duk na shahara ga maroƙa, suka tambayi sunana. Na ce, “Alhaji Imam. ” Ana biki da dala dala. Amma ni fam guda guda, na ke yi”.

“Wannan shagali da na yi ya sa Sarki ya yi maraba da ni Muka yi abota da ɗan Sarki, dare kaɗai ya ke raba mu”.

“Gisuwa ko ina daga gidajen fadawa, da attajirai, da malamai da sauran manyan gari. Da haka fa duk na azzama cikin garin ƙasar. Saboda haka a wurina masu laifi ke kamun ƙafa. Masu son sarauta gare ni suke nemanta”.

Idan muka nazarci wannan bayani da ya gabata, za mu fahimci cewa, Alhaji Imam ya sami ɗaukaka a birnin Yamel saboda irin kara da ya nuna a wurin bikin ɗan Sarki duk da ba a san shi ba. Watau ya shiga cikin bikin inda ya yi ruwa ya yi tsaki kamar ana bikin ƙanensa. Wannan kuwa ya faru ne, saboda a tsarin tarbiyyar Bahaushe ta gargajiya, wadda ta yi horon idan wata hidima ta sami ‘yan’uwa ko abokan arziki, za su zo a yi hidimar da su don ƙara nuna kara da alkunya.

Ba a nan wannan al’amari na nuna kara ya tsaya ba, don kuwa Sarkin Aljannu da kansa ya yaba da irin karar da Alhaji Imam ya nuna wa Liman duk da kasancewar ba shi ya haife shi ba a shafi na 37, kamar haka:

“Na gaya masa abin da ya kawo ni tun daga farko har ƙarshe ban ɓoye masa kome ba, har da labarin Saƙimu wana. Ya yi mamaki, ya ce, “Lalle ka cika ɗa, tun da ka sai da ranka don uban wani. ”

 

4. 0 Kammalawa

Hausawa na yi wa saniya kirari da suke cewa, “Nagge daɗi goma ba na zubarwa. ” Haka wannan al’amari yake idan aka danganta wannan karin magana da ire-iren ƙunshiyar da take cikin littafin Ruwan Bagaja. Dalilin da ya sa na ambaci haka kuwa shi ne, dukkan wanda ya nazarci wannan littafi zai tarar yana ƙunshi da abubuwa masu tarin yawa waɗanda suka shafi dukkan rayuwar Hausawa ta gargajiya, wadda ta sami nason addinin Musulunci da kuma zamananci. Haka kuma, wannan littafi ya ƙunshi wasu abubuwan waɗanda suka shafi tarihi, da labarin ƙasa, da tafiye – tafiye waɗanda suka bayyana halin zamantakewar Hausawa. Kamar yadda aka gani a bayanan da suka gabata na wannan takarda, an yi ɗan ƙoƙarin kawo wani ɓangare na al’adun Hausawa kamar yadda wannan littafi na Ruwan Bagaja, ya hango su, watau tarbiyyar Hausawa. A wannan mahanga, an kawo bayanai waɗanda suka bayyana tarbiyyar Hausawa dangane da yadda aka fito da ita cikin wannan littafi wadda ta shafi kiyaye dokokin addini, da biyayya ga shugabanci, da gaskiya da riƙon amana, da sadar da zumunci, da taimakon juna, da riƙo da sana’a, da kuma juriya da jarunta.

 

Manazarta

Al-Bukhari, M. I. (Ba Ranar Bugu) Al-Sahihul Bukhari, Beirut-Lebanon: Dar-al-Fikr.

Alhassan, H. da Wasu, (1982) Zaman Hausawa. Zariya: Institute of Education Press, ABU.

Muhammadu Bello, U. Ɗ. (Ba Ranar Bugu) Fassarar Maƙala Mai Taken Usul al-Siyasa, Babu Sunan Wanda ya Fassara ta Zuwa Harshen Ingilishi.

Emarah, M. R. (1430 AH, 2009) Fassarar Littafin ‘Al-Kbae’r (The Major Sins) Zuwa harshen Ingilishi, El-Mansoura – Egypt, Dar Al-Manarah.

Gumi, A. M. (1979/1399A. H. ) Tarjamar Ma’anonin Alƙur’ani Zuwa Harshen Hausa. Beirut-Lebanon: Dar-al-Arabia.

Gusau, A. R. (2004) Faɗakar da Al’umma a kan Riƙo da Sana’a, Fassarar Littafin Tanbitul Ummati Alal Tikhadhil Hirfati, Wanda Muhammadu Sambo Ɗan Ashafa ya Wallafa. Gusau: Farin Batu Digital Press.

Ibrahim, M. S. (1982) ”Dangantakar Al’ada da Addini:Tasirin Musulunci kan Rayuwar Hausawa ta Gargajiya, Kundin Digiri na Biyu. Kano: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.

Imam, A. A. (1966) Ruwan Bagaja.  Zariya:NNPC.

Isah, Z. (2006) “Gaskiya a Tunanin Hausawa”, Kundin Digiri na Farko. Zariya: Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya da Afirka, Tsangayar Fasaha, Jami’ar Ahmadu Bello.

Sallau, B. A. “Tarbiyyar Hausawa a Matsayin Ginshiƙi na Samar da Ingatacciyar Al’umma”, Takarda da aka Gabatar a Babban Taron Ƙasa na Farko, Wanda Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano, ta Gudanar a kan Harshe da Adabi, da Al’adu, Daga Ranar Litinin 14 Zuwa Laraba 16 ga Watan Janairu, 2013.

Smith, M. G. (1957) "The Hausa System of Social Status",  in Africa Vol. ƊƊƁII. No. 1.

Shu’aibu, M. (2003) “Gurbin Gaskiya Cikin Adabin Hausa”, Kundin Digiri na Biyu. Sakkwato: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Yahaya, I. Y. (1988), Hausa a Rubuce: Tarihin Rubuce-Rubuce Cikin Hausa. Zariya: NNPC. 

www.amsoshi.com

Post a Comment

0 Comments