TAMBAYA (02) ❓
Fatan katashi lpy yauwa dama inaso namaka wata
tambaya akwai wata kawata tanada saurayi kuma yanasonta itama haka Amma daga
baya seyafara bujiromata dawasu abubuwa misali idan yaxo sungama zance seyace
setayi kissing nashi kokuma hugging nashi itakuma bataso shine take fadamin
nabata shawara rabuwa zatai da shi kokuma meyakamata tayimasa yadaina
AMSA:
USMANNOOR: To da farko dai muna addu'a Allah ya
shiryi wannan saurayi nata domin kuwa wannan ba dabi'a ce mai kyau ba
Abin na lura anan shine daya daga cikinsu kokuma
gaba dayansu sun gina soyayyarne akan tafarkin son kai, ma'ana basu miqawa
Allah zabi ba ta hanyar yin addu'ar neman zabin Allah SWT wato ISTIKHARA, kamar
yanda Jabir Bin Abdullah ya rawaito hadisin da isnadi mai kyau (Addu'ar tazo a
cikin littafin Hisnul Muslim wallafar marigayi Shaikh Sa'ed Alqahtany), domin
kuwa duk wanda zaiyi addu'ar ISTIKHARA da zuciya daya bazai bige da irin wannan
ashararancin ba, domin kuwa hakan daga shaidan ne, yayi amfanida son zuciyarnan
da aka gina soyayyar akai
Na 2 kuma akwai tasirin so, wanda shine yasa
qawartaki ta kasa rabuwa da shi har saita tambayi shawararki, a yanzun haka son
da take nuna masa yakai mataki na 3 a cikin matakai 5 a fahimtar wasu al'ummar.
Matakin 1. shine kaga mutum ya birgeka amman kana wucesa saika mantashi. Na 2
shine wanda idan ka hadu da shi halinsa ya burgeka saikaji kana sonshi koda
kuwan ba aurensa zakayiba. Na 3 kuma gaba daya zaizamana baka son rabuwa da shi
koda kuwan yana aikata laifi saboda kana masa kwadayin shiriya, ma'aurata sunfi
bayyana wannan. Na 4 kuma son da mukeyiwa Annabi SAW wanda anason yafi son
kowanne mutum, sannan na 5 kuma na karshe son da mukeyiwa mahaliccinmu wato
Allah SWT
Kuskuren da tayi anan shine, ta dauki mataki na 3
wato son da ma'aurata suke a junansu alhalin ita saurayintane kawai, shiyasa
take shakkar rabuwa dashi. Anan yakamata tasanardashi cewar bazan iya kissing
ko hugging nakaba domin kuwa Allah SWT ya ce a cikin Suratun Nur ayata 3
( الزَّانِي لَا يَنكِحُ إِلَّا زَانِيَةً أَوْ مُشْرِكَةً وَالزَّانِيَةُ لَا يَنكِحُهَا إِلَّا زَانٍ أَوْ مُشْرِكٌ ۚ وَحُرِّمَ ذَٰلِكَ عَلَى الْمُؤْمِنِينَ )
النور (3) An-Noor
Mazinãci bã ya aure fãce da mazinãciya kõ
mushirika, kuma mazinãciya bãbu mai aurenta fãce mazinãci kõ mushiriki. Kuma an
haramta wannan a kan mũminai.
Sannan kuma Allah ya ce a cikin Suratul Isra ayata
32:
( وَلَا تَقْرَبُوا الزِّنَا ۖ إِنَّهُ كَانَ فَاحِشَةً وَسَاءَ سَبِيلًا )
الإسراء (32) Al-Israa
Kuma kada ku kusanci zina. Lalle ne ita ta kasance
alfãsha ce kuma tã mũnãna ga zama hanya
Mu fahimtafa bawai kada mu aikataba, saboda girman
laifin saiyace KADA MU KUSANCETA, to kinga anan baima kamata ya ce rungumeshi
kokuma tayi kissing dinsaba, domin kuwa a matsayinmu na Bani Adama, Allah ya
haliccemu kuma yasaka sinadarin adrenaline (hormones) a jikinmu wanda a duk
sanda jinsin dayanmu yahadu da na daya to hakan zai janyo sha'awa har yakaiga
fadawa tarkon Zina (indai ba ga ma'aurataba masu raya sunnan Annabi SAW ba),
shiyasa akace kada ku kusanci Zina
Ma'anar kissing shine, goga lebe akan leben wani
domin tabbatarda tsantsar soyayya kokuma qauna, anan shi saurayinnata bayyana
mata yayi bawai tabbatarwaba kuskuren kenan, kamata yayi ya tabbatarda yana
sonta tayi kissing din idan ya aureta amman sai ya bayyana ma'ana yanasonta da
Zina bawai da aureba. Ma'anar hugging kuma shine rungume mace ko namiji wanda
ba muharramiba shi wannan kanin Zina ne domin indai za a kira Kissing da gambo
to Zina da Hugging twins ne. Kuma akwai Sahihin Hadisin da Annabi SAW ya ce: Da
dayanku ya hada hannu da mace (gaisuwa) gwara ya zauna akan garwashi
Dangane da batun kissing kuma, ya tabbata a cikin
Hadisi Sahihi Nana Aisha (RA) tace: "Manzon Allah SAW yakasance yana
sumbatar iyalansa a duk sanda ya shigo gidansa".
Haka kuma Urwah RA ya rawaito daga Nana Aisha RA
tace masa: "Annabi SAW ya sumbaci daya daga cikin matansa". Sai Urwah
RA ya tambayi Nana Aisha RA: "Ko dai kece wadda ya sumbata (kissing)
?" Sai Nana Aisha RA tayi murmushin (Wanda haka ke nuni da ita Ma'aiki SAW
yayiwa kiss
(Hadisin yana cikin Sunan al-Tirmidhi 86, Sunan
abu-Dawud 181 da kuma Sunan al-Nasa'i 170)
Wannan shine abin da yawancin mazajen yanzu suka
kasa koya shiyasa aketa samun rashin fahimta dakuma yawaitar sakin aure
akai-akai, kissing matarka yana nufin tabbatarda so da qaunar da kake mata, da
baka sonta ai da bazaka biya sadakintaba, amman duk anyi watsi da Sunnar Annabi
SAW shiyasa muketa shan wahala a rayuwarmu. Idan wani magidancin ya ce kai
akwai kunyafa nayi kissing matata kuma raini na iya shiga tsakaninmu to sai
muce masa a ba wanda yakai Annabi SAW kunya (Kamar yanda ya tabbata a cikin
Seerah) kuma maimakon zubewar qima saidai hakan ya qara janyo so da qauna a
tsakani
Wannan kenan, fatan magidanta zasu dinga dabbaqa
wagga Sunnah
Mafita ga shi wancan saurayinnata anan shine
yakamata a sanardashi dalilin dayasa ma har yake bukatar tayi masa hakan
(kissing din) wanda yana cikin ilimin addinin Islam wanda kimiyya ta tabbatarda
hakan, cewar qwaqwalwar mutum ta rabu kaso 4. Na 1: Temporal-lobe wanda shine
wajenda yake tattara saqon haddace abu, koyon abu, koyon yare da daukar sauti
idan yakasance mai yawan sauraren kide-kidene saurayinnaki saiya daina domin
kuwan suna tasiri kuma suna kai mutum ga aikata Zina. Na 2: Parietal-lobe
wajenda yake tattara tabawa, karatu, shauqi, gane fuska, gane lokaci, motsawa,
hangen nesa, idan shauqinsa yakai wani mataki to zai dinga bayyana sha'awarsa
anan kinga dalilin dayasa yayi batun tayi hugging dinsa kenan
Na 3: occipital-lobe wanda yake gane kalar abu,
girman ko qanqanta, gane nisa ko tazarar abu, adana saqonnin gani, idan suna
zance ta matso kusa da shi to shaidanne na ukunsu haka idan mai sha'awar kallon
abin da aka haramtane to anan yakan tasirantu da ya rungumeta kokuma kissing
dinta. Na 4: frontal-lobe wanda akafi sanida forelock shine gaban goshin mutum
wajenda Allah ya tsarawa qwaqwalwar mutum ta adana, nutsuwa, tunani, hukunci,
kawarda matsala, hangen gaba, halayya, dabi'a, aikin zunubin da yake aikatawa
dakuma qaryar da mutum yakeyi, kamar yanda Allah SWT ya bamu labarin halayyar
maqaryacinnan Abu Jahal maqiyin Musulunci da sukai zamani da Annabi SAW a cikin
Suratul Alaq "14) Ashe baisaniba Allah yana gani ? 15) A'aha ! Lallene
idan bai hanuba, lallene za Mu ja gashin makwarkwada (fore-lock) 16) Makwarkwada
makaryaciya, mai laifi (Frontal-lobe), to anan sai a sanardashi wannan
saurayinnata ta hanyar tura masa wannan ilimin daganan muna saran zai yiwa
kansa karatun ta nutsu ya koma ga Allah ya daina bukatar hakan
A karshe, shawarar da zan bawa kawarnan taki
shine: Ta ilimantar da shi ta sanardashi girman zunubin hakan, ta
kwadaitardashi cewar so take su kasance tare har a cikin Aljannah gidan da babu
tsufa ballantana mutuwa, idan ya dauka Alhamdulillah haka muke so amman idan ya
nuna bazai dau shawararba sai kawai ta rabudashi, tayi addu'ar Allah ya zaba
mata saurayi Nagari domin kuwan ya tabbatar mata da cewar shi din ba Nagari
baneba
Wallahu ta'ala a'alam
Aturawa yan uwa musulmi maza da mata domin mu
amfana da ilimin baki daya
Amsawa:
✍️Usman
Danliti Mato (Usmannoor_As-salafy)
Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
WHATSAPP👇
https://chat.whatsapp.com/Fc3hX6HoDt65aKhhKOiDpX
https:///
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.