Ticker

6/recent/ticker-posts

Nayi Mafarki Mage Tana Cizo Na

TAMABAYA (07)

Assalamu alaikum brk d sapia yg y alamura...Allah y temakA. Nace watace tace n tmbya mata Dan Allah menene sahihin mafarkin mage kuma tana cizonta?? Ngd

AMSA

Waalaikumussalam, warahmatullahi, wabarakatuhum

Fassarar mafarki ilimi ne mai zaman kansa saboda indai har mutum yana iya tuno mafarki to yanada cikakkiyar ma'ana tunda da akwai hadisin da ya tabbata daga Manzon Allah SAW akanmafarkin alkhairi (kamar na Umra ko Hajji) bushara ce daga Allah SWT, mafarkin sharri kuma  (kamar na shaidanun Aljanu ko na shanuwa tana tunkushin mutum) to daga shaidan ne, saikuma mafarkin da mutum yakeyi silar faruwar wani abu (kamar mutum yaci abinci mai yaji sai ya kwanta baisha ruwaba, zai iya mafarkin gashinan a kusada kogi yana shan ruwa)

Allah SWT ya labarta mana mafarkin da Annabi Yusuf AS yayi na ganin rana, wata da taurari guda 11 wanda mahaifinsa Annabi Yaqub AS ya fassara masa da cewar Allah zai daukakasa akan yan uwansa. Da kuma labarin fassarar mafarkin da Annabi Yusuf yayiwa wadanda aka rufesu a kurkuku tare

Sannan kuma Annabi SAW ya kasance idan ya idar da sallah yakan juyo ya fuskanci sahabbansa RA ya tambayesu shin ko da akwai wanda jiya yayi mafarki ? (Idan an samu sai Annabi SAW ya fada musu fassarar mafarkin)

Imam Malik (Rahimahullah) ya kasance yana da dalibi mai suna Muhammad Ibn Seerin (An haifeshine a garin Basra wato Iraq a shekara ta 33 bayan hijira wanda yayi daidai da 653AD), haka kuma Imam Ibn Seerin ya koyi karatu a wajen Alhasan Ibn Abi al-Hasanul Basry, Ibn Aown, Al-fudhayl, Ibn Iyadh. Allah SWT ya azurta Ibn Seerin da ilimin fassarar mafarki wanda musamman ya rubuta wani shahararren littafi mai suna "Muntakhab Al-Kalam fi Tafsir Al-ahlam

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments