𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum. Malamai suna ta kira cewa a
yawaita addu’a a cikin halin da muke ciki na rashin tsaro, to wai a waɗanne lokuta ne suka dace da yin addu’ar?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam warahmatullahi Wabarkatuh
Ubangijinmu Tabaaraka Wa Ta’aala ya ce:
وَقَالَ رَبُّكُمُ ٱدۡعُونِیۤ أَسۡتَجِبۡ لَكُمۡۚ إِنَّ ٱلَّذِینَ یَسۡتَكۡبِرُونَ عَنۡ عِبَادَتِی سَیَدۡخُلُونَ جَهَنَّمَ دَاخِرِینَ
Kuma Ubangijinku ya ce: Ku yi addu’a gare ni zan
amsa muku, lallai waɗannan
da suke yin girman kai daga yi mini bauta, za su shiga Jahannama suna ƙasƙantattu.
(Surah Ghaafir: 60)
Wannan ya
nuna:
1. Addu’a ita ce haƙiƙanin ibada.
2. Allaah yana son a roƙe shi, shiyasa ya yi
umurni da hakan.
3. Allaah ya yi alƙawarin amsa wa masu addu’a gare shi, idan sun cika sharuɗɗa.
4. Masu girman kai daga yin addu’a ’yan Wutar
Jahannama ne a Lahira.
5. Masu girman kai daga yin addu’a za su samu wulaƙanci
da ƙasƙanci a Lahira
Daga cikin wuraren ko halayen da hadisai sahihai
suka nuna ana karɓar
addu’a a cikinsu akwai waɗannan:
1. A ƙarshen dare. (Sahih Al-Bukhaariy: 1145; Sahih
Muslim: 758)
2. Bayan sallar farilla. (Sahih At-Tirmiziy:
3/167)
3. Tsakanin Kiran Sallah da Iqamah. (Sahih
At-Tirmiziy: 212; Sahih Al-Jaami’: 3408)
4. A cikin kowane dare. (Sahih Muslim: 757)
5. Lokacin saukan ruwan sama. (As-Saheehah: 1469)
6. Ƙarshen yinin ranar Jumma’a, bayan La’asar. (Sahih Al-Bukhaariy: 935; Sahih
Muslim: 852; Zaadul Ma’aad: 2/388-397)
7. Bayan shan ruwan Zamzam. (As-Saheehah: 883)
8. A cikin Sujada. (Sahih Muslim: 479)
9. A bayan farkawa daga barcin da ya kwanta da
tsarki a farkonsa. (As-Saheehah: 3288)
10. Amfani da addu’ar Annabi Yunus (Alaihis
Salaam):
لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ سُبْحَانَكَ إِنِّي كُنْتُ مِنَ الظَّالِمِينَ
(Sahih At-Tirmiziy: 3/168)
11. Addu’ar
musulmi ga ɗan’uwansa
musulmi a ɓoye.
(Sahih Muslim 2733)
12. Istirjaa’i a lokacin aukuwar wata masifa.
Watau:
إنَّا للـهِ وإنَّا إلَيْهِ رَاجِعُونَ، اللَّهُمَّ أجُرْنِي فِي مُصِيْبَتي، وأخْلِفْ لِي خَيْراً مِنْهَا
(Sahih Muslim: 918).
13. A halin tafiya. (As-Saheehah: 1797)
14. A kan wanda ya zalunce shi. (As-Saheehah: 767)
15. Addu'a Mahaifi a kan ɗansa. (Sahih At-Tirmiziy: 2741)
16. Addu'ah Ɗa na-gari ga mahaifinsa. (Sahih Muslim:
1631)
Hanyoyin samun ijaaba (amsar addu’a da biyan buƙata
daga Allaah) suna da yawa. Ga kaɗan
daga cikinsu:
1. Tsarkin zuciya.
2. Farawa da Hamdala da Salati.
3. Sakankancewa da samun ijaaba.
4. Nacewa, da barin yin gaggawa.
5. Godiya a kan ni’imomin Allaah.
6. Amincewa da laifi tare da mayar da haƙƙoƙi, sai
tuba da istighfaar.
7. Ƙanƙan da kai tare da kyakkyawar fata da fargaba.
8. Maimaita addu’a sau uku.
9. Ɗaga hannuwa sama.
10. Tawassuli da Sunaye ko Siffofin Allaah ko kuma
kyawawan ayyukan da bawa ya aikata.
11. Kulawa da cin halal.
12. Nisantan zunubai da saɓo.
Domin ganin dalilai da hujjoji ingantattu a kan waɗannan abubuwa ana iya duba: Muqaddimar
Sharhu Adu’aa’ Minal Kitaab Was Sunnah na As-Shaikh Sa’eed Bn Wahf Al-Qahtaaniy
(Rahimahul Laah) wanda Maahir Bn Abdilhameed (Hafizahul Laah) ya rubuta.
Allaah ya ƙara mana taimako, ya ba mu daman tuba da
yawaita addu’a gare
shi, ya yi mana maganin dukkan masifu da bala’o’in da suke damun mu, ya kawar mana da dukkan firgici da tsoro, ya kawo mana
aminci da kwanciyar hankali.
WALLAHU A'ALAM
Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.