𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum, malam
Menene hukuncin wanda
yai satar jarabawa domin
ya sami aiki??
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus salam Warahmatallahi Wabarkatahu
An Karɓo daga Abu Hurairah R.A Manzon Allah ﷺ yace. Duk wanda ya Ha'incemu to baya daga
cikin mu. (Muslim hadisi na 103)
To faɗin
wannan Hadisi na nuna karara haramcin ha'inci ko da kuwa a Exam ne ko Test haramun
ne mutum yayi satar amsa.
Sheikh Muhammad Saaleh al-Uthaymeen yace; Satar
amsa a jarrabawa haramun ne kuma yakan shafi rayuwar mutum. Domin in ka samu
aiki da wannan certificate na (Diploma ko Degree) da kayi satar amsa a
Jarrabawar to haramun kake ci (ma'ana Salary naka zai zama haramun domin
sakamakon da ka samu aikin da shi na sata ne.).
(Fataawa Noor ad-darb_24/2).
Haka kuma Sheikh Bin Baaz yace; Satar amsa a
jarrabawa haramun ne
(Majmoo al Fataawa Ibn Baaz_6/397).
Dan haka satar amsa haramun ne musamman ma exam
irinsu WAEC, NECO, NABTEB da sauransu.
Gaskiya kaɗan ne cikin dalibai masu rubutawa da basa Satar
amsa. Dan haka ko wani yana sata to kai ka rabu da shi kada ka biye masa kuyi
satar tare.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/DIcJIQrWyLP0oBOMSnDi5P
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
Post your comment or ask a question.