Tattabara uwar alƙawari ta nisa ta ce "Ko yaushe jagororin dajin nan za su fara tausayawa tsuntsaye? Shekaru da yawa muna cikin azabar mulkin Babba-Da-Jaka, yanzu kuma ga shi Jemage shi ma dai yana neman ɗorawa daga inda ya tsaya, Kaico!"
Kurciya ta yi murmurshi sannan ta ce "Da ma ai
mantawa ki ka yi, amma dama ai Jemage ya sha nanatawa cewa zai ɗora
ne daga inda Babba-Da-Jaka ya tsaya, ya ko cika alƙawarin don ga shi nan ya fara aiki
gadan-gadan"
Kanari da ke can gefe kuwa sai ta hau waƙa tana cewa;
"Iya yawan huƙurinku
da juriyar ku,
Iya yawan azabar
da za su yi mu ku.
A zaɓe yawan tsabar da su ka
watsa,
Yawan Kogin wahalar da za ku ratsa.
Tsuntsun da a yini guda ya yi zalama,
Zai shekara ko
yana cikin nadama...
"Ke Kanari! Yi mana shiru! Waƙar ta ki ma duk babu daɗi,
ki ƙyale mu da abin da ke damun mu na ƙara farashin ruwan sinadiri da aka ƙara mana" Kurciya ta katse ta a
fusace.
Bainu ta ce "Duk da dai babu alamun tsufa gare ni,
amma na daɗe a rayuwa ban ga tashin hankali da
matsi da aka shiga irin wannan lokacin ba, yanzu ta kai ta kawo tsuntsaye da
yawa haka su ke kwana babu ƙoto,
tsuntsaye duk an firgice, ni daga yanzu ma sheƙar
bauta zan koma da zama, don da dukkan alamu ƙiyama
ta kusa"
Hazbiya da tunda aka fara zancen ba ta ce komai ba, ta kaɗa
fiffike ta kimtsa sannan ta ce "Na lura ba Jemage kaɗai
ke da laifi ba, akwai majalissar Ragon-Maza, su ma da su ake haɗo
baki a ga na mana azaba, sannan Balbela da ƴan'uwanta
su ma da su, kullum sai a rufe ƙofa
da su, sai su je jihohinsu su nuna su na gari ne, tabbas farin Balbela na
yaudara ne, da ka bincika namanta sai ka ga baƙi
ne"
Tsatsewala ta ce "Haka ne kam, yanzu dai Jemage dai
ya ba su sulalla da yawa, don kowa ya je jiharsa ya yi bajinta sannan ya
taimaki tsuntsayen jiharsa da tallafi don a rage raɗaɗin
da ake ciki, yanzu yakamata tsuntsaye su sanya idanuwa akan Balbelu, don a
tabbatar sun yi amfani da sulallar da Jemage ya ba su a hanyar da ta dace."
Da ya ke dare ya yi, nan tsuntsaye su kai sallama kowa ya
nufi sheƙarsa.
*An hango Alhudahuda a ciƙin
sheƙarsa a tsakkiyar wasu manyan littattafai
sanye da farin gilashi ya na bincike.
Daga Taskar
Mukhtar Mudi Sipikin
22/07/2023
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.