𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mene ne Hukuncin Wanda yake gaggauta sahur da kuma yin buɗa baki cikin dare?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wannan ya saɓawa shiriyar Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama,
kuma wannan koyine da yahudawa da kiristoci da kuma yan shi'a. Abinda yake
Sunnah daga Manzon Allah shi ne gaggauta buɗa baki, kamar
yadda ya zo ahadisin Sahal Manzon
Allah ya ce "Mutane ba za su gushe cikin alkhairi ba matuƙar suna gaggauta buɗa baki". A hadisin Abu Huraira kuma yake cewa
"Addini bazai gushe a bayyane ba matuƙar ana
gaggauta buɗa baki, domin yahudawa da kiristoci sune suke jinkirta buɗa baki.
Shikuma suhur, abinda akeso shi ne a jinkirta shi har
zuwa dab da ketowar alfijir, saboda hadisin Zaidu bin thabit Allah ya ƙara yarda dashi yake cewa "Mun yi suhur tareda Manzon Allah sai muka tashi mukaje mukayi sallah,
sai Anas ya ce sai na tambayi Zaidu yaya gwargwadon gama suhur din da kiran
sallah?? Sai ya ce gwargwadon mutum ya karanta ayoyi hamsin.
Dan haka yin ihtiyaɗi wurin barin suhur ya saɓawa Sunnah, ibnu
Hajar Allah masa rahama yake cewa "yana daga cikin bidi'o'i munana da aka ƙirƙiro awannan zamanin shi ne ƙiran sallah na biyu kafin fitowar alfijir da kusan minti
15 a cikin watan Ramadan, gamida
kashe fitilu wanda ake yinsu amatsayin alama na haramta ci da sha ga duk wanda
zai yi azumi, azaton masu yin hakan shi ne sunayin ihtiyaɗi ne a cikin ibada, hakan ya sa kuma basa ƙiran sallah alokacin buɗa baki har sai
rana da fadi da wasu mintuna duk wai dan su tabbatar da shigan lokaci azaton
su, sai suka gaggauta suhur suka jinkirta buɗa baki, hakan ya
haifar musu da Saɓawa sunnah, hakan ya sa alkhairi ya yi ƙaranci a cikin su, sharri ya yawaita musu, Allah ya mana taimako".
سسبعون مسألة مهمة في الصيام
WALLAHU A’ALAM
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/IƘUc0RxgCwA3JFiEKl8j5E
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
No comments:
Post a Comment
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.