𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Asssalamu alaikum, malam to wanda bai samu talakawan da zai
ba wa zakkar fidda kai ba yaya zai yi?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Zakkar fidda kai Allah maɗaukakin sarki ya wajabtata ta
harshen manzansa sallallahu Alaihi wasallam, a kan maza da mata, yara da manya, bawa da ɗa, kuma Annabi sallallahu
Alaihi wasall ya yi umarni a bayar
da ita kafin afita sallar idi, wanda bai samu talakawan dazai bawa akewayansa
ba, wajibi ne yanemesu agaruruwan da suke kusa dashi, ya yi gaggawar bayar da ita kafin fita sallar idi, bai halatta
yajinkirta zuwa bayan sallar idi, saboda wannan saɓanin Abunda manzan Allah
sallallahu Alaihi wasallam ya yi umarni
dashi ne.
Hakika Annabi sallallahu Alaihi wasallam ya yi umarni afitar da ita kafin afita
sallar idi ya ce: (Duk wanda ya bayar
da ita kafin fita sallar idi hakika zakkah ce karbabbiya wanda ya bayar da ita
bayan sallar idi sadakace cikin sadakoki).
Abunda yake wajibi shi ne mutum yakula sosai yafitar da
ita, ko da kafin idi ne da kwana biyu
ko ɗaya ko uku.
Abdullahi dan Umar Allah yakara yarda da su ya kasance
yana fitar da ita kafin ranar idi dakwana ɗaya ko biyu, wani lokacin kafin
ranar idi da kwana uku hakama sahabbai Allah yakara yarda dasu.
Manufa dai shi ne mutum yafitar da ita daka ranar ashirin
da takwas har zuwa ranar idi, Amma kada yakuskura yajinkirtata harzuwa bayan
sallar idi, idan a inda kake babu talakawa to ka nemesu a wani wajan ko da zakayi tafiyane wajan neman talakawan dazaka bawa.
Abdul'aziz bin baaz fatawa Nurun Alar darbi (2/1209).
WALLAHU A'ALAM
Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/FmJ5Ojsns1KFolTP8ƙu9GT
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.