Ticker

6/recent/ticker-posts

Sharuɗɗan Amsar Addu'a

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alikum Malam ina da tambaya: Mene ne sharuɗdɗan yin addu, a?Maana wanne sharaɗi za ka cika kafin addu'arka ta karɓu?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Allah s.w.t yana karɓar addu'ar bawansa idan bawan ya cika wasu sharuɗɗa kamar haka:

1- Tsantsnta addu'ar ga Allah kaɗai: Ma'ana: ya zama Allah kaɗai ya roƙa kuma gare shi kaɗai ya sallama wa lamurransa bai haɗa shi da kowa ba.

2- Dacewa da koyarwar Manzon Allah s.a.w cikin addu'ar: Saboda addu'a ibada ce kamar sauran ibadu, ibada kuwa ba ta karɓuwa sai ta dace da koyarwar Manzon Allah s.a.w.

3- Yardar zuciya da sakankancewa: Yayin da kake addu'ar da bayanta ka zama mai gamsuwa da yaƙini a zuciyarka cewa Allah zai karɓi addu'arka. Ko da ka ga jinkiri ka nutsu da cewa lallai sakamako yana nan tafe matuƙar ba an ci karo da wani dalili da zai hana a biya maka buƙatarka na daga wasu laifukanka ko rashin dacewar buƙatar da kai ba.

4- Halartowar zuciya da khushu'i da ƙasƙantar da kai ga Allah yayin addu'a.

5- Ƙarfin azama: kada ka roƙi Allah kana mai taraddudi abin zai yiwu ko ba zai yiwu ba, ka roƙi Allah roƙo na yankan shakku.

6- Nisantar cin haram: Ka tsarkake cikinsa da jikinsa daga haram.

7- Kada abin da za ka roƙa ya zama haram ne ko yanke zumunci.

WALLAHU A'ALAM

Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare Da Fadakarwaa Sunnah.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/L8l4xHCd7wUG5xZEmvBbzB

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
************************************** 

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments