Sharuɗɗan Amsar Addu'a
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alikum Malam ina da tambaya: Mene ne sharuɗdɗan yin addu, a?Maana wanne sharaɗi za ka cika kafin addu'arka ta karɓu?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Allah s.w.t yana karɓar addu'ar bawansa idan
bawan ya cika wasu sharuɗɗa kamar haka:
1- Tsantsnta addu'ar ga Allah kaɗai: Ma'ana: ya zama Allah kaɗai ya roƙa kuma gare shi kaɗai ya sallama wa lamurransa
bai haɗa shi da kowa ba.
2- Dacewa da koyarwar Manzon Allah s.a.w cikin
addu'ar: Saboda addu'a ibada ce kamar sauran ibadu, ibada kuwa ba ta karɓuwa sai ta dace da koyarwar
Manzon Allah s.a.w.
3- Yardar zuciya da sakankancewa: Yayin da kake
addu'ar da bayanta ka zama mai gamsuwa da yaƙini a zuciyarka cewa Allah
zai karɓi addu'arka. Ko da ka ga jinkiri ka nutsu da cewa
lallai sakamako yana nan tafe matuƙar ba an ci karo da wani
dalili da zai hana a biya maka buƙatarka na daga wasu
laifukanka ko rashin dacewar buƙatar da kai ba.
4- Halartowar zuciya da khushu'i da ƙasƙantar da kai ga Allah yayin
addu'a.
5- Ƙarfin azama: kada ka roƙi Allah kana mai taraddudi abin zai yiwu ko ba zai yiwu ba,
ka roƙi Allah roƙo na yankan shakku.
6- Nisantar cin haram: Ka tsarkake cikinsa da jikinsa daga haram.
7- Kada abin da za ka roƙa ya zama haram ne ko yanke
zumunci.
WALLAHU A'ALAM
Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Fadakarwaa Sunnah.
SHARUƊƊAN AMSAR ADDU'A
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alikum Malam
ina da tambaya: Mene ne sharuɗdɗan yin addu, a? Ma'ana wanne sharaɗi za ka cika kafin addu'arka ta karɓu?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumusalam
warahmatallahi wabarakatuh.
Allah s.w.t yana karɓar addu'ar bawansa idan bawan ya cika wasu sharuɗɗa kamar haka
1. Tsantsanta addu'ar ga
Allah kaɗai: Ma'ana: ya zama Allah kaɗai ya roƙa kuma gare shi kaɗai ya sallama wa
lamurransa bai haɗa shi da kowa
ba.
2. Dacewa da koyarwar
Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam cikin addu'ar: Saboda addu'a ibada ce
kamar sauran ibadu, ibada kuwa ba ta karɓuwa sai ta dace
da koyarwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam.
3. Yardar zuciya da sakankancewa:
Yayin da kake addu'ar da bayanta ka zama mai gamsuwa da yaƙini a zuciyarka cewa Allah zai karɓi addu'arka. Ko da ka ga jinkiri ka nutsu da cewa lallai
sakamako yana nan tafe matuƙar ba an ci karo da wani dalili da zai hana a biya maka buƙatarka na daga wasu
laifukanka ko rashin dacewar buƙatar da kai ba.
4. Halartowar zuciya da
khushu'i da ƙasƙantar da kai ga Allah
yayin addu'a.
5. Ƙarfin azama: kada ka roƙi Allah kana mai taraddudi abin zai yiwu ko ba zai
yiwu ba, ka roƙi Allah roƙo na yankan shakku.
6. Nisantar cin haram:
Ka tsarkake cikinsa da jikinsa daga haram. Yana daga cikin sharaɗin addu'a musulmi ya kasance babu haram a cikinsa (baici
abincin haram ko abin sha na haram ba),
7. Kada abin da za ka roƙa ya zama haram ne.
8. Musulmi ya kasance
bai yanke zumunta ba.
9. Nisanci Neman
gaggawar karɓawa. Ya tabbata a hadisi
cewa; An Karɓo daga Abu Hurayrah
(R.A) Ya ce; Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam) Ya ce: (Allah) yana karɓawa ɗayanku
(addu'arsa) matuqar baiyi gaggawa ba, (shi ne) ya ce nayi addu'a (amma har
yanzu) ba a amsamin ba. (Bukhari, 5865. Muslim, 2735).
10. Akwai wasu lokuta
idan bawa yayi addu'a Allah na karɓa masa kai
tsaye. Misali kamar sulusin dare na karshe kamar yadda ya tabbata a hadisi.
11. An karbo hadisi daga
Buraidata (r.a) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam) ya ji wani
mutum yana cewa
اللَّهُمَّ إِنِّي أَسْأَلُكَ بِأَنِّي أَشْهَدُ أَنَّكَ أَنْتَ
اللَّهُ لاَ إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ الأَحَدُ الصَّمَدُ الَّذِي لَمْ يَلِدْ وَلَمْ يُولَدْ
وَلَمْ يَكُنْ لَهُ كُفُوًا أَحَدٌ
MA'ANA: "Ya Allah
hakika ina rokonka, na shaida kai ne Allah, babu abin bautawa da gaskiya sai
kai, makaɗaici, madawwami, wanda
ba ya haifuwa kuma ba a haife shi ba, kuma babu wanda ya kai shi." sai
manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallam) ya ce: “Lallai ka yi roƙo da sunan da Idan aka
yi roƙo da shi ana bayarwa,
kuma idan aka yi addu'a da shi ana amsawa". mutane huɗu suka ruwaito shi, Ibn Hibban ya inganta shi.
Wannan hadisin na nuna
mana ke nan ana saurin Amsa addu'ar Wanda ya yi amfani da waɗannan sunayen ke nan. Don haka Idan mutum zaiyi addu'a,
sai ya fara ambaton waɗancan sunayen,
sannan sai addu'ar ta biyo baya.
Manzon Allah (Sallallahu
alaihi Wasallam) Ya ce : "hakika ubangijinku mai kunya ne, mai karamci ne.
yana jin kunyar bawansa yayin da ya cira hannayensa ya rokeshi, ace ya mayar
dasu ba tare da komai ba".
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/L8l4xHCd7wUG5xZEmvBbzB
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.