𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalaamu alaikum wa rahmatul laah. Mallam Ni budurwa ce kuma gobe za a ɗaura mini aure zan zama amarya, wace shawara za a ba ni da kuma wasiyya?
𝐀𝐌𝐒𝐀👇
Wa alaikumus salamu wa rahmatullahi wa
barakatuh.
Shawarar da za a baki ba ta da yawa kuma ba ta da
amfani har fa sai idan za ki aiki da ita.
Da farko dai, ki yi haƙuri, domin aure ibadah ne,
kuma ba wata ibadah da ke yiwuwa sai da haƙuri. Ki zamo mai tsoron
Allah da taķawa, hakan bai samuwa sai da zuwa makaranta. Don haka ki maida
hankali wajen neman ilmi.
Ki zama mai cikakkiyar biyayya ga Allah da Manzonsa ﷺ kafin ga mijin ki. Haka ki
so mijin ki, amma ki fifita son Allah da Manzonsa ﷺ a kan son sa. Ki sani
wannan zama na aure da duk abin da zai haifar ibadah ne.
Ki zamo mai
biyayya ga mijin ki har ki fifita biyayyar ki a kan ta iyayen ki, biyayyar
Allah da ta Manzo Allah ﷺ kaɗai ke fin ta shi a matsayin
sa na mijin ki. Ki girmama iyaye, yan'uwa da aminan sa.
Ki zamo mai yawaita addu'ar alkhairi gare shi a ko da
yaushe. Ki zamo mai wadatuwa da duk abin da ya iya baki, sannan ki gode masa.
Ki kula da tsabta da canja girki mai daɗi a kai a kai. Ki ji, ki yi
kamar baki ji ba, ki gani kiyi kamar baki gani ba. Ki guji almubazzaranci da
tozarta masa dukiya ko abinci in ya kawo, ki zamo mai tattali. Ki zamo mai raha
a labarin ki da shi.
A wannan farko zaman na ku, ki ƙoƙarin gane abin da yake so,
ko ki tambaye shi, da irin abin da baya so don ki guji yi masa su da
ganganci.
Kar ki dinga bashi labarin kawayen ki. Ki guji kai
labarin ku na sharri, a wurin yan'uwa ko iyayen ki. Kina da damar farun
albarkacin bakin ki, amma da kin hararo zai koma musu, toh ki kame bakin ki.
Haka a lokacin saɓani da ɓacin rai, ki koyi bashi haƙuri. Ki zamo mai taimakon mijin ki da karfin ki da dukiyar
ki. Ki zamo mai tausayin mijin ki. Mijinki ya zamo abokin shawarar ki ba wanin
sa ba.
Daga ƙarshe kar ki dauko salon
zaman wasu ma'aurata ki kawo gidan ki, sai na alkhairi. Wannan kaɗan ne daga cikin abin da za
a baki na Shawara.
Wallahu ta'ala a'lam.
Amsawa:
Malam Aliyu Abubakar Masanawa
Ku Kasance Da mu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/BXjuXb1WxX99NV3OsXPnLV
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.