𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum. Allah yakarawa Malam lafiya, dan Allah tambaya nake. Idan namiji yana da mata biyu sai ɗaya ta yi tafiya tayo kwanaki ta dawo, tambayata a nan ita ce ranar da ta dawo wane daki ya kamata mijin ya kwana?
𝐀𝐌𝐒𝐀👇
Wa'alaykumussalam. Mu'amala ta aure da zamantakewa
abin da shari'a ke buƙata a cikin su shi ne yin
adalci, aduk yadda mai gida da iyalansa suka tsara yadda za su zauna matuka an
kiyaye ka'idar (Kada a yi cuta kuma kada a cutar) toh babu laifi, don haka ba
laifi don ya shiga dakin wadda ta yi tafiya duba ga an dade ba a haduba.
Wallahu A'alam
Amsawa✍🏻
Malam Nuruddeen Muhammad Mujaheed
Ku Kasance Da mu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/GcU1I5wjOB18K4PA6eURƘƘ
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.