Ticker

6/recent/ticker-posts

Dangantakar Jigogin Wasu Labaran Magana Jari Ce Da Na Tatsuniyoyin Hausa

Jigo na nufin babbar manufa ko muhimmin saƙon da mai aikin adabi ke da shi ga jama’ar da aka shirya aikin adabin domin su.

Dangantakar Jigogin Wasu Labaran Magana Jari Ce Da Na Tatsuniyoyin Hausa 

 Abdulbasir Ahmad Atuwo1
Abdurrahman Faruk2

1Department of Nigerian Languages, Usmanu Danfodiyo University, Sakkwato
2Department of Nigerian Languages, Umaru Musa Yar’adua University, Katsina 

Tsakure

Idan dai mutum ma’abocin karatun rubutattun labaran Hausa ne, ko mai sha’awar sauraro ko karatun tatsuniyoyin Hausa ne, babu shakka zai riƙa ganin wasu kamannu tsakanin wasu rubutatttun labaran Hausa da kuma tsatsuniyoyi na Hausa. Wannan dalili ne ya sa wannan takarda ta yi tsokaci a kan kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin rubutattun labaran Hausa da tatsuniyoyin Hausa. Taken wannan takarda shi ne, “Dangantakar Jigogin Wasu Labaran Magana Jari Ce da Na Tatsuniyoyin Hausa.” Manufar takardar ita ce, kwatanta dangantakar da ke akwai tsakanin wasu labaran da ke cikin Magana Jari Ce I - III da tatsuniyoyin Hausa ta fuskar jigogi, wato saƙonnin da suke ɗauke da su. An karanta wasu ayyukan masana da suka yi a kan fagagen tatsuniyoyi da rubutattun labaran Hausa. An kuma karanta littafin Magana Jari Ce I-III a matsayin dabaru da hanyoyin gudanar da bincike. An ɗora wannan bincike a kan Ra’in Tsarin Adabi (Structural Theory) na Propp (1928). Bayan an ƙare binciken, sai aka gano cewa, akwai kyakkyawar alaƙa ta fuskar jigogi tsakanin wasu labaran Magana Jari Ce I-III da tatsuniyoyin Hausa. Wannan alaƙa kamar yadda aka gano ta samu ne saboda rubutattun labaran Hausa sun tusgo gyauronsu ne daga tatsuniyoyin Hausa. Haka kuma, mawallafin littafin Magana Jari Ce I-III wato Abubakar Imam ya daɗe yana sauraron tsatsunoyin Hausa daga bakin kakanninsa tun yana yaro ƙarami kamar yadda kowane yaro ke tashi da sauraron su a ƙasar Hausa. Wannan babu shakka ya tasiranci tunanin Abubakar Imam wajen gina littafin Magana Jari Ce I-III.

Fitilun Kalmomi: Jigo; Tatsuniya; Labari; Magana Jari Ce

 

1.0 Gabatarwa

     Babu wata nahiya ta duniya da al’ummarta ba ta da labaran kunne-ya-girmi-kaka. Da ire-iren waɗannan labarai ne kowace al’umma ke tashi, kuma a cikinsu ne suke samun tarihin asali da samuwar al’ummar tasu. Nahiyar Afirika ma ba a bar ta a baya ba dangane da tattalin ire-iren waɗannan labarai. Shi ya sa ma al’ummomin nahiyar suka yi tarayya a kan tsari iri ɗaya na aiwatarwa da bayar da waɗannan labarai (Usman, 2013: 8). A ƙasar Hausa, labaran nan na kunne-ya-girmi-kaka da aka fi sani da tatsuniyoyi. Ita tatsuniya labari ne ƙagagge da aka ƙirƙira aka yi amfani da gizo da ƙoƙi da dabbobi da ƙwari da tsirrai da tsunuka da aljannu na tudu da na ruwa da ma wasu abubuwa da babu su a zahiri waɗanda tunani ke kintatowa. Ana ƙaga tatsuniya da nufin a ba al’ummar da ke tasowa wato yara tarbiyya a kan hani da horo domin su tashi masu amfani ga kansu da iyayensu da al’ummominsu da ma duniya baki ɗaya (Zarruƙ, 1987: 5).

            Kafin zuwan Larabawa da Turawa a ƙasar Hausa, wato kafin Bahaushe ya yi mu’amala da baƙin al’ummomin da suka kawo masa tsarin karatu da rubutu, waɗannan labarai na tatsuniya da ka ake ƙirƙirar su, a bayar da su da baka ga yara, kuma da ka yaran suke adana su, su tashi da su, su yi amfani da su wajen daidaita rayuwarsu, sannan idan sun girma su ma, su bayar da su ga ƙannensu ko ‘ya’yansu da ke tasowa. Ke nan dangane da tatsuniya, ana rama wa kura aniyarta ne, ko ma a ce inda akuyar gaba ta sha ruwa, a nan ta baya ita ma za ta sha (Furniss, 1996: 57).

            Kamar yadda aka nuna a sama, Bahushe ya sami ilmin karatu da rubutu ne daga baƙin al’ummomi da suka yi ta karakaina ƙasar Hausa da burace-burace iri-iri (Yahaya, 1988: 8). Larabawa ne suka fara zuwa ƙasar Hausa suka koya wa Hausawa karatu da rubutu a cikin haruffan Larabci. Da Hausawa suka ƙware, sai suka fara tunanin rubuta nasu harshen na Hausa da haruffan Larabci, ganin cewa sun fahimci muryar kowane baƙi da wasali na Larabci. Wannan fasaha ta rubuta harshen Hausa da haruffan Larabci ce ake kira Rubutun Ajami (Yahaya, 1988: 31).

Bayan shuɗewar Larabawa, al’ummomin da suka ratso ƙasar Hausa su ne Turawa a ƙarshen ƙarni na sha tara (Ƙ19) zuwa farkon ƙarni na ashirin (Ƙ20). Turawa sun zo wa Hausawa da ilmin boko, wato karatu da rubutu cikin haruffan Turanci. Hausawa sun dage sun iya, daga nan sai suka fara tunanin rubuta harshen nasu na Hausa cikin baƙaƙe da wasula na boko. Wannan lamari ne ya kawo Hausar Boko (Yahaya, 1988: 72).

            Tun da rubutu da karatu cikin Hausar boko ya samu a ƙasar Hausa, sai Hausawan suka fara tunanin mayar da rubutattun labaran Hausa cikin tsarin Hausar Boko. Kodayake, kafin Hausawa su fara wannan namijin ƙoƙari na rubuta ƙagaggun labaran Hausa cikin Hausar boko, Turawan suka fara yin wannan shiga hanci da ƙudundune. Sun kutsa sosai sun koyi magana da harshen Hausa, saboda haka, sai suka fara tunanin rubuta tatsuniyoyin Hausa da Hausar boko. Da haka ne littafin Edgar (1911) da na Skinner (1969) suka samu (Furniss, 1996: 56). Tun bayan bayyanar waɗannan rubutattun tatsuniyoyi na Hausa, aka ci gaba da samun rubutattun labaran Hausa a ƙasar Hausa. Ken an akwai kyakkyawar alaƙa tsakanin ƙagaggun labaran tastuniyoyi da kuma rubutattaun labaran Hausa.

            Manufar wannan takarda ita ce yin sharhi game da labaran tatsuniya da kuma wasu labaran da ke cikin littafin Magana Jari Ce I-III. Takardar ta nazarci dangantakar da tsakanin tatsuniyoyin Hausa da wasu labaran Magana Jari Ce I-III ta fuskar jigogin da labaran suka ƙunsa. Takardar ta lura duk rubuce-rubucen da suka gabata na masana da manazarta, babu wanda ya yi tsokaci dangane da wannan dangantaka, duk da kuwa cewa fage mai muhimmanci. Rubuce-rubucen da aka yi tayi a kan tasuniyoyi da kuma littafin Magana jari Ce I-III, sun ta’allaƙa ne kawai ga nazarce-nazarce a kan gundarin tatsuniya (Edgar (1911) da (Ruth, 1970) da (Poul, 1970) da (Yahaya, 1971) da (Thomson 1977) da (Umar 1982) da (Zarruƙ, 1986) da (Yahaya 1992) da (Koko, 2009) da Usman (2012) da Usman (2013) da sauransu. Wasu kuma nazarce-nazarcen kuma, sun karkata akalarsu su ne a kan littafin Magana Jari Ce I-III, inda suka yi tsokaci a kan fagage daban-daban da littafin ya ƙunsa. Misali ayyuka ire-iren su Ibrahim (1990) da Musa (1993) da Geza (2004) da Guga (2010) da Hassan (2013) da Guga (2015). Duka waɗannan rubuce-rubuce dam asana da manazarta suka yi, sun shafi labaran Hausa da kuma littafin Magana Jari Ce. Kodayake masana sun bar giɓi, wato babu ɗaya daga cikinsu da ya danganta wasu labaran da ke cikin littafin Magana Jari Ce I-III da kuma tatsuniyoyin Hausa, saboda haka wannan takarda ta yi yunƙurin cike wannan giɓi domin ganin an sami daidaito a ɓangaren nazari.

 

1.1 Ra’in Bincike

            An ɗora wannan bincike a kan Ra’in Tsarin Adabi (Structural Theory) wanda Ɓladimir Propp ya ƙirƙiro a shekarar (1928). Wannan ra’i yana ƙarfafa nazarin tsarin adabi ne wanda ya fara ɓulla a doron ƙasa tun kafin shekarar (1960). Kamar yadda maƙirƙirin ra’in ya bayyana, ra’in ya ƙunshi nazarin bayanin sigar labari ne dangane da ginshiƙansa da kuma haɗuwarsu da juna. Ke nan ana maganar wasu rassa na adabi da suke haɗuwa da juna su amfanar da waɗanda aka ƙirƙiri adabin domin su (Gusau, 2001: 37).

Akwai dangantaka tsakanin wannan ra’i da kuma wannan bincike da aka gudanar. Dalili kuwa yadda Ra’in Tsarin Adabi yake bayanin sigogin adabi da yadda suke haɗuwa da juna, wato jigogin aikin adabi da yadda ake samun alaƙa tsakanin wani aikin adabi da wani, haka wannan bincike yake fayyace haɗuwar wasu labaran Magana Jari Ce I-III da tatsuniyoyin Hausa ta fuskar jigogi. Ganin cewa Ra’in Tsarin Adabi da wannan maƙala alƙiblarsu ɗaya ce shi ya sa aka ɗora binciken a kansa.

 

1.2 Labari

              Idan aka ce labari, ana nufin labarai ko wasu bayanai ko ƙagaggen labari ko almara. (Bargery1934: 706). Bayyanawar wani abu da ba a sani ba ma labara ne (CNHN, 2006: 296). Ma’anar da Bargery tare da Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero suka bayar, ba ta gamsar da wannan takarda ba, saboda ma’anar ta taƙaita a kan bayanai ko ƙagaggen labari ko almara. Haka kuma an taƙaita ma’anar ga faɗar abin da ba a sani ba. A wannan lokaci, ma’anar labari ta wuce nan. Saboda haka, aka lalubi ma’anar labari ta ilmi. Dangane da haka, aka dubi ma’anar labari wadda Malumfashi, (2019) ya bayar. Ga abin da Malumfashi ya bayyana a kan labari cewa:

Ayyanannen lamari ne da ke ƙunshe da gaskiya da kuma ƙarya domin a nishaɗantarwa da sa walwala da kuma isar da saƙo. Shi wannan ayyanannen lamari ba ƙagawa ba ce, ba zayyanawa ba ce ba ƙirƙira ko firtsa ba ce, ba kuma wani sanabe ba ne. Haka kuma samuwa da tabbatuwar wannan ayyanannen lamari yana bisa matakan halittar Ɗan’adam da yananyin wanzuwar Ɗan’adam a doron ƙasa musamman abin da ya danganci rayuwar yau da kullum da abin da ƙwaƙwalwa ke rayawa da kitsawa na daga abin da ta ci karo da shi na ji ko gani ko na cikin gado ko kuma zamantakewa ta kusa ko ta nesa ta al’umma (Malumfashi, 2019: 35).

 

Kamar yadda aka gani a sama, ma’anar da Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero ya kawo game da labari taƙaitacciya ce ƙwarai. Dalilil kuwa an sake maimaita kalmar labari ne kawai a cikin wasu kalmomi na daban kamar bayani da almara. Ma’anar da Malumfashi (2009) ya kawo ta fi fito da ma’anar labara a fili. Shi a ra’ayinsa duk bayanin da aka sake ambatowa ga mai sauraro ko karatu wanda dama can ba baƙon abu ba ne ga mai gabatarwa ko mai karɓa. Imma dai ya taɓa ji an faɗa ko ya taɓa gani ko ya taɓa karantawa daga wani littafi. Wannan bayani yana iya kasancewa gaskiya ne ko kuma ƙirƙira ce ta mai gabatarwa. Ke nan ga yadda Malumfashi ya nuna, duk abin da mai gabatar da labara zai faɗa, to, ba shi ne mafarinsa ba, yana da tasirinsa a cikin ƙwaƙawalwarsa da kuma zuciyarsa.

1.3 Ma’anar Jigo

Idan aka yi maganar jigo, ana magana ne a kan saƙo na musamman da marubuci yake ƙoƙarin bayyana wa ga jama’a a ƙagaggen labari ko wasan kwaikwayo ko waƙa (CNHN, 2006: 217). Masana sun bayar da ma’anar jigo daidai gwargwado. A cewar ɗaya daga cikinsu, “Jigo dai kodayaushe yana nufin saƙo ko manufar da abu ke ɗauke da ita zuwa ga waɗanda ake nufi” (Koko, 2009: 18). Kodayake, wani masani ya nuna cewa, “Jigo na nufin manufar marubuci, wadda dukkan bayanai suka dogara da ita, saboda haka ana iya cewa, jigo shi ne saƙon da marubuci ke son sadarwa ga jama’a. Duk wani salo da tsari ko wata dabara da marubuci zai yi amfani da su, zai yi haka ne da nufin isar da saƙon nasa ga jama’a” (Sarɓi, 2007: 71).

Duk idan aka tattara waɗannan ma’anoni da Ƙamusun Hausa da masana suka bayar dangane da jigo, za a iya bayyana jigo da cewa babbar manufa ko muhimmin saƙon da mai aikin adabi ke da shi ga jama’ar da aka shirya aikin adabin domin su. Ke nan jigo shi ne ƙudurin da mawallafi ke da shi ga jama’a. Babu wani aikin adabi da ba ya da jigo ko manufar da aka yi shi dominta. Kowane aikin adabi kamar waƙa da zube da wasan kwaikwayo suna ɗauke da saƙon da aka tsara, wanda ake son a isar ga jama’a. Kowane aikin adabi da irin jigon da yakan zo da shi. Daga cikin ire-iren jigogin da ayyukan adabi kan zo da su sun haɗa da faɗakarwa da ilmantarwa da nishaɗantarwa da hannunka-mai-sanda da tsoratarwa da gargaɗi da sauransu. Akwai kuma ƙananan jigogi ire-iren su jarunta da kishi da ladabi da biyayya da ƙeta da tausayi da sauran illolin wasu miyagun ayyukan da al’adun da zamantakewar al’ummar Hausawa take ƙyama da dai sauransu.

 

2.0 Samuwar Littafin Magana Jari Ce

 

A wajen shekarar 1932-1933, ‘yan ƙasa sun sami ilmin boko bakin gwargawado. Da yawansu sun iya karatu da rubutu. Sai dai kash!, Ga dai ilimi ya samu, amma kuma ga ƙishirwar litattafan karantawa. La’akari da cewa litattafan da ake karantawa a makarantu sun yi ƙaranci, ga rashin dacewa ga ɗalibai. ɗaliban makarantar Elemantare sun gaji da karanata su, saboda babu sauyi. Ga litattafan da saurin gundurar mai karatu, saboda babu ɗaya daga cikinsu da ya shafi tantagaryar adabi. Duka-duka ma litattafan da ake koya wa yara karatu da su guda biyu ne: Daga Aljaman Yara, sai Littafin Koyarwa na Karatu da Rubutu (Malumfashi, 2009: 52).

            Ko da Gwamnatin Arewa ƙarƙashin Hukumar Ilmi ta fahimci wannan matsala ta rashin littattafan karantawa a makarantun Elemantare, sai ta sa wani Jami’inta wato Dr. R.M. East a ƙarƙashin Hukumar Fassara, ya kewaya cikin ƙasa ya yi yekuwar cewa, Hukumar Ilmi za ta sa gasar rubuta ƙagaggun labarai na Hausa. Kamar yadda sunan litattafan ya nuna, an sanya dokokin gasar waɗanda su ne R.M. East ya kewaya ya shaida wa ‘yan ƙasa da suka ilmanta, cewa ba fa fasssara ake so ba, a wannan karon ana buƙatar ƙagawar mawallafi ne. Duk wanda ya yi nasara, za a ba shi kyauta mai tsoka, kuma a buga masa littafinsa kyauta, littattafan su kuma kewaya cikin ƙasa (Malumfashi, 2019: 52).

            Bayan an yi wannan gasa a shekarar 1932-1933, sai aka fitar da sakamakon gasar, inda littattafai biyar suka fice kuma suka lashe gasar. Ga litaffan:

1.      Ruwan Bagaja na Abubakar Kagara

2.      Ganɗoki na Bello Kagara

3.      Shaihu Umar na Abubakar Bauchi

4.      Idon Matambayi na Sani Gwarzo

5.      Jiki Magayi na R.M. East da John Umaru Tafida Zariya (Malumfashi, 2009: 25).

Wannan nasara da Abubakar Imam ya samu ta sa an buga littafinsa na Ruwan Bagaja a shekarar 1933, kuma sai aka aro Abubakar Imam daga Lardin Katsina inda yake aikin koyarwa ya zo ofishin Hukumar Fassara da ke Zariya don ya rubuta littaffan da za a raba a makarantun da ke Arewacin Nijeriya. Kafin ya fara rubuta komai, sai da ya ba da shawarar sauya wa Hukumar fassara suna, wadda aikinta a da fassara ne daga Turanci da Larabci zuwa Hausa. Daga nan sai aka mai da ita Hukumar Talifi, saboda yadda aikin wallafe-wallafen littattafai ya ƙaru ga hukumar (Adamu, 2019: 17).

Aikin da Abubakar Imam ya fara yi ƙarƙashin Hukumar Talifi shi ne rubuta litattafan Magana Jari Ce na I-III. Kafin ya fara wannan aiki, sai da uban gidansa wato Dr. R. M. Esat ya tattara masa littattafan labaran Turawa da Larabawa da Mutanen Sin da na Al’ummar Rasha, ya yi ta karantawa. Da yake Abubakar Imam yana jin harsuna da dama. Da ya naƙalci yadda rubuce-rubucen labaran wasu al’ummomi suke, sai ya yi azama ya fara rubuta Magana Jari Ce (Pweddon, 1977: 151).

Kodayake, Pweddon ya tabbatar da ba Abubakar Imam ne ya rarraba littafin Magana Jari Ce littafi-littafi ba. Abubakar Imam ya faɗa masa haka a hirar da ya yi da shi, sai Abubakar Imam ya tabbatar masa da cewa sam, shi bai karkasa littafin Magana Jari Ce littafi na farko zuwa na uku ba. Shi ya ci gaba da rubuta labaransa kara zube. Duk labarin da ya faɗo masa a rai, sai ya rubuta abinsa. A cewar Imam editan littafin ne wato Dr. R. M. East ya kasarkasa shi zuwa littafi na farko da na biyu da na uku don ya yi daɗin karantawa ga ɗalibai (Pweddon, 1977: 151). A cikin wannan liitafi na Magana Jari Ce wannan maƙaka ta yi nazarin dangantakar jigogin wasu labarin cikinsa da tatsuniyoyin Hausa.

3.0 Tatsuniyar Hausa         

Tatsuniya labari ne da ake ba wa yara na hikima domin hira (CNHN, 2006: 433). Tatsuniyar Hausa ƙagaggen labari ne da ake shiryawa game da gizo ko waninsa da ya ƙunshi wani darasi ko ya cim ma wata manufa ta musamman cikin hikima (Zarruƙ, 1987: 11). A ganin wani masani, tatsuniya wani ƙagaggen labari ne da al’adar Hausawa ta tanada domin nishaɗantarwa da kuma cusa tarbiyya ga ‘ya’yan Hausawa (Yahaya, 1971: 5). Wata manazarciya ta bayar da ra’yinta game da tatsuniya inda ta nuna tatsuniya a matsayin wasu labarai da mutane ke ƙirƙirowa cikin azanci don su tarbiyyantar da ‘ya’yansu da kuma cim ma wasu buƙatoci dangane da al’umma (Koko, 2006: 4).

Duk idan aka tattara waɗannan ma’anoni na tatsuniya da Ƙamusun Hausa da kuma masana wannan fage suka bayar, za a iya daddagewa da cewa, tatsuniya labari ne ƙagagge da ake shiryawa domin ba yara da nufin yi musu tarbiyya musamman abin da ya shafi hani a kan abubuwan da al’umma ta ɗauka su ne gurɓatattu da horo a kan lamurran da al’umma ta aminta su ne kyawawa. Tastuniya tsohon labarin Hausawa ne da suke amfani da shi suna bayar da tarbiyya ga yaransu da nufin yaran su girma a cikin al’umma masu amfani ga kansu da iyayensu da ma al’ummar da suke rayuwa a cikinta. Tatsuniya tana da lokacin da al’adar Bahaushe ta ware na yin ta, wato da dare bayan yara sun ci abincin dare, musamman idan akwai farin wata. Muhallan tatsuniya ba su wuce gidajen tsofaffi mata ba. Ana yi wa yara a cikin gida inda kakanninsu ke yi musu. Ana kuma yin tatsuniya a dandali wurin wasa ko kuma ma a gidan sabuwar amaryar da takan gayyaci yara a gidanta don su ɗebe mata kewar iyaye da ƙawayenta da ta baro.

Mabuɗin tatsuniyar Hausa shi ne, “Ga ta nan, ga ta nan ku.” Marufinta kuma shi ne, “Ƙungurus kan kusu ko Ƙurunƙus kan kusu, ba don gizo ba, da na yi ƙarya, ko yanzu ƙarya ce na giggilla muku.” Akan ɗaure gizo kafin a yi tatsuniya da rana, ta hanyar ajiye tsakuwa ko sakaina a hanyar da mai tastuniya ya biyo ko zana da’ira a ƙasa. Idan ba a ɗaure shi ba, mai gabatarwa zai yi ciwon dundumi (Makantar dare) kokuma ɗemuwa ta kama shi. An raba tatsuniya gida biyu: Tatsuniyar Labari wadda ake zubo labari mai ɗauke da darussan zaman duniya da na rayuwa. Akwai kuma Tatsuniyar Almara wadda ake kawo wasu matsaloli guda biyu ko abin da ya fi biyu a buƙaci mai sauraro ya warware su cikin hikima. Akan kuma kawo wata sarƙaƙƙiya daga ƙarshe a buƙaci mai sauraro ya nuna idan shi ne lamarin ya shafa, yaya za ya yi?

 

4.0 Dangantakar Jigogin Wasu Labaran Magana Jari Ce Da Na Tatsuniyoyin Hausa   

 Dangantaka na nufin ‘yan’uwantaka (CNHN, 2006: 95). Idan aka ce dangantakar wasu labaran Magana Jari Ce da tatsuniyoyin Hausa ke nan ana nufin ‘yan’uwantakar wasu labaran Magana Jari Ce da tatsuniyoyin Hausa. Ke nan a wannan fasali, an bayyana kyakkyawar dangantaka da ‘yan’uwantaka da alaƙar da ke tsakanin labaran guda biyu. Kamar yadda aka bayyana a baya, ana ƙoƙarin a kawo wuraren da wasu labaran da ke cikin Magana Jari Ce I-III suka yi kama ainun da labaran tatsuniyoyin Hausa musammam ta fuskar saƙoƙnnin da duka labaran ke ɗauke da su. Akwai dangantaka tsakanin wasu labaran Magana Jari Ce da tatsuniyoyin Hausa ta fuskar saƙoƙnnin da duka labaran ke ɗauke da su. Akwai jigogi da dama da aka yi tarayya tsakanin Magana Jari Ce da tatsuniyoyin Hausa. Daga cikinsu akwai ladabi da biyayya da illar cin amana da kishi da jarunta da soyayya da adalcin shuwagabanni da wayon zaman duniya da illar bijire wa iyaye da raha da illar ruwan ido da dai sauransu.

 

4.1 Dangantaka ta Fuskar Jigon Ladabi da Biyayya

             Ladabi na nufin biyayya ko ƙasƙantar da kai (CNHN, 2006: 297). Yayin da biyayya ke nufin ladabi da bin na gaba (CNHN, 2006: 49). Shi ya sa kodayaushe kalmomin suke jingine da juna ake kuma amfani da su tare saboda kusancin ma’anoninsu a harshen Hausa. Ke nan ladabi da biyayya na nufin ƙasƙantar da kai ga wani mutum da yi masa biyayya ga kyawawan shawarwarinsa. Daga cikin jigogin da wasu labaran Magana Jari Ce da tatsuniyoyin Hausa suka yi tarayya a kansu akwai jigon ladabi da biyayya. A kwai labaran da suka zo da wannan jigo na ladabi da biyayya a cikin labaran Magana Jari Ce I-III da kuma tatsuniyoyin Hausa. A cikin Magana Jari Ce littafi na uku a labarin, “Mai Arziƙi Ko a Kwara Ya Sai Da Ruwa” an fito da wannan jigo inda aka nuna yadda Bawa yake yi wa mahaifiyarsa ladabi da biyayya. Saboda ladabinsa ne ya sa da mahaifiyarsa ta umurce shi ya tafi ya raka tsohuwa Inna don ya ɗaukar mata tafasarta ya kai mata har gidanta, bai yi musu ba, duk da kuwa cewa sun rigaya sun fara samun saɓani da aljana Inna saboda raina musu sana’a da ta yi da ta sunsuna musu tafasa:

 

Ɗebo mini ta sisin kwabo in tafi, amma don Allah ki sa ɗan-ɗan nawa ya ɗaukar mini ya raka ni da ita. Kin san ni yanzu ba na iya ɗaukar kome, ni ma kaina sai in da sanda nake iya tafiya.” Ko da jin haka, sai Bawa ya yi farat ya ce, “Wallahi Inna, in ba ta ɗauka sai ta bari, ba dominta kaɗai muka kawo ba. Ni dai ba na ɗaukar mata. Duk faɗin kan nan nata ta ce ba ta iya ɗaukar tafasar sisin kwabo, to, ina amfaninsa?” Uwar ta dubi tsohuwa, ta ga ranta ya ɓaci bisa ga wamnan magana, sai ta tsananta wa ɗanta dai ya tafi. Don ba ya son ya yi wani abin da zai ɓata wa iyayensa rai, sai ya tashi ya shige gaba, tsohuwa na bin sa, suka kama hanya tinƙis, tinƙis sai ka ce masu shiga ɗaki (Imam, 1940: 123).

 

Dubi yadda tsohuwar aljanar nan ta fusata Bawa, da yadda Bawa ya yi rantsuwa da Wallahi ba zai kai mata tafasa gida ba, amma saboda ladabi da biyayya ga mahaifiyarsa, sai dai ya haƙura ya tafi. A dalilin wannan rakiya da Bawa ya yi wa aljanna Inna da ta fito musu a matsayin tsohuwa, ya sa ta cuce shi ta sauya masa siffofinsa ta mai da shi tsoho mai doro da ƙusumbi. Da Irin wannan jigo ne aka yi amfani aka gina tatsuniyar Gizo da Sarki. Kamar yadda aka nuna a tatsuniyar, tsohuwa ba ta yi wa sarki gardama ba da Sarki ya buƙaci ta ba shi santa da ta turka. Duk da cewa ita ta turka abinta, amma da Gizo ya zo bara ya gan shi, sai ya tafi ya tsegunta wa Sarki, shi kuma sarki ya aika mata kawai ta kawo san nata, an ƙawace mata:

 

Sarki ya tura dogarai don a kamo kuma a kawo masa san. Da dogarai suka kama hanya ba su tsaya ko’ina ba sai gidan tsohuwa. Suka same ta, suka isar da saƙon Sarki. Da ta ji bayanin dogaran sai ta ce, “To yaya zan yi yanzu?” (Usman, 2012: 94).

  

Dalilin rashin yi masa gardama ya ta’allaƙa ne da ladabi da biyayyar da tsohuwa take nuna wa Sarki. Tabbas, da ba sarki ba ne ya nemi ya ƙwace mata sa ba, da ta yi mursisi kuma sai inda ƙarfinta ya ƙare. Ke nan an yi kunnen doki a labarin, “Mai Arziƙi Ko A Kwara Ya sai Da Ruwa” na cikin Magana Jari Ce III da kuma tatsuniyar Hausa ta “Gizo da Sarki” ta cikin Taskar tatsuniyoyi.

 

4.2 Dangantaka ta Fuskar Jigon Illar Cin Amana

Akwai alaƙa ƙwarai tsakanin Magana Jari Ce I-III da tatsuniyoyin Hausa ta fuskar jigon illar cin amana. A cikin wasu labaran Magana Jari Ce, an nuna cewa cin amana ba shi da wani amafani. Idan aka ce cin amana, ana nufin yaudadar wanda ya aminta da mutum. Idan aka aminta da wani, kuma ya yi yaudara, sai a ce ya yi zamba cikin aminci, wato dai ya ci amana ke nan. A cikin Magana Jari Ce littafi na uku. A cikin labarin, “Munafunci Dodo Yakan Ci Mai Shi,” an nuna yadda Sarki Sabitu ya amince da Maisango ƙwarai har ya saka shi cikin ‘ya’yansa kamar Sarki ya haife shi. Da yake Maisango maciyin amana ne, sai da ya yi ƙulle-ƙulle ya tura ‘ya’yan Sarki Sabitu suka haɗa kai suka kashe shi har lahira:

 

Ba a daɗe ba da yin wannan taɗi, sai aka ga kawai ran nan daga Sarki ya gama cin abinci sai ya yi ta murɗe-murɗe, cikinsa na ciwo. Kasuwa ta buɗe ga ‘yan bori, amma duk a banza, ciwo sai gaba-gaba yake yi (Imam, 1940: 67).

 

Kamar yadda aka nuna a labarin nan na sama, Maisangon da Sarki Sabitu ya tsinto ne ya haɗa baki da mai kai wa sarki abinci, aka zuba masa guba ya ci ya mutu. Ya yi haka ne saboda ya yi ƙulle-ƙullen da aka naɗa wanda yake so daga cikin ‘ya’yan Sarki don ya yi wa Maisango wata sarauta mai tsoka. Wannan ba ƙaramin cin amana ba ne, Sarki Sabitu ya taimaki Maisango ya ɗaukaka shi, amma shi Maisango ya yi dalilin halaka Sarki Sabitu.  Maisango bai tsaya nan ba, Bayan Sarki Sabitu ya rasu kuma, sai ya riƙa bi yana raba kawunan ‘ya’yansa, suka yi ta faɗa a tsakaninsu. A cikin tatsuniyar, “Talipaku da Kurciya” ma irin wannan saƙon ne aka aika da shi ga mai sauraro. An nuna yadda yadda Talipaku ta ci amanar Kurciya inda a matsayinsu na ƙawayen juna ta sace mata ‘ya ta gudu. Ita ‘yar Talipaku bakinta dogo ne ba ya barin ta ko ta ci abinci. Ita kuwa kurciya bakinta ɗan ƙarami ne madaidaici, shi ya sa take da kyau.

 

Shi ke nan, sai Talipaku ta yanke shawarar sace ‘yar Kurciya ta gudu da ita. Wata rana suna wurin neman abinci, sai Talipaku ta sulale ta je ta sace ‘yar Kurciya ta gudu da ita. Da Kurciya ta ɗaga kai ba ta ga Talipaku ba, kuma suna daf da tafiya gida, kuma ta nemi ƙawarta har ta gaji, sai ta dawo gida ita kaɗai. Da ta shiga sheƙa, sai ta ga ba ‘yarta, sa ɗiyar Talipaku. Sai ta fita ta kama cigiya. Sai aka ce mata an ga Talipaku ta ɗauki ‘yar Kurciya sun yi Yamma (Usman, 2012: 120).

 

Satar ‘yar ƙawarta da Talipaku ta yi cin amana ne, wanda daga ƙarshe sai da lamarin ya kai ta ga da-na-sani. Dalili kuwa, an nuna a tatsuniyar cewa, bayan da Kurciya ta gaji da neman Talipaku, sai ta tafi gidan Sarkin Tsuntsaye ta kai ƙara. Shi kuma ya sa dogarawa su tafi duk inda Talipaku ta shiga a kawo ta. Haka aka yi, suka gano ta suka zo da ita gaban Sarki. Shi kuma ya karɓi ‘yar Kurciya da Talipaku ta sace, ya mayar mata da abinta. Ya kuma miƙa wa talipaku ‘yarta da ta bari, ya kuma sa aka hukunta Talipaku hukunci mai tsanani a kan wannan cin amana da ta yi wa ƙawarta Kurciya. Ke nan da labarin, “Munafunci Dodo Ne Yakan Ci Mai Shi” na Magana Jari Ce III da tatsuniyar, “Talipaku da Kurciya” duka da jigo iri ɗaya aka saƙa su wato jigon illar cin amana.

 

4.3 Dangantaka ta Fuskar Jigon Kishi

Kishi na nufin rashin jituwa da nuna ƙyashi irin wanda matan da ke auren mutum ɗaya ke yi wa juna (CNHN, 2006: 247). Tsananin son da mace ke yi wa mijinta ko neman keɓancewa zuwa ga mijunta ko wanda take son ta aura da take nuna ƙauna da kyakkyawar fata gare shi tare kuma da nuna ƙiyayyarta ga duk wata da ke son sa da aure ko kuma shi yake son ta da aure, shi ne kishi (Bakura, 2014: 8-9).

Kishi yana cikin zuciyar kowace mata sai in akwai kawaici. A tsarin zamantakewar al’ummar Hausawa, kishi wani furen kallo ne a tsakanin mata. Da yake al’adar Hausawa da addinin Musulunci da aka san Hausawa da shi, sun aminta da auren mace fiye da ɗaya. Wannan dalili ne ya sa kishi ya zama wani lamari da ke ci wa matan Hausawa tuwo a ƙwarya. Su kuwa mazaje, rikice-rikicen kishi ba ya hana su auren mace fiye da ɗaya. Kishi jigo ne da ya haɗa wasu labaran Magana Jari Ce da tatsuniyoyin Hausa ya sarƙe. Misali a cikin labarin, “Yadda Muka Yi da Ubangijina Ojo” da ke cikin Magana Jari Ce littafi na farko, an fito da wannan jigo ƙarara. Mawallafin littafin Abubakar Imam ya nuna yadda wani tauraron labarin ya auro mata uku suna zaune gida ɗaya, sai kuma ya ƙaro wata matar suka zama huɗu:

 

Amma duk da haka, abin ya ba ka mamaki in ka ji na ce matarsa ɗaya ce tal. Da yana da uku, sai ya auro wata hatsabibiyar karuwa suka yi huɗu. Ko da karuwan nan ta shiga gidansa, sai ta tasar ma shiga bokaye da ‘yan bori don ta sami maganin da za ta kori sauran matan. Kwanci tashi ta ko samu (Imam, 1939: 53).

 

A nan, an nuna yadda Ojo ke da matansa uku. Duk da yake dai Ojo ba Bahaushe ba ne, kamar yadda aka nuna a labarin, shi Bayarabe ne, amma yana rayuwa a ƙasar Hausa. Al’adu da ɗabi’u da tsarin rayuwar Hausawa sun haɗiye nasa na Yarbawa, saboda haka, ya auri mata uku a lokaci ɗaya. An kuma nuna cewa ya ƙara auren wata hatsabibiyar karuwa a matsayin mata ta huɗu, wato dai ya kai maƙurar abin da addinin Musulunci ya tsara wa kowane namiji. Karuwa Ojo ya aura a matsayin mata ta huɗu kuma ya haɗa da ukun da yake da su. A ƙasar Hausa, an san yadda karuwa take da ƙulle-ƙullen makirci har ma dai idan ta sami nasarar shiga gidan kishiyoyi. Karuwa tana da tsananin kishi, kuma takan haɗa kishinta da bin malaman tsibbu da bokaye da ‘yan bori don ta kori sauran matan gida ta mallaki miji ita kaɗai.

            A cikin tatsuniyar, “Kaza da Gishiri” ma irin wannan jigo na kishi ne aka warware zaren labarin da shi. Gishiri ne dai ya auri Kaza suna zamansu. To, amma saboda gishiri ba ya son ruwa, narkewa yake yi, sai Kaza ta ce idan ta ga hadari ya taso alhali shi kuma yana gona, sai ta hau danga ta yi cara ta kira shi. Haka suka yi ta yi, har ya riƙa samun amfanin gona mai yawa. Suna cikin wadata da yalwa. Da ya ga sun fi ƙarfin kome, sai ya yi mata kishiya, inda ya auro tunkiya. Ita ma da ta zo gidan:

 

Ana nan sai damina ta kama. Gishiri ya kira matansa ya ce musu damina ta kama, don haka za a yi yadda aka saba. Sai Kaza ta ce za ta yi, amma sai ranar kwananta kawai za ta kira shi, ran kwanan Tunkiya ita za ta kira shi (Koko, 2009: 56).

 

Kaza ta nuna cewa, ba ta ji daɗin ƙara aure ko kishiyar nan da mijinta Gishiri ya yi mata ba. Duk macen da ta ji martanin da Kaza ta mayar ga mijinta da kishiyarta Tunkiya, ta san cewa akwai ɓacin rai da zafin kishi a zuciyar Kaza, saboda haka ta nuna ba za ta kira mijinsu ba, idan ba ranar girkinta ba ne. Akwai haɗari tattare da rashin kiran Gishiri da Kaza ta yi ranar girkin kishiyarta, domin ruwan sama zai bugi Gishiri ya narke ya mutu su duka su huta. Saboda zafin kishi ne ya sa ta ƙi kiran sa, kuma daga ƙarshe ya rasa ransa.

 

4.4 Dangantaka ta Fuskar Jigon Jarunta

Wani jigo da wasu labaran Magana Jari Ce da Tatsuniyoyin Hausa suka yi tarayya a kansa shi ne jigon jarunta. Juriyar wahala da ƙalubale wajen cim ma wani buri ita ce jarunta (CNHN, 2006: 214). A cikin labarin “Jimrau Ɗan Sarkin Noma na Biyu” da ke cikin Magana Jari Ce littafi na biyu, an nuna yadda Jumrau ya yi amfani da jarunta ya kashe dodanniyar da ke tare fatake tana kashe su ta ƙwace musu kaya. Jimrau ya cire fargaba ya tunkari gidan Dodanniya. Da ya yi sallama, Dodanniya ta fito sai ya yi ta-maza ya riƙa yi mata shaguɓe yana kambama ta. Ta nuna wa Jimrai tana iya rikiɗa ta koma dabbobi manya da ƙanana. Ta yi ta rikiɗa tana komawa dabbobi iri-iri, sai kawai ya ce mata:

 

“Ai wani abu sai mai shi. Yanzu kina iya rikiɗa ƙananan dabbobi kamar su ɓera ko? Dodanniya ta ce, “Af, ɓeran me kuma? An rikiɗa giwa balle ɓera?” Sai ta girgiza jikinta, ta zama ɓera. Da ganin ta zama ɓera, sai Jimrau ya yi farat ya saki kyanwarsa yadda yaron nan ya gaya masa. Ko da kyanwa ta ga ɓera, sai ta yi tsalle ta kama shi ta kashe ta cinye. Ko da ta cinye Dodanniya, sai ya ji gidan ya ɗauka, “Haa! Jimrau ka yi nasara, babu kuskure, ka yi nasara (Imam, 1940: 43).

 

Jaruntar da Jimrau ya nuna a wannan gaɓa ita ce yadda Jimrau ya tunkari gidan Dodanniya ya yi ido-da-ido har suka yi zance na raha a tsakaninsu. Haka kuma, bai ji tsoron cewa Dodanniya ta gane cewa akwai mage tare da shi ba, ganin cewa za ta iya gane haka, saboda ita ba mutum ba ce. Yin farat da Jimrau ya yi ya saki kyanwar da ke cikin jikinsa ma wani nau’i ne na jarunta. Domin da ya yi fargabar sakin kyanwa, to da Dodanniya ta gama rikiɗe-rikiɗenta, sai ta yi kansa ta kuma halaka shi har lahira. A cikin Tatsuniyar, “Sarkin Maƙera da Dodo” ma irin wannan jigo ne na jarunta aka gina ta da shi. A cikin tatsuniyar an nuna yadda babban tauraron tatsuniyar wato Fugo Sarkin Maƙera ya nuna jarunta wajen kisan Dodon da ya tare ƙanwarsa za ya cinye ta a cikin daji. Abin da ya faru shi ne, ƙanwar Sarkin Maƙera Fugo ne mahaifiyarsu ta rasu. Ta yi nufin ta tafi wajen zaman makoki. A kan hanyarta, sai Dodo ya tare ta zai cinye. Da ta ga lamarin ba girma, sai ta haye kan wata bishiya. Tana nan zaune Dodo na ƙasan bishiyar yana jira ta sauko ya cinye ta, sai ga Kurciya, sai ta ruga garin su Fugo Sarkin Maƙera ta shaida masa abin da ke faruwa. Ko da Fugo ya zo sai:

Ya zaro kibiya ya ɗirka wa Dodon nan. Kafin ya farka ya farka, sai da Fugo ya yi masa ruwan kibau kamar ashirin. Da ya farka kafin ya wartsake, Fugo ya jefa masa masu kamar guda tara. Amma duk da haka, da ya wartsake sai aka ji yana cewa: “Kai wane cinnaka ne yake damuna?” Shi kuwa Fugo sai ya zaro wasu kibau masu dafi ya dinga ɗana su yana sakar wa Dodo ɗaya bayan ɗaya a idonsa na dama, nan take idonsa ya tsiyaye. Kafin ya san abin da ake ciki, Fugo ya sake auna ɗaya idon, kuma ba kuskure ya same shi. Shi ma nan take ya tsiyaye. Dodo ya zama ba ya iya gani. Tuni dafin kibiyar ya bi jikin Dodo, har ya zamanto ba zai iya tashi ba. Sai Fugo ya ce da Awa ta sauko (Usman, 2012: 194).

 

Abin da mai karatu zai gamu da shi a cikin wannan bayani na samu shi ne, tsananin jaruntar da Fugo Sarkin Maƙera ya nuna wajen ceto ƙanwarsa daga hannun Dodo. Dodo ya yi niyyar ya halaka Awa, amma da yake Awa na da Jarumin ɗan’uwa wato Gugo, sai ga shi ya tseratar da ita daga zaluncin Dodo. Kamar yadda aka gani a cikin bayanin, Fugo ya yi amfani da ƙarfi da salon harbi da juriya da rashin fargaba da jajircewa da ƙarfin hali ya kashe Dodo. Wannan namijin ƙoƙari d Fugo ya yi, ba ƙaramar jarunta ba ce. Don haka, yadda ake samun wasu labaran Magana Jari Ce I-III na zuwa da jigon jarunta, haka ake samun tatsuniyoyin Hausa su ma suke zuwa da jigon jarunta.        

 

4.5 Dangantaka Ta Fuskar Jigon Soyayya

            Soyayya gamon jinni. Soyayya ruwan zuma, in an sha a ba masoyi. Waɗannan duk kirare-kiraren da Hausawa ke yi wa soyayya ne. Bayan haka, Nuna ƙauna daga ɓangarori biyu na masu ƙaunar juna, musamman mace da namiji shi ne soyayya (CNHN, 2006: 398). Soyayya babban jigo ne na wasu labaran Magana Jari Ce I-III da Tatsuniyoyin Hausa suka yi tarayya a kansa. Da jigon soyayya ne aka bayar da labarin, “Sauri Ya Haifi Nawa” na cikin Magana Jari Ce littafi na farko. An fito da soyayyar da ta ƙullu tsakanin Nana Yauƙi da ɗan Sarki. Sarki ya tafi rangadi tare da ɗansa, har Allah Ya kai su garin su Nana. Lokacin da ya ga Nana, sai soyayyarta ta kama shi:

 

...Ya taƙale ta da maganar aure, ya ga alamar lalle tana son sa. Wancan mijin da za a ba ta, wai dattijo ne mai gemu. Ita kuwa ta ce ba ta auren mai gemu. Bayan sun shirya da ita a nan sai ta tafi. Ya ɗauki buta a masallaci ya yi alwala, ya shiga ya yi salla. Da yai sallama, ya yi addu’a ga Fiyayyen Taliki ya nufa Allah Ya sa ya auri wannan yarinya. Don ɗokin buƙatar auren yarinyar nan har ya yi suɓul da baka ya ce wai in Allah Ya nufa ya aure ta ya kashe kansa don murna (Imam, 1939: 117).

 

Haka nan ma a cikin tatsuniyar, “Marainiya” ma, babban jigonta shi ne soyayya. An fito da soyayyar da ta ƙullu tsakanin Aminu ɗan sarki, da wata yarinya marainiya wadda iyayenta suka rasu. Bayan iyayenta sun mutu, sai kishiyar uwarta ta riƙa ƙuntata mata, saboda haka, sai ta tafi daji ƙarƙashin wata bishiyar kurna ta zauna tana kuka tana tunani. Akwai wani ɗan sarki mai suna Aminu da yakan zo kullum ya hau kan bishiyar kurnan nan ya sha iska da yamma. Kullum yana ganin ta bai taɓa yi mata magana ba, sai ran nan dai Aminu ya gan ta a wurin:

 

Aminu ya ce, “Me ke damun ki ne? Kullum sai in zo in gan ki a gindin wannan bishiya, har ma domin tunanin da kike yi ba ki sanin zuwana, kuma ga shi kikan riga ni zuwa don ni sai da la’asar nake zuwa, har in hau bishiya ba ki gan ni b a. “To yaya kake zama a kan bishiyar Kurna mai ƙaya?” Ta tambaye shi. Sai ya ce: “Ni na san dabarar da nake yi.” Haka dai suka ci gaba da hirarsu har ya kawo ga maganar aure. Sai ta ce, “Ni marainiya ce, ban da uwa, ba ni da uba.” Sai ɗan sarki ya Aminu ya ce: “Yau na zama uba da uwa a wurinki.” (Usman, 20126-7).

 

Idan aka lura da waɗannan bayanai na sama, za a iya ganin kyakkyawar dangantaka ta fuskar jigon soyayya tsakanin labarin, “Sauri Ya Haifi Nawa” na cikin littafin Magana Jari Ce II, da kuma tatsuniyar Marainiya. An nuna yadda soyayya ta yi ƙarfi tsakanin Nana Yauƙi da ɗan sarki na cikin Magana Jari Ce II da kuma soyayya mai danƙo tsakanin Marainiya da Aminu ɗan sarki. Tabbas akwai alaƙa tsakaninsu. Aalaƙar ta farko ta jigon soyayya da aka gina duka labaran da ita, sai kuma yadda samarin suka zama ‘ya’yan sarki su kuma ‘yanmatan suka zama ‘ya’yan talakawa. Haka kuma, duka masoyan sun sami damar cim ma gurinsu na auren juna. 

 

4.6 Dangantaka ta Fuskar Jigon Adalcin Shuwagabanni

Adalci yana nufin tausayawa ko yin hukunci bisa gaskiya ko rangwantawa (CNHN, 2006: 2). Yayin da shugaba a ɗaya ɓangaren, yake nufin jagora ko jagaba wanda ya ɗauki nauyin jan ragamar jama’a ko wata ƙungiya ta mutane (CNHN, 2006: 415). Shugaba guda ɗaya ke nan ko mace ko namiji, yayin da jam’in kalmar akan ce, “Shuwagabanni.” Akwai kyakkyawar dangantaka tsakanin wasu labaran Magana Jari Ce I-III da tatsuniyoyin Hausa dangane da jigon adalcin shuwagabanni. A “Labarin Annabi Sualaimanu” na cikin Magana Jari Ce littafi na farko, an nuna yadda wasu mata suka zo wajen Annabi Sulaimanu domin ya yi musu hukunci da adalci a kan matsalar da ta shiga tsakaninsu.

Waɗannan mata gida ɗaya ɗaya suke kuma sun haihu, kowace tana goyon jariri. Sai ɗaya ta kwanta a kan ɗanta ba ta sani ba, tana cikin barci. Da ta farka ta ga abin da ke faruwa, sai ta tashi ta yi wa ‘yar’uwarta musayar ɗa, ta ajiye mata gawa, ita kuma ta ɗauki mai rai, sai gardama ta sarƙe tsakaninsu, kowace na cewa, mai ran ce tata:

 

Da Annabi Sualaimanu ya ji maganar matan nan, sai ya sa aka ɗauko takobi aka zare, ya ce, “Tun da yake abin ya rikice haka, abu ɗaya kaɗai za a yi a raba gardamar nan. Zan raba ɗan nan biyu, kowacenku ta ɗauki rabi kowa ya huta, ku dangana har Allah Ya sake ba ku waɗansu. Da mace ɗaya ta ji haka, sai ta ce, “Don Allah kada a kashe shi. A ba ta na yarda mata.” Amma waccan ta ce, “A’a daidai ne, ya Annabi. A dai raba shi kowa ya huta.” Da Annabi Sulaimanu ya ji haka, sai ya ce, “Ku miƙa ɗan nan mai rai ga waccan da ta ce kada a kashe shi. Ɗanta ne ita ta haife shi.” (Imam, 1939: 94).

 

Tatsuniyoyin Hausa ma kan zo da irin wannan jigo na Adalcin Shuwagabanni. Dubi abin da ya faru a cikin tatsuniyar, “Talipaku da Kur4rciya.” Sheƙa ɗaya Talipaku da Kurciya suka yi ƙwayayensu suka ƙyanƙyashe. Zuriyar su Talipaku da dogon baki suke haihuwar ‘ya’yansu. Su kuma zuriyar su Kurciya da ɗan ƙaramin baki mai kyau ake ƙyanƙyashe su. Ashe wannan lamari ya dami Talipaku ganin ba mai son ɗaukar ‘yarta ya taya ta raino, saboda dogon bakin da ‘yarta ke da shi. Ita kuwa kurciya kowa sai son ɗaukar ‘yarta yake yi, saboda bakinta ɗan ƙarami mai kyawu. Hassada ta turnuƙe Talipaku, saboda haka, sai da ta bari sun fita neman abinci da ita da Kurciya, sai Talipaku ta yi waiwai-da-baya ta dawo gida ta sace ‘yar Talipaku ta fice da ita ta bar wa Talipaku ‘yarta mai babban baki. Da Kurciya ta dawo ta ga abin da ya faru, sai ta fita neman Talipaku don ta karɓi ‘yarta, ita kuma ta ba ta tata. Tana ta cigiya, sai aka ce mata an ga Talipaku da ‘yarta sun yi Yamma. Ko da Kurciya ta tabbatar da zargin da take yi, sai ta garzaya gidan Sarkin Tsuntsaye ta shigar da ƙara:

 

Sai Sarkin ya sa aka ƙwace ‘yar Kurciya aka ba ta ‘yarta. Ita ma Talipaku aka ba ta ‘yarta. Sarkin Tsuntsaye ya ja kunnen Talipaku da kada ta kuskura ta sake satar ‘yar wani tsuntsu. Idan kuwa aka sake kawo ta ƙarar ta, to, za a kashe ta. Sai aka sallame su. Kurciya ta ɗauki ‘yarta. Ta yi godiya ta tafi. Ita kuma Talipaku ta tafi da ‘yarta (Usman, 2012: 121).

 

Akwai dangantaka sosai dangane da saƙon adalcin shuwagabanni da aka isar a cikin labaran nan guda biyu: “Labarin Annabi Sulaimanu” da kuma tatsuniyar “Talipaku da Kurciya.” Duka shuwagabannin cikin labaran biyu: Annabi Sulaimanu da Sarkin Tsuntsaye sun yi hukunci da gaskiya. Hukunci da gaskiya ga masu jayayya ko mai laifi shi ne adalci. Akan nusar da shuwagabanni a kan yin adalci cikin hukunci ta hanyar rubuta ƙagaggen labarin Hausa kamar Magana Jari Ce da kuma tatsuniyar Hausa kamar tatsuniyar Talipaku da Kurciya.

 

4.7 Dangantaka ta Fuskar Jigon Wayon Zaman Duniya     

Wayo na nufin dabara ko cuta (CNHN, 2006: 472). Tun da wayo dabara ce, ke nan idan aka ce “Wayon zaman duniya,” ana nufin dabarar zaman dauniya. Babban jigo ne da masu bayar da labari ke amfani da shi. An kuma samu dangantaka mai danƙo tsakanin wasu labaran Magana Jari Ce da tatsuniyoyin Hausa. A cikin “Labarin Kyanwa da Ɓera” da ke cikin Magana Jari Ce littafi na farko, an warware irin wannan jigo. A cikin labarin an nuna yadda ɓera yake da wayon zaman duniya, inda ya nuna dabara daban-daban wajen cinye igiyar ragar tarkon da ta kama muzuru. Tarkon mai gona ne ya kama muzuru. A ɗaya ɓangare kuma, ɓera ya ga maciji da shirwa a wurin. Ɓera ya san ba su jituwa da shi. Ɓera ya yi amfani da wayon zaman duniya inda ya yi shawarar cinye igiyar ragar da ta kama muzuru:

 

Ɓera kuwa da ya waiga ya ga tarko ya kame muzuru, sai ya yi rawa yana murna. Yana nan yana murna, ya duba haka cikin kara kusa da raminsa, sai ga wani maciji nan yana jira ya rabo da muzuru ya haɗiye shi. Ya duba sama don ya hau, sai ya ga shirwa na kewaya tana jira ya motsa ta fyauce shi. Abu ya zama masa gaba siyaki baya damisa. Yana nan sai ya tuna da wata dabara, ya ce, “Na san dai da maciji da shirwa ba mai iya zuwa kusa da muzuru. Yanzu ba abin da ya fi sai in je wajen muzuru in ce ya rantse ba zai sake cuta ta ba, ni ko in cinye igiyar ragar nan in sake shi” (Imam, 1939: 44).

 

Wannan tunani na neman kuɓutar da rayuwa da ɓera ya yi, wayo ne na zaman duniya. Da bai yi wannan tunani ba, da ya rasa ransa, domin maciji ko shirwa za su halaka shi. Dubi yadda ɓera ya yi nazarin mummunar dangantakar da ke akwai tsakanin maciji da shirwa da muzuru, wadda a kanta ne ya shirya yadda zai haɗa su wuri guda, shi kuma ya kuɓuta. Wayo wani lokaci yana nufin cuta ko yaudara kamar yadda (CNHN, 2006) ya nuna. Ta wannan fuska, muzuru ya cuci ɓera, ya kuma yaudare shi Domin bayan sun ƙulla abota, sai suka shirya haɗa kayan abincinsu wuri ɗaya, da yarjejeniyar cewa, ba za su fara amfani da su ba, sai lokacin hunturu. Ko da aka kwana biyu, sai Muzuru ya yi wa ɓera ƙaryar an gayyace shi taron suna, sai ɓera ya ce da shi kada ya manta da shi ga kayan suna:

 

Muzuru ya ce, “Haba, in na manta da kai, in tuna da wa?” Ya nufi gari. Da ma ƙarya yake yi, ba wanda ya gayyace shi suna, wajen ajiyarsu yake so ya je ya ci. Da ya ci ya ƙoshi, sai ya sami wuri ya kwanta yana lasar gashi, yana gurnani. Can da rana ta yi sai ya komo (Imam, 1949: 47).

 

Wannan jigo na wayon yaudara da cuta shi ne aka warware a cikin wannan bayani na sama. Kamar yadda ake gani, muzuru ya cuci ɓera ta hanyar yaudararsa yana sulalawa yana cinye musu kayan abincinsu da ba shi kaɗai ya tara su ba. Duk lokacin da ya je ya ci, sai ya dawo ya yi wa Ɓera ƙarya, har ya faɗa masa sunan jariri wanda sunan ke aika saƙon shaguɓe da habaicin cutar da ya yi wa masa. Ta fuskar wannan jigo ne kuma aka samu kamanceceniya da tatsuniyar Hausa ta, “Ƙawancen Kyanwa da Ɓera.” A cikin wannan tatsuniya ma Ɓera ne ya yaudari kyanwa, yana zuwa yana cinye kayan abincin da suka yi tanaji sai lokacin hunturu su yi amfani da shi. Ya riƙa yi wa Kyanwa ƙaryar an gayyace shi ne wajen bikin ƙanwarsa:

 

Suna nan, ran nan Ɓera ya ce da Kyanwa zai je bikin ƙanwarsa. Da ya fita sai ya nufi rumbun abincin da suka tara, ya ci har sai ya da ya ƙoshi. Da ya dawo gida sai Kyanwa ta yi masa maraba, ta tambaye shi, “Me aka samu ne?” Ɓera ya dubi Kyanwa ya ce, “Abin da aka samu shi ne Wuyar Aikin Ba a Fara Ba.” (Usman, 2012: 69).

 

Idan aka lura, za a ga cewa akwai kyakkyawar alaƙa tsakanin “Labarin Kyanwa da Ɓera” da ke cikin Magana Jari Ce littafi na farko da kuma tatsuniyar, “Ƙawancen Kyanwa da Ɓera.” Labarin iri ɗaya ne, sai dai wajen ruwayar labaran ne aka samu bambanci. A cikin Magana Jari Ce, an nuna cewa Muzuru ne ya cuci Ɓera, yayin da cikin tatsuniyar “Ƙawancen Kyanwa da Ɓera” kuma sai aka sauya lamarin aka nuna Ɓera ne ya yi wa Kyanwa Wayon cuta da yaudara, amma dai jigon na wayon cuta da yaudara, iri ɗaya ne bai sauya ba.  

 

4.8 Dangantaka ta Fuskar Jigon Illar Bijire wa Iyaye

            Bijirewa na nufin kangarewa (CNHN, 2006: 46). Yayin da Kalmar “Iyaye” ke nufin uwa da uba (CNHN, 2006: 209). Bijire wa iyaye wato kangare wa koyarwarsu a al’adar Bahaushe da addininsa illa ace babba. Masu ba da labari kan ɗauki wannan lamari a matsayin jigo na musamman da suke isarwa ga jama’a a cikin labaransu. A cikin labarin, “Babban Mugun Abu Ɗa Ya Yi Hushi da Iyayensa” na cikin Magana Jari Ce littafi na farko, an nuna yadda wani yaro ɗan makarantar boko wai shi Ilu ya bijire wa iyayensa kawai don sun yi masa faɗa a kan ya ƙara mai da hankali a kan karatunsa, saboda sakamakon jarabawarsa bai yi kyau ba. Kawai sai:

 

Yaro ya tashi yana ta hushi, wai uban ya ce in bai yi ƙoƙari ba, zai ba da shi ga mahauta ya je ya yi tallar tsire. Ya koma ƙaramin zauren gidan ya zauna. Yana nan yana ciccika, lokacin cin abinci ya yi, ƙanensa Ibrahim ya zo ya kira shi su je su ci. Sai Ilu ya dube shi da hushi ya ce, “Je ka ci, ni ban ci!” Ibrahim ya bushe da dariya, ya ce, “Kana tsammani wani ya kula don ba ka ci abinci ba. Je ka huta.” (Imam, 1939: 75).

 

Fushin da Ilu yake yi da iyayensa wani ɓangare ne na bijire musu. Ba sa son ɗabi’ar da yake yi ta fushi da yajin cin abinci kwana da kwanaki. Sun yi, sun yi ya daina fushin amma ya kangare musu. Ya riƙa ɗaukar kayansa na sawa yana kai wa kasuwa yana sayarwa yana cin abinci ba su sani ba. Da Allah Ya tsahi kama Ilu, sai da ya sayar da kayan, ya nufi tukubar mai nama, ya saya ya ci, ya sha ruwa ya dawo gida. Ya kwanta ke nan yana ta fushi, sai cikinsa ya kama ciwo, ya yi ta amai yana fitar da naman nan, ya galabaita matuƙa. Iyayen nasa da yake fushi da su, su dai ne suka tarairaye shi, suka nema masa magani ya warke. Daga baya ya yi nadama. Irin wannan jigo ne aka yi amfani da shi aka gina “Tatsuniyar Wani Yaro Mai Taurin Kai” da shi. Wani yaro ne da ba a ambaci sunansa ba, ya zama mai taurin kai da bijire wa iyayensa:

 

Wata rana wannan yaro ya je gona da iyayensa. Bayan sun yini suna aiki sai suka koma gida da rana ta faɗi. Da tsakar dare sai yaron nan ya tuna da cewa ya manta mabusarsa a gona. Ya ta da iyayensa daga barci ya gaya musu cewa zai je gona ya ɗauko mabusarsa da ya manta a can. Iyayensa suka roƙe shi da kada ya je, ya bari har safiya ta waye, amma ina! Kafin ma su ƙare magana, har yaron nan ya yi nisa da tafiya cikin duhun dare ya nufi gona (Koko, 2009: 44).

 

Dubi yadda yaron nan ya kangare wa iyayensa ya nufi gona ɗaukar mabusarsa da ya manto. Ga shi kuma dare ya yi sosai. Wannan bijirewa da kangarewa da ma taurin kan da ya yi wa iyayen ne suka sa ya haɗu da aljannu a gonar inda suka azabtar da shi ta hanyar tursasa masa ya riƙa yi musu busa suna rawa. Da ƙyar wannan yaro ya kuɓuta. Wannan wahala da ya sha a hannun aljannu ce ta sa ya zama yaron kirki, ya yi nadamar laifukan da ya yi wa iyayensa. Ke nan an sami kyakkyawar dangantaka tsakanin labarin, “Babban Mugun Abu ga Ɗa Ya Yi Fushi da Iyayensa” na cikin Magana Jari Ce littafi na farko da “Tatsuniyar Wani Yaro Mai Taurin Kai” ta fuskar jigon illar bijire wa iyaye.

 

4.9 Dangantaka ta Fuskar Jigon Raha

            Akwai dangantaka mai ƙarfi tsakanin wasu labaran Magan Jari Ce da tatsuniyoyin Hausa ta fuskar raha. Walwala ko fara’a ita ce raha (CNHN, 2006: 364). Babban jigo ne da masu bayar da labari ke laɓewa bayansa wajen isar da saƙonnin labaransu ga jama’a. Raha a cikin labari, ta ƙunshi kawo wata gaɓa mai sa nishaɗi da ban dariya ga mai sauraro ko karatun labari. A cikin labarin, “Sahoro da Sahorama” na cikin Magana Jari Ce littafi na farko, mawallafin ya kawo wata kokawa da ta kaure tsakanin miji (Sahoro) da mata (Sahorama) mai ban dariya. Sahorama dai ce take tsaye a tsakiyar ɗakinta inda mijinta Sahoro ke kwance yana hutawa. Labari ya kawo inda Sahorama take nuna yadda za ta yi wa almajirin da za su ɗauko ya riƙa yi musu kiwon awaki da tata da ta mijin. Lamarin ƙaddara, sai ta buge goron zumar da ta rage musu da sanda. Gora ya fashe ya malale ƙasa. Sahorama ta duƙa tana kwasa da hannu tana zuwa rabi cikin gora, rabi kuma tana shanyewa. Wannan hali na Sahorama ya kufula mijinta Sahorami, saboda haka sai ya tsawata mata. Ai sai Sahorama ta ce, “Ina wuta ta jefa shi?” Kai! Har da dai su zagi. To, a wannan gaɓar ne Sahorami ya ce, “Ni kika zaga?: ”

 

Sahorama ta ce, “An je an zage ka, kai dai ne Kafiri ba ni ba. In kai ɗa ne, ba shege ba, ka gina rami ka tsattsage ni!” Sai zuciya ta turniƙe Sahoro, ya tashi daga kwance ya sauko ya tarar da matar, sai kokowa kicici-kicici, kica-kica. Can Sahoro ya gaji ya ga bai kada matar ba, sai ita ke neman tandara shi da ƙasa, sai ya ce mata, “To sakar ni kin kayar. Na ce ko iyakarta ke nan?” Sahorama ta ce, “Af! in sake ka ni in faɗi?” (Imam, 1939: 31).

 

Akwai lamurran da ke sa raha a cikin wannan kokawa da ta kaure tsakanin Sahoro da Sahorama. A matsayinsa na namiji, Sahoro ya kamata a ce ya ci galabar Sahorama ya ka da ita. Sai ga shi ana zaton wuta a maƙera, an same ta masaƙa. Sahorama ta ɗaga Sahorami sama za ta kayar. Ga shi Sahorami ya saduda har ya yi raki, yana cewa Sahorama ta sauke shi ƙasa ya saduda. Abin ban dariya, ashe ita kuma ba ta kama ƙasa ba, ta dogara da ƙafar Sahorami guda ɗaya da ta rage a kan ƙasa, da ya faɗi, ita ma za ta faɗi. Ba ta yi nauyin baki ba, sai ta sanar da abokin kokawar halin da take ciki. Banza ta kori wofi. Irin wannan jigo na raha ne aka yi amfani da shi aka gina tatsuniyar, “Lolloda.” A tatsuniyar, an bayyana yadda tsohuwa ta tsinci wani ƙashi mai magana. Da ta tambaye shi sunansa, sai ya ce mata Lolloda. Ta yi tunani mai kyau ta sake tambayar sa me yake yi? Ƙashi ya ce mata shi “Zuzzuba” ne aikinsa. Tsohuwa kuwa ta ce ya zuzzuba. Da ya dinga zuzzuba mata kuɗi, sai da ta kasa ɗauka.

Abin ƙaddara, sai Sarki ya ji labarin yadda tsohuwa ta yi arziƙi. Ya kuma ji labarin arziƙin tsohuwa sanadiyyar wani ƙashi ne mai Magana, saboda haka ya aika wa tsohuwa ta yi gaugawar kawo ƙashin nan. Ba ta yi gardama ba ta kawo masa, don haɗama irin ta Saraki:

 

Sai ya ce a rufe shi tare da ƙashin kuma ko me aka ji, a ƙyale shi kada a buɗe. Aka rufe sarki, sarki ya ci gaba da kiran Lolloda, ƙashi na ta loda masa bugu ga kai yana ta kuwa. Kowa ya ƙyale shi. Sai da ya sha kashi sosai sannan aka buɗe shi duk kansa ya kumbura (Koko, 2009: 79).

 

Kamar yadda aka sha dariya a cikin labarin “Sahoro da Sahorama” na cikin Magana Jari Ce littafi na farko, haka ita wannan tatsuniya take ba mai sauraro ko karatu dariya. Abin dariya a wannan bayani da aka ciro daga tatsuniyar Lolloda da ke sama shi ne, yadda Sarki ya ƙwace wa tsohuwa ƙashi don zalunci. Saboda garajen ya sami kuɗi bai tambayi tsohuwa kalmar da ake faɗa wa ƙashi ya yi aman kuɗi ba. Domin wauta irin ta Sarki ma, sai ya ce a rufe shi cikin ɗaki tare da ƙashi domin ba ya son wani ya sami ko ɗari daga kuɗin da ƙashi zai amayar masa. Yadda Lolloda ya riƙa loda wa Sarki bugu cikin ɗaki yana raki, shi ma abin dariya ne kuma zai sa mai sauraro ko karatu raha. Wani abin da zai ƙara ba da dariya cikin tatsuniyar shi ne yadda aka fito da sarki daga ɗakin nan, duk ƙashi ya saɓa masa kamannu. Saboda haka, dangane da jigon raha, tabbas akwai kyakkyawar dangantaka tsakanin wasu labaran Magana Jari Ce da tatsuniyoyin Hausa.  

 

 

 

4.10 Dangantaka ta Fuskar Jigon Illar Ruwan Ido

   Idan aka ce, “Ruwan ido” ana nufin rashin tsai da rai a wajen zaɓen abu (CNHN, 2006: 377). Ruwan ido ɗabi’a ce mai illa a tsarin zamantakewar Bahaushe. Mutum mai ruwan ido ma, Hausawa na kallonsa a matsayin mutum marar nagarta da son abin duniya. Illar ruwan ido babbar jigo ne ga masu ba da labarin Hausa. Ana kuma samun dangantaka tsakanin wasu labaran Magana Jari Ce I-III da kuma tatsuniyoyin Hausa ta fuskar jigon illar ruwan ido. A cikin labarin, “Wanda Ke Wulaƙanta Jama’a Duk ya Ga Iyakarsa” na cikin Magana Jari Ce littafi na Uku. Labarin wata ‘yar sarki ce mai suna Mama aka bayar. Mama ta kasa zaɓen wanda za ta aura, duk da cewa ta girma sosai ta isa a yi mata aure. Ga yadda aka nuna a labarin duk tsararrakinta ma sun haihu. Lamarin ya dami mahaifinta Sarki, saboda                                                                                                                 kowa ya je nemanta sai kushe shi, sai wani aljani daga zuriyar Ƙurungu Sarkin Kawuna, waɗanda halittarsu kai ne kawai babu gangar jiki ya ji labari. Ya kuwa aiko wata tsohuwa da ta tambaya masa izni. Amsa kuwa ta yi daidai, Sarki ya yi murna ya buƙaci tsohuwa ta kawo ango fada a gan shi. Ko da tsohuwa ta shaida wa Ƙurungu buƙatar Sarki:

 

Kai ya ce, “Ba kome, sa ni cikin tasa ki kai ni.” Tsohuwa ta sa shi cikin tasa, ta ɗauka ta kai gaban Sarki duk jikinta na rawa. Ta ajiye, ta ce, “Allah Ya baka nasara, ga ɗan nawa.” Sarki ya ja kujera baya, fadawa kowa ya ja da baya. Sarki ya ce, “Me zan gani haka? Har abada ba na aurar da Mama ga wannan dodo. Ku kira Mama ta ga abin da ruwan idonta ya jawo mana.” (Imam, 1940: 40).

 

Illar ruwan ido ce ta sa Mama, babbar tauraruwar labarin, “Wanda Ke Wulaƙanta jama’a Duk Ya Ga Iyakarsa” ta auri dodo. Domin a nuna a ƙarshen labarin cewa Mama ta tare gidan Kai babu yadda ta iya. Domin zuriyar Ƙurungu sun yi alƙawarin cewa idan ba a ba su matarsu ba, za su saka al’ummar gari cikin bala’i. da Mama ba ta yi ruwan ido wajen zaɓen ɗaya daga cikin ‘ya’yan sarakunan da Sarki ya tara mata ba, da ba ta shiga wannan matsala ba. Da irin wannan jigo na illar ruwan ido aka warware tatsuniyar, “Budurwa Marar Tabo.” A cikin tatsuniyar, an nuna yadda wata budurwa marar tabo ta sha alwashin auren saurayi marar tabo. Wannan alwashi nata ne ya kai ta ga ruwan ido wajen zaɓen mijin da za ta aura. Duk saurayin da ya zo neman aurenta, sai budurwar nan ta sa ya cire kayansa ta dudduba jikinsa, ko ga yatsa ta ga tabo, kome ƙanƙantarsa, sai ta hau kujerar na-ƙi, ta ce ta fasa auren.

            Ana nan, ana nan, sai wasu aljannun macizai suka ji labarin wannan cin mutunci da budurwar nan take yi wa maza, sai suka yi alƙawarin yi wa tufƙar hanci. Macizan suka rikiɗa suka zama samari santala-santala, jikin nan nasu sumul, suka tafi domin budurwar nan ta yi musu jarabawa. Da ta dudduba jikinsu, sai ta ga babu tabo ko ɗaya a jikinsu, saboda haka ta aminta za ta auri ɗaya daga cikinsu. Aka kuwa ɗaura aure:  

 

Shi ken an, ta tattara kayanta suka tafi da amaryarsu. Da suka je jeji sai suka ce, “Yawwa mun iso gida.” Ita ko ta ce, “Ina gidan a nan?” Sai suka ce da ita, “Ai nan ne gidan.” Amarya ta yi zuru-zuru babu yadda za ta yi domin ta riga ta auri ɗayansu, kuma ga shi sun kai ta dokar daji inda ba za ta iya komawa gari ba. Daga nan sai suka saka ta a kogon bishiya, suka rikiɗe macizai suna lasar jikinta har ta zama fara fat, babu kyan gani kuma abin ƙyama (Usman, 2012: 20).

 

Kamar yadda yadda Mama ta cikin labarin, “Wanda Ke Wulaƙanta Jama’a Duk Ya Ga Iyakarsa” ta tsaya ruwan ido wajen zaɓar miji, daga ƙarshe ta auri Aljani kuma kai babu gangar jiki, haka ita ma wannan budurwa, babbar tauraruwar tatsuniyar “Budurwa Marar Tabo” ta yi ruwan ido wajen zaɓen nata mijin aure, daga ƙarshe ita ma ta auri macijin aljani. Ke nan, an sami dangantakar jigon ruwan ido tsakanin labarin cikin Magana Jari Ce da tatsuniyar Hausa.     

 

4.11 Sakamakon Bincike

Bayan an ƙare wannan bincike, sai aka gane cewa, wasu daga cikin labaran da aka gina Magana Jari Ce I-III da su, tushensu daga tatsuniyoyin Hausa ne musamman ta fuskar jigo. Da yake jigogin rubutattun labaran Hausa da na tatsuniyoyin Hausa suna da alaƙa ƙwarai, sai ma aka gane cewa Abubakar Imam, mawallafin Magana Jari Ce I-III, ya tasirantu matuƙa da tatsuniyoyin Hausa, wato ya ji su daga bakin magabata, shi ya sa ya yi wa wasu kwaskwarima ya sake mayar da su cikin rubutaccen labarinsa na Magana Jari Ce. Dubi “Labarin Kyanwa da Ɓera” na Magana Jari Ce I, da kuma “Ƙawancen Kyanwa da Bera” na tatsuniyar Hausa, a gaskiya tatsuniyar ce Abubakar Imam ya yi wa baddala ta hikima. Taken labaran iri ɗaya ne, taurarin labaran iri ɗaya ne kuma jigon labaran ma iri ɗaya ne.

Haka kuma, irin wannan baddalawa ce ta faru ga labarin, “Babban Mugun Abu Ɗa Ya Yi Fushi da Iyayensa” na Magana Jari Ce I” da kuma tatsuniyar, “Wani Yaro Mai Taurin Kai” duka jigon iri ɗaya ne, wato suna aikawa da saƙon illar bijire wa iyaye. An kuma gano cewa, dangantakar jigogi tsakanin Magana Jari Ce da Tatsuniyoyin Hausa ta fi shafar Magana Jari Ce littafi na farko, saboda an fi samun labarai masu kama da tatsuniya waɗanda aka gauraya rayuwar mutane da dabbobi da ƙwari da tsirrai da dai sauran halittu kuma a nuna suna magana da aiwatar da wasu ɗabi’u da halaye irin na ɗan’adam.

 

5.0 Kammalawa

            Saƙonnin da ke cikin wasu labaran littafin Magana Jari Ce I-III na Abubakar Imam, su ne kuma ke cikin tatsuniyoyin Hausa, kuma su ne masana da manazarta ke kira jigogi. Jigogin da littafin Magana Jari Ce da tatsuniyoyin Hausa suna da ɗimbin yawa, d babu wanda domin babu wanda zai bugi gaba ya ce ga yawansu. Jigogin nan sun fi karkata a kan hani da wasu miyagun halaye na zamantakewar al’umma da kuma horo a kan aikata wasu kyawawan ɗabi’u da al’umma ta ɗauka su ne masu kyawu. Takardar ta kwatanta tare da alaƙanta jigogin wasu labaran Magana Jari Ce da tatsuniyoyin Hausa. An yi bayanin gabatarwa a farkon takardar, daga nan sai da aka kawo ma’anonin tubalan take, kamar labari da jigo da tatsuniya. Daga nan sai aka yi taƙaitaccen jawabi a kan samuwar littafin Magana Jari Ce I-III. An kawo dangantakar wasu jigogin labaran da ke cikin Magana Jari Ce da tatsuniyoyin Hausa. Duk dangantakar da aka kawo, sai a shiga cikin matanin labarin da kuma tatsuniyar domin a samo misalai a kafa hujja da su. Daga ƙarshe sai aka kawo sakamakon bincike, sannan aka kawo jawabin kammalawa. An kawo muhimman wuraren da aka sami bayanan da aka gina maƙalar da su a matsayin manazarta.

 

Manazarta

 

Bakura, A. R. (2014). Kishi a Ƙasar Hausa. Kaduna: Garkuwa Media Publication.

 

Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, (2006). Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero. Zaria: Ahamadu Bello University Press.

 

Furniss, G. (1996). Poetry, Prose and Popular Culture of Hausa. England: Edinburgh University.

 

Guga, S. B. (2010). Yanayin Sarauta a Cikin Magana Jari Ce I-III. Kundin Digiri na Biyu. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya da Afirika. Zaria: Jami’ar Ahamadu Bello.

 

Guga, S. B. (2015). Gaskiya a Bahaushiyar Al’ada. Ƙalubalen Magana Jari Ce ga Sarakuna. A Cikin Kadaura, Journal of Multi-discipilinary Studies. Department of Nigerian Languages, Kaduna State University. Kaduna: Winners Printers Limited. P46-58

 

Gusau, S.M. (2015). Mazhabobin Ra’i Da Tarke A Adabi da Al’adu Na Hausa. Kano: Century Research and Publishing Ltd.

 

Geza, S. M. (2004). Matsayin Karin Magana a Cikin Rubutaccen Adabin Hausa. Nazarin Littafin Magana Jari Ce. Kundin Digiri na Farko. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya. Sakkwato. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.  

 

Hassan, S. (2013). Nazari a Kan Mutuntaka da Adabi. Tasirin Abubakar Imam a Magana Jari Ce. Kundin Digiri na Uku. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya da Afirika. Zaria: Jami’ar Ahmadu Bello.

 

Ibrahim, I. S. (1990). Morality in Abubakar Imam’s Magana Jari Ce. A Paper Presented at Departmental Seminar. Department of Nigerian and African Languages. Zaria: Ahmadu Bello University.

 

Imam, A. (1939). Magana Jari Ce Littafi na Farko. Zaria: Northern Nigeria Publishing Company.

 

Imam, A. (1940). Magana Jari Ce Littafi na Biyu. Zaria: Northern Nigeria Publishing Company.

 

Imam, A. (1940). Magana Jari Ce Littafi na Uku. Zaria: Northern Nigeria Publishing Company.

 

Koko, H. S. (2009). Jagoran Nazarin Tatsuniya. (Babu Wurin Ɗab’i).

 

Malumfashi, I. (2009). Adabin Abubakar Imam. Sokoto: Garkuwa Media Serɓices Limited.

 

Malumfashi, I. Ed. (2019). Labarin Hausa A Rubuce 1927-2018. Zaria: Ahamadu Bello University Press.

 

Musa, S. (1993). Juyar da Labarin Kalala da Kalalatu na Magana Jari Ce na Dr. Abubakar Imam Zuwa Wasan Kwaikwayo. Kundin Digiri na Farko. Zaria: Jami’ar Ahmadu Bello.

 

Poul. R. (1970). African Folklore. New York: University Press.

 

Propp, Ɓ. (1928). A Morphology of Folktale. Lincoln: University of Nebreska.

 

Pweddon, N. (1977). Thematic Conflict and Narratiɓe Techniques in Abubakar Imam’s Ruwan Bagaja. Ph.D Thesis. Department of African Languages. Madison: University of Wisconsin.

 

Ruth, F. (1970). Oral Literature in Africa. Ibadan: Oxford University Press.

 

Sarɓi, S. (2005). Nazarin Waƙen Hausa. Kano: Samarib Publishers.

 

Todorov, T. (1969). The Theories Du Symbole. Translated into English by Fludernik, M, 2004. England: Routledge.   

 

Thomson, S. (1977). The Folktale. Lodon: University of Caliponia Press Barkley.

 

Umar, M. B. (1982). Dangantakar Adabin Baka da Al’adun Gargajiya. Kano: Benchmark Publishers.

 

Usman, B. (2012). Taskar Tatsuniyoyi. Kano: Gidan Dabino Publishers.

 

Usman, B. (2013). Folklore and History. The Twin Riɓers of World Heritage. Abuja: Klamidas Communications Limited.

 

Yahaya, I. Y. (1988). Hausa a Rubuce: Tarihin Rubuce-Rubuce Cikin Hausa. Zaria:  Northern Nigeria Publishing Company.

 

Yahaya, I.Y. (1971). Tatsuniyoyi da Wasanni na IV. Ibadan: Oxford University Press.

 

Yahaya, I.Y. (1992). Darussan Hausa Don Manyan Makarantun Sakandare. Ibadan University Press Plc.

 

Zarruk, R. M. (1986). Sabuwar Nazarin Hausa Don Ƙananan Makarantun. Ibadan: University Press Plc.

Post a Comment

0 Comments