Ticker

6/recent/ticker-posts

Bambancin Sha'awa Da Soyayya (Kashi na 09)

Wannan na ɗaya daga cikin jerin rubuce-rubucen da Zauren Markazus Sunna ke samarwa kan batutuwa daban-daban da suka shafi rayuwar al’umma. A wannan karon rubutun ya shafi “Bambancin Sha’awa Da Soyayya” wanda Baban Manar Alƙasim ya rubuta

Bambancin Sha'awa Da Soyayya (Kashi na  09)

Baban Manar Alƙasim

Abubuwan da suke gina soyayya ta ƙwarai kamar yadda muka fada guda uku ne:- 1) Huduwar ginin jiki, ta yadda uba zai gina yaronsa har ya tabbatar da cewa yana da ƙarfin da zai iya daukar nauyin kansa da na waninsa nan gaba, zai iya neman na kansa ba tare da ya tsaya sai wani ya ba shi ba, zai iya tsayawa a inda Allah SW ya ajiye shi, ba zai riƙa kallon wasu ya sanya kansa dole sai ya yi irin abin da suke yi a gidajensu ba, ya gamsu da cewa shi fa namiji ne, kuma an yi shi ne masamman don ya bayar, yanzu ya zama dole ya nema din don ya miƙa.

In ya zama namiji yana buƙatar wannan tarbiyyar a waje don ya zama kamar sauran maza, mace kam sai dai a cikin gida tare da uwa ta gari, yadda za ta saba da aikin cikin gida tun tana ƙarama, koda kuwa mahaifanta masu hali ne, dole ta iya tsaftace daki da bandaki, ta saba da wanki da wanke-wanke, har ya zama ma ta jiki, yadda za a cire ma ta kasalar hidimar miji da tsagina-gini, a koyar da ita cewa sirrin zaman aure yana kan hidimar miji ne da kauce wa gasa da shi, sau da yawa in mutum ya saurari uwayemmu zai ji suna cewa zaman aure shi ne "Yi na yi, bari na bari" sai kuma gudun ƙiwa (ƙyuya) waɗannan abubuwa ba za su taba samuwa ba sai uwaye sun gina 'ya'yayensu ta hanyar da za su iya musayar ƙauna a tsakaninsu.

2) Sai haduwa ta hanyar mu'amalla da iya zamantakewa, yara sukan fara koyon wannan ne daga mahaifansu, in mahaifan ba su da kyakkyawar mu'amalla ga junansu to za su zama makaranta, dole uwa ta ba diyarta kyakkyawar tarbiyyar da za ta iya zama da miji ta hanyar yadda take mu'amalantar na ta mijin, haka uban zai ba wa na sa dan ta hanyar yadda yake zaune da uwarsu, kenan kafin yara su fara kwafo dabi'un waje, sai sun ƙoshi da na cikin gida tukun, sai uwaye su kula da abokai, ƙawaye, maƙwabta, matattara, da makaranta, don waɗannan suna gyarawa kamar yadda suke batawa.

3) Haduwar manufa ga kowani yaro ko yarinya don fuskantar hadaddiyar soyayya, dole su sani cewa aure fa rayuwa ce ta har abada wace ba a fatar rabuwa, sai a fara duba ɓangaren addini sama da komai, domin komai lalacewar mutum ya san akwai Allah, masamman lokacin da ya sami kansa a wani runtsi, to bare kuma aure wanda ba zama ne na rabin wuni kamar aikin gwamtati ba, zama ne na ba dare ba rana har sai ta Allah ta kasance, Hausawa kuwa suna cewa "Zo mu zauna, zo mu saba" dole kowanne cikinsu ya san cewa aure fa ibada ne, abin da yake yi ga masoyinsa ba don shi yake yi ba don Allah yake yi, in ya zama yana yi dominsa zai rabu da shi idan ya saba masa, in kuwa yana yi don Allah ne, to ko ya saba masa yana tare da shi, don wanda yake yi dominsa yana ganin abin da yake yi kuma yana farin ciki.

Da wannan 'yar shimfidar za mu fahimci duk wasu ƙarairayi da ake yi gabanin aure na zaman zance ko na hira a waya ko danna-dannar hanyoyin sadarwa kan cewa "Wallahi ina bala'in son ki da ƙaunarki, in ba ki ba zan iya rayuwa ba, ba zan ko iya cin abinci ba, muryarki ita ce abinci na, ganinki shi ne ruwan shana, sadurmu dake ita ce rayuwata, ni ko zagina kika yi dadi zan ji" wace ta yarda da wannan laffuzan alhali ba ta ko shiga gidan mijin ba ta yaudari kanta, matakin farko ta tambayi duk wata matar aure ta ji, za ta iske cewa ita ma ta ji sama da haka, kuma ta gasgata, amma da ta shigo gidansa ba haka ta sami zancen ba.

Ee to, an sami mummunar fassara ne, don kuwa ya fado abubuwan da suke da alaƙa da sha'awarsa ne, kuma da ta shigo gidansa bayan mako biyu, yanzu ba murya ba ko ganin kwalliya, ya gan ta a haƙiƙaninta, ya ji muryarta ta gaskiya, ya kuma tabi inda bai isa ba, ya taki abin da ya dade yana bege a boye ko a sarari, yanzu sha'awa ta ƙare, in ba a yi guzurin soyayya ba to sai dai kuma zaman haƙuri, ba soyayyar ce ta ƙare ba, don ko tun asali ba ta, sha'awa ce take amsa sunanta, in mace tana da wayau ba ta yarda a yi wannan shirmen da ita, na san wata budurwa (Allah ya jiƙanta, ta yi aure ta rasu ta bar 'ya'ya) daga ranar da saurayinta ya kama hannunta wai zai sanya ma ta zobe, rabuwarsu kenan ta har abada. In wannan ya zama abin lura, ta ina mace za ta yarda wani ƙato ya ribace ta na minti daya ko biyu? Bare ya wawantar da ita da cewa aurenta zai yi amma na dan wani lokaci gajere da zai biya buƙatarsa ta sha'awa, ba ruwansa da tunanin halin da za ta shiga nan gaba, bai damu ba in ya shiga zuciyarta ko bai shiga ba, in wata sha'awar ta sake taso masa lokacin zai neme ta, wannan ya sa dole 'yammatammu da samari mu san bambancin sha'awa da soyayya.

Wannan kuwa zai iya faruwa ne ta wurin kula, nazari da bin tsarin zamantakewa, da wannan 'yar matashiyar za mu fara magana kan aure amma tun daga yadda za a fara nemansa har zuwa yadda Allah SW zai yardar mana, dan abin da muka dan tattauna a baya ya ishi mai hankali ya fahimci me take bibiyarsa, soyayya ce ko sha'awa? In Allah Ya sa matasa da 'yammata da samari har da uwayenmu suna da lokacin da za su karanta kuma su yi tsokaci muna buƙata, sai dai muna roƙon duk wanda zai yi tsokaci ya yi shi a fili yadda kowa zai amfana, Allah ya sa mu dace da masoya na ƙwarai. A nan zan dakata. Sai mun haɗu a rubutu na gaba.
Bambancin Sha'awa Da Soyayya (Kashi na  09)

Post a Comment

0 Comments