Ticker

6/recent/ticker-posts

Malam Mene ne Hukuncin Matar Da Take Zagin Mijinta?

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Malam Mene ne Hukuncin Matar Da take Zagin Mijinta?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

الحمد لله رب العالمين.

Idan mace takasance tana cutar da mijinta da zagi da cin mutunci da munanawa, wajibi ne ya zaunar da ita yai mata nasiha, ya tsoratar da ita, ya bayyana mata haɗarin laifin datake aikatawa na zaginsa, musamman saboda miji shi ya fi can-canta ta kyautata masa, kamar yanda Annabi sallallahu Alaihi wasallam ya ce:(Da ya halatta wani yaiwa wani sujjada dana umarci mace taiwa mijinta sujjada) Abu dauda(2140) da turmuzi (1159) Albani ya ingantashi a cikin sahihu Abu dauda.

 saboda tsananin haƙƙin biyayya da kyautatawa dake kan mace ga mijinta.

Ya kamata mijinta yabi matakan ladabtar da ita wanda Allah ya ambata a cikin alƙur'ani nayi mata wa'azi da tunatarwa, da kauracewa, da duka wanda bamai fasa jiki ba.

Idan yaihakan duk bai amfaniba, yahadata dawani salihi cikin danginta yaimata nasiha, saboda kiyaye zurriya dakuma lura da haƙƙin 'ya'ya idan akwaisu, Allah madaukakin sarkin ya ce:

(الرجال قوامون على النساء بما فضل الله بعضكم على بعض وبما أنفقوا من أموالهم فالصا لحات قانتات حافظات للغيب بما حفظ الله والاتي تخافون نشوزهن فعظوهن وهجروهن في المضاجع واضربوهن فإن أطعنكم فلا تبغوا عليهن سبيلا إن الله كان عليا كبيرا)، النساء 34

Mazaje sune shugabanni akan matayensu saboda Abun da Allah yafifita sahinsu akan sashi, saboda abun da suke ciyar damatayen nasu daka dukiyoyinsu, Nutsatstsiyar mace saliha tagari ita ce, tsayayya akan dokokin Allah dana mijinta, mai kiyaye mutuncin mijinta da dukiyarsa idan baya nan, da abun da Allah yakiyayeta waɗanda kukaji tsoran fandarewarsu kuyi musu wa'azi ku ƙaurace musu awajan kwanciya kudakesu, idan sundawo sun yi biyayya akan abun da suke saɓa muku sun daina, kada kuce zaku bijiro dawata hanya ta cutarwa agaresu, lallai Allah ya kasance madauki mai girma.

Daka wa'azin dazai gabatar mata, shi ne yabayyana mata girman zunubin dake kanta na saɓawa mijinta, da abun da Allah yatanadar mata na lada gwaggwaba idan tabi mijinta takyautata masa.

Idan ta amsa wa'azin yai mata tasiri takuma dawo tadena saɓa masa, wannan shi ne abun da ake nema, idan kuma taci gaba da cin mutunci dazaginsa darashin biyayya, Anan babu lafi yasaketa dan babu bukatar cigaba dazama da irin wadannan kangararrun matan.

Malamai sun ambaci saki yana iya zama halal yayinda bukatarsa takama, saboda mugun halin mace, dakuma munana zamanta damijinta, da cutuwar da miji yake da ita, ba tare da faruwar wani dalili daka gareta ba, Almugni (10/324).

Saboda haka hukuncin matar datake zagin mijinta da saɓa masa, shi ne ita mai saɓo ce tana cikin fushin Allah madaukakin sarki, wajibi ne ta gaggauta tuba zuwaga Allah, takuma nemi yafiya daka gurin mijinta, lallai kasncewarta cikin wannan mummunan aiki yana janyo mata fushin Allah dabala'in dabatasan karshensaba.

Wallahu A'alamu.

سبحانك اللهم لا علم لنا إلا ما علمتنا إنك أنت العليم الحكيم.

Tambaya da Amsa Abisa fahimtar magabata Nakwarai

+2348123432272

+2348163731622.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/BXjuXb1WxX99NV3OsXPnLV

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments