Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Wanda Ya Kashe Kansa

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

السلام عليكم

Malam menene hukuncin mutumin da ya kashe kansa sakamakon ya shiga kunci? Kuma menene matsayin masu yi masa addu'ar Allah ya jiƙan sa, Shin hakan ya halasta ne ko kuwa? Ina son a yi min ƙarin bayani na gode.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

وعليكم السلام

Mutumin da ya kashe kansa ya aikata babban zunubi daga cikin manyan zunubai da malamai ke kira Kabá'iruz Zhunuub. Babu wani dalili da zai sa mutum ya kashe kansa a yi masa uzuri a nan duniya, kuma Allah ya ce:

"KADA KU KASHE KAWUNANKU, LALLAI ALLAH YA KASANCE MAI JINƘAI NE A GARE KU". Suratun Nisá'i, aya ta 29.

Hadisi ya tabbata daga Annabi ﷺ cewa: "Duk wanda ya kashe kansa da wani abu, za a dinga yi masa azaba da wannan abun a ranar Alƙiyama" Duba Sahihu Muslim hadisi mai lamba 110.

Sai dai a aƙidarmu ta Ahlussunnah waljamá'ah, duk wani saɓon Allah da mutum ya yi Allah zai iya yafe masa idan ya so in banda shirka, kamar yadda aya ta 48 da ke Suratun Nisá'i ta tabbatar.

Wannan ya nuna kenan Allah zai iya gafarta ma wanda ya kashe kansa idan ya ga dama, idan kuma ya ga dama zai yi masa azaba, daga bisani a fitar da shi daga azaba zuwa rahama matuƙar ya mutu a kan musulunci, saboda wanda ya kashe kansa ba kafiri ba ne. Allah ya tsare mu da mugun ji da mugun gani. A taƙaice dai lamarinsa na wurin Allah Ta'ala.

Haka nan kuma, game da yi ma wanda ya kashe kansa addu'a, wannan shi ma ya halasta, matuƙar ya kashe kansa a halin zamowarsa Musulmi.

Allah ne mafi sani.

Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.

Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin mu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/JoWs3feDfdyGE9yBsa1RSC

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments