Ticker

6/recent/ticker-posts

Hakkokin Aure Abisa Alƙur'ani Da Sunnah

DARASI NA 38

Yadda Allah Ya Hukunta Saduwar Aure

Annabi {s.a.w} ya yi nuni da idan mutum zai kusanci matarsa, to ya aika ɗan aike,

 Abinda ake nufi da ɗan aike anan shi ne ka fara gabatar da wasanni sosai kafin fara saduwa da ita.

 Amma a cikin saduwar akwai iyoyinkin da ALLAH ya iyakance, wanda ya kiyayesu zai sami lada, wanda ya tsalleke dokar ALLAH kuma zai haɗu da azabar ALLAH, kamar yadda hadisai suka tabbatar.

 Jabiru Ɗan Abdullahi (R.A) ya ce:

Yahudawa sun kasance suna cewa: Idan mutum ya yi jima’i da matarsa ta baya, a cikin farjinta, yaronsa zai zama mai ido a juye,

Sai ALLAH Maɗaukakin sarki ya saukar da cewa:

 Matayenku gonaki ne a gareku kuzo ga gonarku ta inda kuke so.

[Bukhari da Muslim]

Wannan hadisi yana magana ne akan halaccin saduwa ta ko wacce siga, a kwance ko a juye koma ta yaya ne, amma kada mutum ya sadu da matarsa ta duburarta, kuma kada ya sadu da ita idan tana haila.

 Manzon ALLAH {s.a.w} ya la'anci wanda ya sadu da matarsa ta duburarta (luwaɗi kenan) kuma ya tsine wa wanda ya sadu da matarsa tana haila.

Abbas (R.A) ya ce: Manzon ALLAH {s.a.w} ya ce: ALLAH baya dubi ga mutumin da yazowa namiji, ko macce ta duburunta.

[Tirmizi da Nisa’i da ɗan Hibban]

Wannan hadisin yana nuni da cewa ALLAH baya kallon Rahma ga wanda ya sadu namiji ko mace ta baya, wato ya aikata luwadi da namiji ko da mace.

 Abu Huraira (R.A) Ya ce:

 Manzon ALLAH {s.a.w} Ya ce:

Wanda aka la’ana shi ne luɗu da mace ta duburunta.

[Abu Dawuda da Nisa’i]

Wato wannan hadisin ma yana magana akan yadda ALLAH ya tsine wa me yin luwaɗi da mace, wato me saduwa da matarsa ta duburarta.

 ALLAH TA'ALAH ya tsine wa namijin da yake saduwa da mace tana haila da kuma wanda yake saduwa da mace ta duburarta.

 Duk wanda yake aikata irin wannan aiki ya yi ƙoƙari ya tuba ya daina, duk wacce tasan mijinta yana aikata irin wannan aiki da ita daga yanzu ta daina, inba haka ba da ita da mijin ALLAH zai yi musu azabah.

 Kome mijinki zai yi kada ki yarda ya sadu dake idan kina haila, kuma kada ki yarda mijinki ya sadu dake ta duburarki, wato ya yi luwaɗi dake.

 Domin hakkin ALLAH da hakkin Manzon ALLAH {s.a.w} sama suke da hakkin iyaye da kuma hakkin miji.

ALLAH ka bamu ikon aiki da abinda muka karanta.

ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.

Hukuncin Wanda Ya Sadu Da Dabba

 Manzon ALLAH {s.a.w} ya ce:

Wanda ya yi zina da dabba, to a kashe shi, kuma a kashe ta itama,

Sai nace: Ibn Abbas (R.A) Mene ne sha'anin dabbar kuma?

Sai ya ce: Nima ban sani ba, sai dai ya faɗi wannan ne saboda kawai yana ƙyamar kada aci namanta bayan an aikata wannan aikin da ita.

[Abu Dawud da Tirmizi]

Wannan hadisi yana nuni kai tsaye da duk wanda aka samu ya aikata zina da dabba to a kashe shi itama dabbar a kasheta,

 Sai dai kuma muna wani zamani da ba a hukunci da littafin ALLAH, saboda haka duk wanda ya aikata irin wannan aiki, to sai ya gaggauta tuba ga ALLAH, idan ALLAH yaso sai ya yafe masa, idan yaso kuma sai ya yi masa hukunci a ranar lahira.

 Amma wajibi ne a kashe wannan dabbar saboda namanta ya haramta.

ALLAH ka bamu ikon aiki da abinda abinda muka karanta.

ALLAH ka gafarta mana zunubanmu baki ɗayanmu Ameen.

 ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments