Wannan rubutu ya yi taƙaitaccen sharhi game da makaɗan jama'a a ƙasar Hausa.
Abbas Musa Jega
abbasmusajega750@gmail.com.
Ɗalibi A Sashen Harsunan Nijeriya Jami'ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato.
Gabatarwa
Makaɗan Jama'a su ne waɗanda ba su tarar yi wa kowa kiɗa. Watau ba sai kana sarauta kaza ba ko kana sana'a kaza, a'a duk wanda ya ba su shi ne uban gidansu. Haka haka suke yi wa Basarake su yi wa mai kuɗi kuma idan ta kama su yi wa talaka. A taƙaice dai wannan rukunin na makaɗa jama'a su makaɗan kowa da kowa ne.
Irin waɗannan makaɗa akan same su suna wasa a ƙofar gidan wani, ko a kasuwa, ko kuma a gefen hanya ko wani keɓattaccen wurin shaƙatawa inda sai an biya za a shiga. Makaɗan jama'a sun kama daga ƴan wasan raha, kamar ƴan kama da ƴan gambara da ƴan ƙoroso. Sun haɗa har da manyan makaɗa kamar su Shata da Ɗanmaraya da Amadu Doka da sauransu.
Watau dai duk wanda ya ɗauki sana'arsa ta kiɗa kamar kasuwanci yana sayar wa kowa fasaharsa sai a ce shi makaɗin jama'a ne.
Ibrahim Yaro Yahya da wasu (1992) ya ce; "Makaɗan jama'a su ne makaɗan da ba su dogara ga wani mutum ɗaya ya zama ubangidansu ba. Sukan yi wa kowa da kowa waƙa saraki da masu kuɗi, da talakawa kai har ma ga karuwai da ɓarayi.
Bello Bala Usman (2021) ya ce; "Makaɗan jama'a su ne waɗanda ake yi wa kirari da cewa kowa ya sha kiɗa abin sa ya bayar. Wanda ya fi kowa shahara a wannan rukunin na makaɗa shi ne Alhaji Mamman Shata".
Daga cikin abin da ke rarrabe makaɗan jama'a da sauran makaɗa shi ne;
1. Ba su da takamaimen ubangida
2. Suna iya yin waƙa a ko'ina
3. Suna yawan yabon halin mutum
4. Suna faɗin duk abin da suka so
5. Suna yawan faɗin sunan wanda ya ba su kuɗi.
6. Suna yin waƙoƙin gargaɗi
7. Suna yin waƙoƙin talla
Abdulƙadir Ɗangambo (1982) ya ce "Makaɗan jama'a su ne makaɗan da suke yi wa kowa da kowa waƙa, ba sai mai sarauta ko mai wani mai babban muƙami ba. Su duk wanda ya ba su, ko kuma idan suka ga dama, to, sai su yi masa waƙa".
Misalan waɗannan su ne:
Alhaji Mamman Shata
Alhaji Adamu Ɗanmaraya Jos
Muhammadu Ganga-ganga
Haruna Oji
Garba Sufa
Hassan Wayam
Audu Karen Gusau.
Ɗangoma
Sa'idu Ziti
Hussaini Jikan Boka
Sani Ɗan'indo
Babangida Kakadawa
Bello Ɗan sha biyu
Gero Zarto
Audu Wazirin Ɗanduna
Alh. Shehu Ajilo Ɗanguzuri
Makaɗan jama'a sukan gina waƙoƙin ne a kan yabo, wani lokaci kuma sukan yi zambo. Idan za su yi yabo sukan yi yabo da alheri, da gwanancewa a sana'ar wanda za su yaba. Kuma sukan haɗa da yi masa kirari da iyayensa da matansa da ƴaƴansa.
Kamar yadda Ali Ɗan Saraki yake cewa Alhaji Mamman Ɗangwate;
"Mai-ƙi-faɗi na Mariya Sanusi, Alhaji Ɗangwate
Mijin Tasidi Alhaji Mamman Ɗangwate
Ɗan Ali baban Ali
Wannan yana da ɗab'iar arziki.
Shi kuwa Alhaji Mamman Shata ga abin da yake cewa Alhaji Magaji Ɗankamasho.
Shugaban ƴan kamasho
Magaji mai ido ɗaya
Mil ɗaya in ya ce sule,
Dole sulen za ka biya
Mil biyu in ya ce dala
Dole dalar za ka biya
Mil arba'in ya ce kwabo
Ka ga kwabon za ka biya
Direba ba za ya ƙi ba.
Waƙar Indon Musawa Ta Shata
"Wata yarinya ga kyan diri
Da kyan tsari Indon Musawa
Wata mace ce mai kyau Indon Musawa
Wata ƴar yarinya mai kyan diri da kyan tafiya Indon Musawa
Ta yi zaune kamar kumsa
Ta ɗan karkace kamar rufu'a
Ga daɗin faɗi kamar basin, lallan hakuri
Ga kuma daɗin riƙo Kamar carbi Indon Musawa
Ga alƙawar da son jama'a Indon Musawa.
Daga cikin waɗannan makaɗan zan ɗauki ɗaya daga ciki in yi bayanin tarihi, kayan kiɗi da kuma wasu daga cikin waƙoƙin da ya yi. Wanda zan ɗauka a cikin wannan rukunin na makaɗa na jama'a shi ne Alhaji Adamu Ɗanmaraya Jos.
Alhaji Adamu Ɗanmaraya Jos an haife shi a garin Ɓukur cikin jahar Filato a shekarar 1964, sunansa na yanka shi ne Adamu. Ya tashi yana maraya ne, mahaifinsa ya rasu a lokacin yana da kwana saba'in a duniya, mahaifiyarsa ta rasu kafin ya isa zangon yaye. Wannan shi ne dalilin da ya sa mutane suke kiran sa ƊANMARAYA.
Asali:
Mahaifin Adamu Ɗanmaraya Basakkwace ne, ana ce da shi Malam Wayya, shi kuma makaɗin kotso ne na sarakuna. Ya yo ƙaura da iyalinsa zuwa Ɓukur a sababiyar yawace-yawacen kiɗa ya zauna wajen Sarkin Ɓukur Alhaji Muhammadu ya zama Sarkin Kiɗan Kotsonsa. Ashe ke nan, ta duba asali, Adamu Ɗanmaraya Jos mutumen Sakkwato ne.
Raino da ƙuruciya da sana'a:
Bayan rasuwar malam Wayya mahaifin Ɗanmaraya, sai Sarkin Ɓukur Alhaji Muhammadu ya ɗauki rainonsa tamkar ɗansa. Ya sanya shi makarantar boko tare da ƴaƴansa, amma bai yi nisa ciki ba. Ya kuma tura shi makarantar allo inda ya sami gwargwadon karatu. Ɗanmaraya ya so ya fuskanci sha'anin sana'a da kasuwanci amma sai sha'anin waƙa ya ɗauke masa hankali. Ya yi biyar mota tare da karnukan mota tun kafin ya kai shekaru goma sha biyu, daga nan sha'anin waƙe-waƙensa ya ƙara kankama.
Fara waƙarsa:
Ɗanmaraya ya fara waƙe-waƙe tare da yara ƴan'uwansa tun da ake tura shi makaranta sai ya janye jiki ya bi su yana yi musu waƙoƙi. Haka kuma ya taɓa biya ga wata zabiya, mawaƙiya Mamu. Zabiya ce mai yin waƙoƙi tana yawon kiɗa, har Allah ya kawo ta Ɓukur inda Adamu ya taɓa biya tare da ita da yaranta guda biyu wato Audu da Idi.
Kamar yadda na nuna a lokacin da yake biyar mota waƙoƙinsa suka fara kankama. Waƙarsa ta farko ita ce ta "karen mato". Ya sami basirori game da zaman direba da karen mato da fasinjoji da rikicen-rikicen karen mato, musamman a ci tuwo ba biya da sauransu. Bayan wannan waƙa kuma sai ta "ƴan amalanke" daga nan tafiya ta miƙe. Saboda zaman cuɗanya yau da gobe ya janyo sha'awar Ɗanmaraya ya soma yi musu waƙa don kada ya bar wannan wannan ilmi da ya samu ya tafi a banza.
Kayan ƙidansa
Alhaji Adamu Ɗanmaraya Jos yana amfani da kayan kiɗa ne nau'in Isga, wato kayan kiɗa ne waɗanda ba nau'in ganga ba.
KUNTUGI
Yadda ake haɗa kuntugi shi ne, ana samun gwangwanin kifi ne irin wanda ake haɗa kuntugi da shi, da itace kamar na darbejiya ko na ƙirya wanda za a fiƙe, sai a sami yisgar doki a shirya kuntugi.
Kuntugin Ɗanmaraya na farko yana yaro ƙarami ya sami fankon ashana da tsinken tsire da yisgar doki ya harhaɗa shi.
A yau akan yi amfani da gwangwanin kifi sadin da itace fiƙaƙƙe da yisgar doki da fatar damo ko wata dabba wajen haɗawa da shirya kuntugi.
Daga cikin makaɗan da ke amfani da kuntugi bayan shi Ɗanmaraya sun haɗa da Babangida Kakadawa da Sani Ɗan'indo da sauransu.
DOKTAN KIƊA
Jami'ar Jos ta yi la'akari da taimakawar da Adamu Ɗanmaraya yake yi ta fuskar habaƙa adabi da al'adun al'ummarsa sai ta girmama shi da ba shi Digirin Dokta, a lokacin bikin saukar karatu na jami'ar na shekarar 1990/1991.
Waƙar karen mato Ɗanmaraya ya yi ta ne a lokacin da yana da shekaru goma sha biyar. Ga misali daga cikinta.
To Bismilla Malam nabaya
Ga faralin Malam nabaya
Ga tarihin Malam nabaya
Aura dillalin ƙuli-ƙuli.
Ga tarihin Malam nabaya
Ɓaleri karen mato
Aura babban kaftaninka rana
Ɗan baƙi mai buje da rana.
Na-innako takalminka la
Ga babban faci a tsuli
Gago mai ɗinki da basilla
Ɗan-baƙi mai totur da sakaina.
Karen mato yai girman kura
Ga gashin baki ga gemu
Ga hana ƙarya ga saje
Sannan kuma ga rinto gidan tuwo.
Ɗanmaraya ya yi waƙoƙi da yawa dangane da fannonin rayuwa daban-daban. Akwai waƙoƙinsa shahararru waɗanda mutane suke sha'awa suke ƙaruwa da ilmantuwa. Daga cikin waƙoƙinsa akwai:
Waƙar Lebura
Waƙar Jawabin aure
Waƙar Malalaci
Waƙar Talakawa
Waƙar Sojoji
Waƙar Ɗangaye
Waƙar Ɗan'adam
Waƙar Tica
Waƙar Sisi Legas
Waƙar Falmata
Waƙar Ƴankamasho
Dubi yadda ya bayyana rayuwar yau da gobe daki-daki cikin waƙar Lebara;
Yau Lebura wai kamar zakka
Aiki rani zuwa kaka
In gwamnati za ta sa doka
Shi Lebura ba shi karya ta
Aiki aiki cikin taro
Ana abu sai ka ce horo
In dai Allah ake tsoro
Da Lebura bai talauci ba
Dubi tara gyaɗa kamar dala
Ƙauye da cikin Kano jalla
A ɗauki guda a ɗora ta
Amma ba za ta goce ba.
Ɗanmaraya ya rasu a ranar ashirin ga watan Yuni na shekarar 2015, ya rasu ba tare da Allah ya nufe shi da haihuwa ba, sai dai ya riƙa yara da yawa a gidansa.
17011443H
26082021M
MANAZARTA
Ɗangambo, A. (1982), Rabe-Raben Adabin Hausa da Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa.
Gusau, S.M (1987), Makaɗa da Mawaƙan Hausa. Littafi na ɗaya. Usman Al-amin publishing company, Kano, Nigeria.
Galadanci M.K.M da wasu. (1992) Hausa Don Ƙananan Makarantun Sakandare 2. Siga Press Ltd.
Zarruƙ, R.M (2005) da wasu. Sabuwar Hanyar Nazarin Hausa Don Ƙananan Makarantun Sakandare. Littafi na biyu. University Press PLC Ibadan.
Gusau, S.M. Ƙamusun Kayan Kiɗan Hausa (2016). Century Research and Publishing Ltd. Kano-Nigeria.
Usman, B.B (2021). Laccar aji da aka gabatar a gabatar a sashen nazarin harsunan Najeriya, Jami'ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.