Ticker

6/recent/ticker-posts

Tarken Littafin "Shaihu Umar: Na Sir. Alhaji Abubakar Tafawa Bisa Mazahabar Makisanci

"Ba wani abu ne ya sa na kira ku ba, abin da na ke so game da ku shi ne ku yi shiri ku tafi ku yiwo mini hari a ƙasar Gwari. Ina da wata babbar buƙata ne, saboda haka ina son ku yi shiri maza ku tafi”.

Shehu Umar


Tarken Littafin Shaihu Umar Na Sir. Alhaji Abubakar Tafawa Bisa Mazahabar Makisanci

Idris Abubakar
Hafsat Muhammad
Hauwa Mu’azu
Huwaila Abubakar
Fatima Muhammad Haruna
Hafsat Alhaji Yaya

Department of Nigerian Languages and Linguistics
Bauchi State University Gadau

Gabatarwa

          Wannan takarda da za a gabatar, za tai bayani ne kan tarke/nazarin littafin “Shehu Umar” Na Alhaji Abubakar Tafawa Ɓalewa. Sannan za a ɗora aikin ne kan tsarin mazahabar Makisanci. Amma kafin mu kai ga yin wannan nazari/tarke yana da matuƙar muhimmanci mu haskaka masu sauraru hanya dangane da wannan mazahaba da za mu ɗora aikin mu a kai, akwai buƙatar mu yi bayani dangane da wannan mazhabar tare da kawo wasu daga cikin manufofinta, domin hakan zai taimaka gaya wajen fahimtar madosar wannan aiki.

          Mazahabar Markisanci ta samo asali ne daga tunanin wani Bajamushe mai rajin neman sauyi a sha’anin tattalin arziki da zamantakewar al’umma da kuma siyasar duniya mai suna Karl Henreich Marɗ (1818-1883). Shi dai mafalsafi ne kuma masanin tattalin arziƙin ƙasashe na ƙarni na 19. Ya fito da wannana ƙidar ne a cikin wani littafinsa mai suna, The German Ideology (1845). Wannan mazahabr tana da wasu manufofinta, kaɗan daga cikin irin wannan manufofi na markisanci su ne kamar haka:

1.     Tana duba sha’anin wasu rukononin jama’a da ake danne su, ko ake ware su, ko ake ɗora musu wani nauyin da bai dace ba, akamr wariyar launin fata, ko tauye ‘yancin mata ko mulkin mallaka ko ƙyamar ‘yan luwaɗi da ‘yan maɗigo.

2.     Tana duba rikice-rikicen neman iko da na matsayi a cikin al’umma.

3.     Sannan tana bayyana irin rikicin tattalin arziƙi da na mulki da zamantakewar al’umma tsakanin masu mulki da waɗanda ake mulka (Talakawa).

4.     Tana gano sababbin hanyoyin fahimtar danganatak tsakanin tattalin arziki da adabi da dukkan abubuwan da al’ada take samarwa.

5.     Tana amfani da fasahar fiɗar adabi mai ƙunshe da batun aƙidoji da fito da yadda taurarin littafi ke mu’amala a tsakaninsu ta la’akari da tattalin arzikinsu da yadda suke neman matsayi a al’umma.

A taƙaice wannan mazahabar tana lura da sha’anin tattalin arziƙi da zamantakewa da shugabanci (siyasa) da tarihin al’umma da kuma adabinta shi ake kira da markisanci. Don haka mazahabar markisanci ta tarken adabi na lura da wasu muhimman sassan nazari guda huɗu da suke ƙunshe da irin halayen rayuwar al’umma, kamar haka:

1.     Ƙarfin tattalin arziƙin al’umma

2.     Rikicin neman matsayi a al’umma

3.     Abubuwa na zahiri da na ɓoye

4.     Aikin fasaha da adabi da aƙidoji

Daga ƙarshe bisa ga wannan jawabi da ya gabata a sama ya isa ya yi mana jagora wajen wannan aiki na tarke na littafin “Shehu Umar” Na Alhaji Abubakar Tafawa Ɓalewa.

Tarken Littafin Shehu Umar Duba Zuwa Ga Mazahabr Markisanci

          Dangane da wannan mazahabar kamar yadda muka ambata a manufofinta a baya, ta fi mayar da hankali kan halayen rayuwar al’umma da suka shafi ƙarfin tattalin arziƙi da rikicin neman matsayi a al’umma tare da duba sha’anin wasu rukunonin al’umma da ake danne su, ko ware su, ko ake ɗaura musu wani nauyin da bai dace ba. Don haka wannan littafi na “Shaihu Umar” Na Alhaji Abubakar Tafawa Ɓalewa zai iya hawa wannan mazahabar in muka duba cikin littafin tun daga farko har zuwa ƙarshe kamar haka:

          “Da dukkan mutane suka hallara, kowa ya ba da abin da ya kawo, sai sarki ya ce “kai, ina Makau? Ko an kashe shi ne a can ku ka ɓoye mini?”.

          Jama’a duka suka amsa “A’a! Ranka ya daɗe, ai ka san halin mutanen duniya. Mu ta ma mun yi shiru ne kawai tun da farko da muka ga ka ɗauke shi mu ga yadda za ku ƙare. Domin mun san duk wanda aka ba shi amana ya ci lalle Allah yana kama shi, balle ma kamar kai da Makau wanda ya ke ka yarje masa kamar naka. Bari dai mu feɗe maka biri har wutsiya, a cikin garin nan ba ka taɓa samun wanda yake cin amanarka kamarsa ba. Ai Makau ne ya ke fallasa ka a wajen talakawa da ka ke ganin suna girman kan nan yanzu. Kuma babu asirin da za ka yi da shi waɗansu ba su ji ba. Ka gani tun da muka fita zuwa harin nan har muka dawo bawan Allah nan bai bar zaginka ba, a kan haka ma har sarkin zagi ya ji haushi ya zare takobi zai yanke kansa, sai da barde ya ba shi haƙuri. Yanzu ma abin da ya sa ba ka gan shi ba a nan ya bi ta gidansa ne domin ya ɓoye waɗansu daga cikin bayin da ya samo, gama dai bawa huɗu ya kama, mata biyu da yara maza biyu; amma dai ba mu sani ba, ma ga abin da zai kawo”.

          Da sarkin ya ji waɗannan maganganu sai ya ce “Daidai ne, amma Makau ya kyauta”.

          Idan muka duba wannan jawabi da ya gabata a sama za mu ga cewa tun a kanun littafin “An Ɓata Tsakanin Sarki da Makau”. Za mu ga cewa rikicin neman duniya ya fito ƙarara a fili a tsakanin taurarin cikin littafin. In kuma muka kwatanta wannan lamari da abubuwan da suke faruwa a cikin rayuwar al’umma na yau da kullum, za mu iya cewa wannan rikicin neman matsayin ba wai a iya kan ƙulla makirci ya tsaya ba, har da kisan kai, da asirce-asirce duk dan dai mutum ya ga ya samu matsayi a cikin al’umma.

          Dangane da taurarin cikin littafin kuwa sun yi haka ne domin su raba tsakanin sarki da Makau, kuma haka abin ya kasance har ma sarki ya kori Makau daga ƙasarsa. Don haka wannan manufa ta mazahabar makisanci da take magana kan rikicin neman matsayi da iko ya dace ko zai iya hawa kan wannan littafi na Shaihu Umar kamar yadda muka ambata ko muka gani a shafi na biyar.

          Dangane da wannan mazahabar ta makisanci har iya yau tana duba sha’anin wasu rukunin al’umma da ake danne su, ko ake ɗaura musu nauyin da bai dace ba. Za mu ga a cikin wannan littafi na Shaihu Umar an samu wasu rukunin al’umma da aka mayar da su bayi ake tauye musu hakki ake ɗora musu nauyin da bai dace ba, za mu tabbatar da haka in muka dubi shafi na talatin da ɗaya (31) kamar haka:

          “Da fitowata daga ɗakinsa, in dai duba haka, sai na ga bayi cikin ƙangi an shanya su kawai a rana. Da na daɗa dubawa cikin bayin nan, sai na ga uwata da uban nan nawa, waɗanda aka kamo ni da su daga gona. Daga nan sai zuciyata ta karaya, tsorona kuma ya yi yawa. Ai da na ga haka sai na sunkuyad da kai na wuce, hawaye yana zuba a idona. Na tafi gida, aka ba ni abinci, ga shi ina jin yunwa amma dole na bar shi. Ba abin da nake tunani sai bayin nan. Yayin da duk na sunkuyar da kai sai in gan su, kai na dai zama sai ka ce wanda aka kawo masa labarin ubansa da uwa tasa sun mutu”.

          Don haka a nan bisa hali ko yanayin da Umar ya shiga a sakamakon ganin yadda bayanin nan suke ya isa cewa wannan littafin yana magana ne a wani ɓangaren da ya shafi yadda ake danne wasu rukunin al’umma kuma ake ɗora musu nauyin da bai dace ba a matsayinsu na bayi kawai.

          Har ila yau, a wannan mazahaba ta makisanci tana bayyana irin rikicin tattalin arziki da na mulki da zamantakewar al’umma tsakanin masu mulki da waɗanda ake mulka (talakawa). Idan muka dubi wannan littafi da muke tarkensa bisa la’akari da wannan amzahabar za mu iya cewa kusan duk an gina wannan labarin ne kan ƙarfin tattalin arzikin al’umma, za mu tabbatar da haka in muka shiga wannan littafin kamar haka:

          “Tun a shafi na uku (3) za mu ga yada ake fafutukar neman arziki tsakanin masu mulki da talakawa inda sarki ya sa aka yi kiran dukkan fadawansa. Da suka taru ya ce musu, “Ba wani abu ne ya sa na kira ku ba, abin da na ke so game da ku shi ne ku yi shiri ku tafi ku yiwo mini hari a ƙasar Gwari. Ina da wata babbar buƙata ne, saboda haka ina son ku yi shiri maza ku tafi”.

          Da fadawan nan suka ji wannan magana ta sarki duka sai suka zama kamar mahaukata sabili da farin ciki, suka yi ta murna suna cewa “Da ma mai neman kuka, balle an jefe shi da kashin awaki”!. Dalilin farin cikinsu kuwa shi ne don ka sani a wajen harin nan za su yi samuwa da yawa na dabbobi har zuwa bayi. Kuma in sun dawo sarki zai sam musu rubu’i daga cikin abin da suka samo. Ko wataƙila in mutum ya kama bayi uku sai sarki ya ɗauki biyu daga ciki, shi kuma bar shi da ɗaya.

          Don haka a nan za mu iya cewa an samu rikicin tattalin arziƙi a cikin wannan littafin tsakanin masu mulki da waɗanda ake mulka (Talakawa). Wannan hari kuwa da sarki ya shirya, dalilinsa wai dan yana son ya sami waɗansu bayi ne waɗanda zai gama da nasa ya aika da su Kano, domin a sayo masa tufafi da kayan doki waɗansu kuma ya aika da su Bida domin a sayo masa bindigogi.

          Saboda haka, yanayin tattalin arzikin al’umma yana nuna irin halin da take ciki da wanda za ta iya kasancewa a nan gaba. Mawallafin yana nuna yadda ake da ƙarancin samuwar wasu abubuwan rayuwar kamar su kayayyaki, sutura, da dawakai da kuɗi na masarufin yau da kullum cikin jama’a. sannan waɗannan abubuwa da aka lissafo talakawa ne dalilin samar da su amma ba su da halin mallakar su, to in suka gane ana tauye musu haƙƙi lallai za a samu rikici. (Dobe, 2009:93).

          Saboda haka, a wannan littafi na Shaihu Umar an nuna haka a fili domin kamar yadda aka nuna a shafi na uku su kansu talakawa su ne silar samar da abubuwan more rayuwar na yau da kullum zuwa ga masu arziƙi. Kenan an nuna ko mawallafin wannan littafin ya nuna cewa talakawa a cikin kowanne rukunin al’umma su ne suke samawa masu arziƙi ko masu mulki matsayi da suke tinƙaho da shi.

          Haka zalika an ƙara fito da rikincin neman matsayi a wannan littafi na Shaihu Umar a shafi na takwas (8) inda sarki ya sa aka yaso kayan Makau har da dabbobin Umar na gado, sai Makau ya tashi ya cewa sarki “Ranka ya daɗe, ina roƙon a cikin kayan nan akwai waɗansu waɗanda suke ba nawa ba, kayan maraya ne”.

          Da jin haka sai fadawa suka ɗauka gaba ɗaya “Mhm kun ji ya fara irin ƙaryan nan tasa! Ina ka ga wata dukiyar maraya har da za ka ce tana wurinka? Allah ya daɗe da sarki, ƙarya ya ke yi, ita dukiyar marayan da ya ke faɗi ba wurinsa ta ke ba. Tana wajen uwar yaro, ita ta san inda ta kai abinta.

          A wannan wuri fadawa sun yi waɗannan maganganu ne domin su sake samun wurin zama ko gindin zama a wajen sarki. Don haka a nan wurin ma za mu iya cewa an samu rikice-rikice na neman matsayi a tsakanin taurarin littafin.

          Dangane da sha’anin tattalin arziki kuwa in muka dubi shafi na 11-15 inda Makau ya sadu da maharbi, ya masa nuni da ya zauna a Maƙarfi sakamkon Makau ya ce yana son yin sana’ar nema ne. za mu ga cewa wannan littafi ya shafir harkan tattalin arziki kamar yadda mazahabar makisanci take magana a kai in muka dubi shafi na 12 inda Makau ya ce, “Wai da ni buƙatata ina so in tafi wani ɗan ƙauye ne wanda ya ke tsakanin Zazza da Kano in yi zamana. Domin buƙatata yayin da na sami matsuguni sosai sana’ar da zan yi ita ce noma.

          Saboda haka ke nan mawallafin wannan littafin ya fito ƙarara ya nuna harkan tattalin arzikin al’umma a wannan labarin. Domin noma a wannan zamani kusan babu wata hanya ta bunƙasa tattalin arziki da ya wuce sana’ar noma don haka ne ma ake mata kirari da cewa “Noma tushen arziki”. A wannan littafin an ambaci wuraren noma da lambuna da dama kamar a shafuka kamar haka:

          A shafi na 4 an ambaci gona a lokacin da ‘yan hari suka isa ƙauyen nan da sarki ya tura su ƙasar Gwari domin yin hari. Su Makau sun ɓuya a bakin gonaki ne, da sassafe wajen goshin asalatu, sai arna suka fara fitowa daga gidajensu suna zuwa gonakinsu. A lokacin nan kuwa ruwan sama ya fara sauƙa dukan manoma za su yi ta gyaran gonakinsu”. Kenan mawallafin ya ambaci abubuwan da suke bunƙasa tattalin arziki kamar su noma a cikin labarin kamar yadda muka faɗa.

          Haka a lokacin da kura ta cinye ɓarawon Umar a shafi na 21 nan ma an ambaci gona a matsayin wurin da ake samar da arziki za mu tabbatar da haka in muka shiga littafin a shafi na 21 kamar haka:

          “Kura ta cinye ɓarawo na”.

          Lokacin da masu nemana suka koma tsakar dare ta yi da mutumin da ya sace ni ya ji daji ya yi shiru, sai ya ce da ni, “yanzu mun huta ko? Mu tashi mu tafi. “Sai ya ɗauke ni a wuya ya yi ta tafiya da ni a cikin daji har muka kawo wani ɗan gona”. Kalmar gona ta sake bayyana a cikin wannan labarin.

          Haka zalika, wannan littafi na Shaihu Umar ya dace da wannan mazahaba ta makisanci domin har yanzu in muka duba shafi na 35 mawallafin ya fito da ƙarfin tattalin arzikin al’umma a wannan shafin domin kanun shafin ma ya tabbatar da haka “Mun Taɓa Ciniki”. A lokacin da su Umar suke tafiya a cikin hamada sun zo wani gari inda suka yada zango a buɗe harkan saya da sayarwa kamar haka:

          “Bayan an jima kaɗan sai na ga mutanen garin mata da maza suna ɓarkewa zuwa gare mu. Kuma in duba haka sai na ga kowane bafatake daga cikinmu ya kwance kayansa ya fito da baƙaƙen rawuna da zannuwa irin waɗanda a ke yi a Kano. Daga nan kuwa sai na ga wurin duk ya hargitse sai ciniki a ke yi. Fataken nan suka yi ta ciniki har rana ta yi sanyi, zuwa can wajen la’asar sai na ga kowa ya kama kayansa ya ɗaure. Da almuru ta fara kusantowa sai kuma aka buga kuge muka tashi.

          Idan muka duba wannan wuri a shafi na 35 sai Alhaji Abubakar Tafawa Ɓalewa ya bayyana irin ƙarfin tattalin arzikin da al’ummar take da shi a wannan lokacin. Domin masana ilimin kasuwanci sun bayyana cewa “Duk ƙarfin/kuɗin mutum ba zai iya rayuwa shi kaɗai ba”. Ta wannan hanyar saya da sayarwar ita ce hanyar da wani zai taimaki wani, abin nufi wannan hanyar ta zama wajibi a cikin al’umma sai an bi ta. Sannan tana bunƙasa/haɓaka tattalin arzikin al’umma ta ƙasa baki ɗaya.

          Baya ga ƙarfin tattalin arzikin al’umma, wannan mazahaba ta makisanci tana duba abubuwan zahiri da na ɓoye da suka fito a cikin labarin/adabin. Dangane da abubuwan na zahiri waɗanda mai karatu ba zai manta da su ba, da suke faruwa a cikin wannan labarin sun haɗa da:

1.     Shaihu Umar shi asalin mutumin Kagara ne

2.     Yadda aka ɓata tsakanin sarki da Makau

3.     Haɗuwar Makau da Maharbi

4.     Yadda ɓarawo ya sace Umar da kuma yadda aka yi kura ta cinye ɓarawon Umar

5.     Sayar da Umar ga Balarabe (Abdulkarim)

6.     Karatum Umar a Ber Kufa

7.     Fitan gyatumar Umar zuwa nemansa

8.     Haɗuwar Umar da mahaifiyarsa

9.     Tasowar iska ta turniƙe su Umar da Abdulkarim

A taƙaice waɗannan su ne irin abubuwan da suka faru na zahiri a cikin wannan littafin na Shaihu Umar waɗanda masu karatu ko masu sauraro ba za su taɓa mantawa da su ba.

          Har yanzu wannan mazahabar tana duba irin abubuwa ko aikin fasaha ko aikin ɓoye da suke faruwa a cikin adabi. dangane da wannan littafi na Shaihu Umar akwai abubwa da dama da suka faru a ɓoye tare da nuna aikin fusaha kamar haka:

          “A shafi na 22 an samu aikin fusaha a daidai lokacin da kura ta cinye ɓarawon Umar lokacin da mijin matan nan ya zo lambu ya tarar da abin da ya faru, kamar yadda ya faru a shafin kamar haka: “Da zuwansa sai suka labarta masa duk abin da ya auku. Bayan haka sai ga tufafin mutumin ya shiga binciken abin da ke akwai. Da buɗe rigar mataccen sai ga wata babbar zabira, ba kome a ciki sai soyayyen nama, da danda ƙwarya, da garin soye, da wani ɗan ƙoƙo. Kuma ya duba ‘yar ciki sai ya ga waɗansu layu guda biyu, ɗaya an mata rufi da fatar goshin damisa da sasari a hancinta. Ɗayar kuwa da fatar minjiyar aka rufe, aka ɗinke da jijiyar biri. Ita layan nan ta biyu kuma a cikin wani yankin tsumman saƙi aka ƙunshe ta. A nan kuma ya sa kitsen mutum wanda ya ke milke ta da shi”.

          “A taƙaice in gajarta maka magana dai, da ya dudduba kayan mataccen nan sarai sai ya ajiye zuciya ya ce, “lalle wannan mutum ba uban yaron nan ba ne, ba shakka ya sato shi ne daga wani wuri, domin waɗannan kaya babu mai irin su sai masu sane ko ‘yan ƙwance”. Saboda haka a wannan wuri aikin fasaha ya tabbata.

          Dangane da abubuwan ɓoye kuma “spiritual life” da suka faru a cikin wannan adabin/labarin in muka duba shafi na 47 lokacin da su Abdulkarim da Umar da mutanensu suna cikin tafiya, sai suka ji kuwwa daga wajen ‘yan’uwansu da suka tafi yawo, sai suka hango su a guje-rudididi kamar wasu garken uda. Da suka duba sama sai suka ga hadari ya tokare sararin smaaniya ɓaƙi-ƙirin. Ashe ba hadari ba ne. iska ce kawai ta girma ta zama hadari. A cikin iskar kuwa ba kome sai yashi. Yayin da iskar ta kawo wajensu nan sai wurin ya hargitse, ba sa iya ganin kome balle su san inda wani yake. Iskar nan ba ta tashi yin sauƙi ba sai bayan wani lokaci mai tsawo, kana ta ɗan kwanta. Da idon Umar ya buɗe sai ya duba cikin sararin nan sai ya ga babu kowa sai shi ɗaya”.

          Saboda haka za mu iya cewa wannan wani ɓoyayyen labari ne da ubangiji ya zantar da hukuncinsa a lokacin da ya so. Sannan kuma wannan ba wani abin mamaki ne don ya faru ba.

          An sake samun wannan ɓoyayyun al’amura a shafi na 48 lokacin da iskar nan ta rufe kowa sai Umar shi kaɗai ya rasa inda zai yi, ya tsaya kawai yana jiran mutuwarsa. “A rana ta huɗu wajen la’asar yana kwance sai ya ji kuka kamar na raƙumi sai gabansa ya faɗi, ya ɗaga kai, sai ya hango wani raƙumi daga nesa da labtu ya nufo inda yake. Ashe raƙuminsa ne wanda ya gada, sai ya ga ya durƙusa a gabansa na kai gare shi na dubi salkar ruwa na sha. Hankalinsa ya komo, sai ya yi godiya ga Allah.

          Saboda haka, wannan al’amari ma za a kira shi da “spiritual life”.

          A taƙaice wannan shi ne tarken littafin Shaihu Umar wanda aka ɗora aikin a mazahabr makisanci, wanda muka duba wasu daga cikin manufofin wannan mazahabr kamar su: Ƙarfin tattalin arzikin al’umma, abubuwa na zahiri da na ɓoye tare da aikin fasaha. Duk waɗannan batutuwa mun fito da su a cikin wannan littafin tare da kafa hujja mai ƙarfi.

 

Manazarta

Tuntu masu gudanarwa.

Post a Comment

0 Comments