Ticker

6/recent/ticker-posts

Shaye-Shaye: Mafari, Illoli da Mafita a Taƙaice




Waƙar da aka shirya domin shiga gasar waƙa ta Hausa Music Institute wanda za a gabatar yayin bukin ƙungiyar Dangin Juna Masoya Ala Foundation a Katsina, ranar Lahadi 23-6-2019.

Shaye-Shaye: Mafari, Illoli da Mafita a Taƙaice

Ta


1.         Alhamdullilla kai kaɗai ke ba da sa’a,
A kullum na ja zaren bai ce a’a,
Allah yi salati ga mai jan jama’a,
Ahlihi, sahabu duk da ke masa ɗa’a.

2.         Duniya mai yayi mai al’adu,
Dubi masu kyau, dubi ko na Yahudu,
Duk ciki shaye-shaye ni ke wa gudu,
Dunkurki ka aikin ga sai mai fasadu.

3.         Nau’o’in shaye-shaye sun fi ƙidana,
Na san na ƙwaya manya da ƙanƙana,
Na ga na busawa idan aka ƙona,
Na ji ana shan sirob, babbar magana!

4.         Ranar da anka riƙa har allura,
            Rayi bai nutsuwa sai an ɗura,
            Raba ni kai! Har shaƙa ake na lura,
                        Raɓe-raɓe can kango domin lalura.

5.         Shi shaye-shaye a zam gane shi,
Shina nufin duk abin da in an sha shi-
Shike sanya maye jiki ya yi yaushi,
Shiru-shiru ko surutun ban haushi.

6.         Mafarin shaye-shaye akwai haɗama,
Masu son aiki tuli wai su gama,
Mahaya na biyu, manema rigima,
Matasa da kan fita “taho mu gama.”

7.         Sai kuma yara da ba a kula su sosai,
Saimomi anka mai da su kamar masai,
Sai fa wanda shi abokai suka kwasai,
Sai majinyaci da ke son jin sa wasai.

8.         Matsalolin shaye-shaye suna da dama,
            Mai yi a ƙarshe sai ya yi nadama,
            Mashayi da lafiyarsa zai yi ta fama,
                        Mutane ba su ganin mashayi da ƙima.

9.         Ba ya iya ajiyar kuɗi ko kadara ba,
Ba zai haifi ‘ya’ya masu lafiya ba,
            Ba zai ko samu yardar Ubangiji ba,
                        Ba dole ne ya zulle homar hukuma ba.

10.       Ya ne za a tsai da safarar ƙwaya,
            Yaɗuwa da shan su yara da manya,
            Yara sai mu tashi mui tarbiyya,
                        Yawo, abokai, mu rinƙa tankiya.

11.       Wanda duk ka so ga ice yai tanƙwarawa,
            Walla tun yana ɗanye yake farawa,
            Walwalar ɗiya duk zamo dubawa,
                        Wurin biɗar illimi su zam dogewa.

12.       Mu lura sai hukuma ta zan ta damu,
            Mutum da anka kama ya san ya kamu,
            Mu jama’a dukanmu sai mun fa gamu,
                        Mu ɗauki jinka gyaran halayenmu.

13.       Ya Allah mun tuba ka ba mu lafiya,
            Ya Ubangiji ba mu arziki da kariya,
            Ya Mai Iko, hana mana ƙwaya da giya,
                        Yara da manya mu guje su bai ɗaya.

14.       Naku ne Abu-Ubaida mai ƙin ɓarna,
            Na rubuta MATISHA ƙidan ramzina,
            Na ƙidaya baitukan sha huɗu dai na,
                                                          Na bar ku lafiya sai wata rana.

Post a Comment

0 Comments