Karin magana na d’aya daga cikin
sassan adabin Hausa da ke taskace tantagaryar rayuwar Bahaushe.
Wannan ya sa da wuya a nemi wani ‘bangare na rayuwar Hausawa a
gargajiyance a rasa shi cikin karin maganar su. Ke nan, karin magana
kandami ne da ake iya lek’awa don ganin rayuwar Hausawa ta
gargajiya da ma wadda take da tasirin had’uwarsa da wasu
al’ummun duniya. A tak’aice kafin had’uwar Hausawa da wasu bak’in
al’ummu, suna gudanar da rayuwarsu ne ta hanyar amfani da tunani da
kuma imaninsu na gargajiya wanda suka gada iyaye da kakanni.
ALAMUNA NUHU
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya da Kimiyyar Harshe
Jami’ar Jihar Kaduna
Kaduna, Nijeriya.
Alamunan@gmail.com
08030472882
Mak’alar da aka gabatar a taron k’ara wa juna sani na k’asa da k’asa na farko a kan Nazarin Hausa a K’arni na 21 wanda Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano, ta shirya daga ranar Litinin 10 zuwa Alhamis 13 ga Nuwamba, 2014.
GABATARWA
Karin magana na d’aya daga cikin sassan adabin Hausa da ke taskace tantagaryar rayuwar Bahaushe. Wannan ya sa da wuya a nemi wani ‘bangare na rayuwar Hausawa a gargajiyance a rasa shi cikin karin maganar su. Ke nan, karin magana kandami ne da ake iya lek’awa don ganin rayuwar Hausawa ta gargajiya da ma wadda take da tasirin had’uwarsa da wasu al’ummun duniya. A tak’aice kafin had’uwar Hausawa da wasu bak’in al’ummu, suna gudanar da rayuwarsu ne ta hanyar amfani da tunani da kuma imaninsu na gargajiya wanda suka gada iyaye da kakanni.
Wannan mak’ala ta k’udiri aniyar waiwayen hoton Maguzanci cikin karin maganar Hausawa domin ta fito da imani da tunanin Hausawa a gargajiyance. Yin haka zai tabbatar da cewa, karin maganar Hausa ba, ta bar wannan rayuwa ba. Ta taskace su ta hanyar fitowa da yanayin rayuwar da ta gabata dangane da imanin Hausawa a gargajiyance kafin su sami saukakken addini. K’ok’arin wannan muk’ala a nan shi ne ta nuna wasu rukuni na karin magana masu nuna imanin Hausawa dangane da halayensu, da d’abi’unsu da abin bautarsu na gargajiya.
TUBALAN TAKE
Wannan fasali zai yi k’ok’arin sharhi kan muhimman kalmomi da suka gina taken wannan nazarin domin su yi k’arin haske ga mai karatu. Kalmomin su ne Maguzanci da kuma Karin magana.
MAGUZANCI
Maguzanci d’abi’a ce ta Maguzawa. Su kuma Maguzawa su ne Hausawan asali da ba musulmi ba, wad’anda suka dogara rayuwarsu ga addininsu na gargajiya da al’adunsu da suka sa’ba wa addinin musulunci (Sarkin Sudan 2008). Ta wata fuskar kuwa kalmar Maguzawa jam’i ne na kalmar Bamaguje (Namiji) ko Bamaguza/Bamagujiya (Mace).Saboda haka yanayin rayuwarsu wadda ta dogara kan imani da tunani na gargajiya da ya had’a da addininsu da yanayin rayuwarsu na gargajiya, shi ne Maguzanci.
- KARIN MAGANA
Wani sashe ne na adabin baka da ake amfani da shi domin dunk’ule zance mai yawa cikin tak’aitattun kalmomi wad’anda idan aka warware su sai a ga cewa zance ne mai yawa aka cure wuri guda. Karin magana na d’aya daga cikin wuraren da ake ganin hoton rayuwar al’umma wad’anda aka adana a cikin zantuka na hikima masu buk’atar a san abin da suka k’unsa. A tak’aice akan taskace tarihin faruwar wasu abubuwa cikin Karin magana don ta zama abin amfani cikin zance idan buk’atar hakan ta taso ga mai magana zuwa ga wani.
- KARIN MAGANAR KALMAR MAGUZAWA KO BAMAGUJE KAI TSAYE
Akwai karin maganar Hausawa wad’anda suka zo da kalmar Maguzawa ko Bamaguje kai tsaye tare da nuna wani ‘bangare na abin da ake ce wa Maguzawa. Ga misalin wasu karin maganganu masu d’auke da kalmar Maguzawa ko Bamaguje:
- Duk d’aya, mara sallah ya je gidan
- Wata daban, an ce da Bamaguje Bamaguje.
- Maganin Biri Karen Maguzawa.
- Komai tuban Bamaguje ba a ‘bare masa
A cikin karin magana ta farko an ambaci Bamaguje kuma aka nuna cewa Bamaguje ba ma’abocin yin sallah ba ne. Karin magana ta biyu tana bayani ne cewa Maguzawa ba sa son a kira su da sunan Bamaguje, sun fi so a kira su Hausawa. Idan kuwa aka kira su da sunan Bamaguje suna ganin ba a yi komai ba. Karin magana ta uku nan ma an ambaci Maguzawa har aka kawo bayani da ke nuna su mafarauta ne. Karin magana ta hud’u ita ma ta ambato Bamaguje kai tsaye, to sai dai ta yi k’arin bayani cewa ko da Bamaguje ya tuba ba ya son katsalandan cikin harkokinsa.
- KARIN MAGANAR MAGUZANCI
Maguzanci wata hanyar rayuwa ce da ta yi takun sak’a da rayuwa irin ta addinin musulunci. Maguzanci ya k’unshi wasu al’adu masu sa’bani da koyarwar musulunci (Sarkin Sudan, 2008). Ke nan akan sami karin magana wanda ake sa ran a ciki a ga abubuwan da suka yi takun sak’a da koyarwar musulunci wad’anda kai tsaye Maguzanci ne suke dauk’e da su.
Maguzanci bai tak’aita ga yanayin abinci ko abin sha ba, hanyar bauta ta gargajiya tana daga abubuwan da Maguzawa suke ba muhimmanci a rayuwarsu. Hanyoyin bauta ga Maguzawa sun k’unshi tsafi, da bautar iskoki (bori) (Ibrahim 1982). A ‘bangaren hanyoyin bauta ana samun karin magana wanda yake bayyana ainihin rayuwar ta Maguzawa. Misali:
- Duk bori d’aya ake wa tsafi,
- Duhu d’akin bori,
- An huta bori ya kashe boka,
- K’arya ta k’are bori ya kashe boka.
https://www.amsoshi.com/2017/11/05/zawarci-da-auren-bazawara-maguzance/
Wad’annan misalai sun nuna wani ‘bangare na addinin Maguzawa wato bori da tsafi a karin magana ta farko. Karin magana ta biyu kuwa ta nuna cewa bori a wajen Maguzawa yana da wuri na musamman da ake aiwatar da shi kuma cikin sirri. Su kuwa biyun k’arshe suna nuna yadda addinin gargajiya ke d’auke da tsari wanda idan aka sa’ba shi, za a sami mummunan sakamako ba da ‘bata lokaci ba. Har ila yau bokanci shi ma d’abi’a ce ta Maguzawa wadda ta shafi bayar da magunguna ta hanyar bori.
Tsafi shi ne bin wasu hanyoyi na gargajiya musamman yi wa iskoki hidima, da yanka, da bauta domin biyan wata buk’ata ko samun wani amfani ko tunkud’e wata cuta (Bunza 2006). Ke nan tsafi yana nufin yarda da hanyoyin bautar gargajiya ta hanyar iskoki domin a sami buk’ata ta fuskar cutarwa ga wasu ko biyan buk’atar rayuwa. Idan kuwa haka ne, me ke ciki wad’annan karin maganganu?
- Tsafi gaskiyar mai shi,
- Ranar tsafi Bunsuru ke kud’i,
- Duk bori d’aya ake wa tsafi.
An kira wad’annan karin maganganun Maguzantattu ne saboda tsafi na d’aya daga cikin hanyoyin bauta ta gargajiya ga wanda ya yarda da ita. Ga masu bin addinin gargajiya na Hausa (Maguzanci) sun yarda da tsafi. Wannan karin magana ya had’e bori da tsafi wuri guda saboda suna da alak’a ta kusa, wato dukkansu hanyoyi ne na amfani da iskoki, da yi masu hidima domin neman biyan buk’ata. Tsafi ba ya yiwuwa ba tare da yin yanka ba. Daga cikin abubuwan da ake yankawa wajen gudanar da tsafe-tsafen Maguzawa D’an’akuya (Bunsuru) shi ne kan ga’ba. D’an’akuya ya yi tasiri a tsafe-tsafen matakan rayuwar Maguzawa na aure, da haihuwa da mutuwa (Sarkin Sudan 2008).
Wani ‘bangare da ya shafi hanyar bauta a gargajiyance shi ne imani da Dodo. Bunza (2006) ya ce: “Dodo a al’adar Bahaushe k’irk’irarren abu ne da ake riyawa aka kuma yi imani da samuwarsa. Ya k’ara da cewa Dodo ba isaka ba ne, kuma ba wani abin bauta ba ne da za a aje a yi bauta wurin da al’ada ta aminta da samuwarsa”. To sai dai wannan nazari ya fahinci cewa, Bahuashe ya yi imani da Dodo ne tun gabanin zuwan Musulunci. Haka kuma dodo yana da kusanci da iska dangane da wasu ayyuka nashi.Wannan ya sa wasu karin maganar Hausa ke kawo ayyukansa, da fahintar Hausawa kansa. Misali, ana samun karin maganar Hausa wad’anda dodo ya fito a cikinsu irin su:
- Munafinci Dodo yakan ci mai shi
- Mijin mai Dodo maganin wani kwarto
Manufar wad’annan karin magana ita ce, dodo yana cin mutane. Haka kuma in dai ba a yin munafurci a fili, to shi ma dodo ‘boye shi ake yi a wani ke’ba’b’ben wuri kamar yadda bori da tsafi ke da nasu muhallai na gudanarwa. Baya ga haka, ana iya samun kyakkyawar fahinta da dodo ya zama ba ya cutarwa ga wanda suka yi aminci. Don haka ne Bahaushe ya k’irk’iri karin magana mai cewa:
- Samun yarda ga Dodo ke sa a shiga ruwa gabagad’i
- Ba a aminci da Dodo a yi fargabar shiga daji
Wato dai akwai wasu wurare da ake sa ran cewa a nan Bahaushe ke ajiyar Dodo, ko kuma nan ne ma’boyarsa. Har ila yau, karin magana ta biyu na nuna cewa Dodo yana zaman luman da mai shi, ko wani da ke kusanci da Dodo yana iya samun kariya a wasu lokuta. Wannan ya nuna cewa, amfani da irin wad’annan karin maganganu ‘bir’bishi ne na imanin gargajiya da aka yi a jiya yake bayyana cikin zantukan Hausawa (Musulmi) a yau. Wannan imani na gargajiya kuwa, ba wani abu ba ne illa Maguzanci
- KARIN MAGANA MAI HOTON LAFAZIN BAMAGUJE
A muhallin da Hausawa suke zaune da Maguzawa, akan gane su kai tsaye daga lafazinsu. Irin wad’anan lafuzza suna nuna Maguzanci ne a cikin su ta yadda idan ba Bamaguje ba, babu wanda zai yi irinsu. Misali.
- Za a sami alheri a wannan gona, Bamaguje ya rufe jan Bunsuru a gonar dawa.
- Allah ya yi Allan nasa, Bamaguje ya iske Biri ya mutu a gonarsa.
- Ana zaman k’arya, Bamaguje ya zo gari ya iske ba
A tak’aice, bayanan da ke k’unshe cikin wad’annan karin magana suna nuna Maguzanci ne. Dalili kuwa, Bamaguje ne ke ta’ammali da Bunsuru musamman a wajen tsafi. Haka kuma noma yana daga cikin abin da ba a raba Maguzawa da shi. Hasali ma, noma babbar sana’a ce ga Maguzawa wadda suka gada iyaye da kakanni. Ta hanyar noma ne Bamaguje yake kaiwa k’ololuwar shahara har a yi masa bukin dubu. Batun tsintar mushen Biri a gona ga Bamaguje kuwa tamkar kara ma Barno dawaki ne domin nama ne mai kyau a gare shi. A wata fuskar kuwa sai a ce lallai tsafinsa na uwar gona ne ya kama Biri a yayin da ya zo yi masa ‘barna.
Idan kuwa ana zancen noma Maguzawa ba baya ba, don haka ne ba sa iya zama wurin da ba zai ba su damar yin noma ba wanda da shi ne rayuwarsu ta dogara. Kenan a wajen Maguzawa, zama wurin da ba a yin sussuka zama ne marar amfani a nasu gani.
Idan aka ji wani yana magana sannan ga batsa yana kutsawa cikin zancensa ana iya cewa akwai ‘bir’bishin Maguzanci tattare da wannan zance. Abu mafi kusanci da batsa wanda Maguzawa ke yi shi ne ashar. Suna yin ashar ne a yayin d’aura aurensu wanda wani ashar d’in ma surke yake da batsa. Ambaton wani sashi na al’aura kai tsaye ko a kaikaice na iya zama batsa kamar yadda ya zo cikin wad’annan karin maganganu:
- An takalo tsuliyar Dodo
- Dole/Tilas zama da d’uwawu
- Ba a had’a gudu da susan d’uwawu
Abubuwa biyu ne ke k’unshe cikin karin magana ta farko wato kalmar tsuliya wadda batsa ce kai tsaye. Ambaton Dodo da aka yi shi kuwa ya nuna imanin Bamaguje ne. To amma sai ga shi irin wannan karin magana tana zama abin kwatance da wani abu da zai wahalar a yayin zance. Haka kuma kalmomi irin su d’uwawu da aka yi amfani da su a misali na biyu da uku fad’arsu zai sa k’imar mutum ta ragu ga masu saurare, saboda kalmomin sun shafi al’aura.
https://www.amsoshi.com/2017/11/05/1267/
6.0 KAMMALAWA
Tsafi da bori da Dodo hanyoyi ne na bauta da suka shafi addinin gargajiya wad’anda idan ba Bamaguje ba, babu mai yin su a matsayin bauta. Wasu lafuzzan kuwa ba a sa ran jinsu bakin kowa sai Maguzawa, su ma d’in sai don kasancewarsu masu bin tsarin gargajiya a harkokin rayuwarsu. Rayuwar Maguzawa ta yau da kullum ta fi karkata wurin noma, wannan ya sa ba sa iya zama nesa da gonakinsu. Samuwar karin maganganun Hausa masu d’auke da Maguzanci cikin zantukan Hausawa a yau kuwa wani abu ne da wannan muk’ala ta gano a matsayin hoton rayuwar Hausawa ta gargajiya a wasu ‘bangarori. Idan har za a rik’a amfani da wad’anan karin maganganu, yana da kyau a lura da abin da suke k’unshe a ciki don kauce wa Maguzanci.
MANAZARTA
Abdullahi, I.S.S 2008. Jiya Ba Yau Ba: Waiwaye a Kan Al’adun Matakan Rayuwar Maguzawa na Aure da Haihuwa da Mutuwa. Kundin Digiri Na Uku, Jami’ar Usman D’anfodiyo, Sakkwato.
Abdullahi, I.S.S 2008. Fitattun D’abi’un Maguzawa, Maiduguri Journal of Linguistics and Literary Studies, (MAJOS) ‘Bolume. d’ Department of Language and Linguistics, University of Maiduguri.
Abdullahi, I.S.S 2008. “Bamaguje da D’an Akuya: Rashin K’auna Ko K’iyayya?” Departmental Seminar Series, Department of Nigerian Languages, Usmanu D’anfodiyo University, Sokoto.
Abdullahi, I.S.S 2012. “Falsafar D’aurin Auren Maguzawa”. Muk’alar da Aka Gabatar a Taron K’ara wa Juna Sani a Cibiyar Nazarin Hausa, Jami’ar Usmanu D’anfodiyo, Sakkwato.
Abdullahi, I.S.S 2014. “Matsalolin Koyar da Maguzantattun Wak’ok’in Hausa”. Mak’alar Da Aka Gabatar A Taron Kara Wa Juna Sani Na K’asa da K’asa A Akan K’alubalen Koyar Da Harsunan Afirka, Niamey Jamhoriyar Nijer.
Bunza, A.M. 2006. Gadon Fed’e Al’ada. Tiwal Nijeria Limited, Lagos.
D’angambo, A. 1984. Rabe-raben Adabin Hausa da Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausa. Triumph Publishers, Kano.
D’anyaya, B.M. 2007. Karin Maganar Hausawa. Makarantar Hausa, Sakkwato.
Gusau, S.M. 2008. Dabarun Nazarin Adabin Hausa. Benchmark Publishers, Kano.
Gusau, S.M. 2011. Adabin Hausa a Sauk’ak’e. Century Research and Publishing Limited, Kano.
Ibrahim, M.S. 1982. Dangantakar Al’ada da Addini Tasirin Musulunci Kan Rayuwar Hausawa Ta Gargajiya. Kundin Digiri Na Biyu, Jami’ar Bayaro, Kano.
Koko, H.S. 2001. Hausa Cikin Hausa. Sokoto Nijeriya.
Magaji, A. 2002. Wasu Al’adun Hausawa: Yanaye-Yanayensu A K’asar Katsina. Kudin Digirin Na Uku, Jami’ar Bayero, Kano.
Malumfashi, I.A. da Ibrahim, N.M 2014. K’amusun Karin Maganar Hausa. Garkuwa Media Ser’bi’bes, Kaduna.
Umar, M.B. 1987. Dangantakar Adabin Baka da Al’adun Gargajiya. Triumph Publishers, Kano.
7 Comments
Sannunku da kokari Malamanmu.
ReplyDeleteMuna gaishe da Malama Zainab. Da fatan za a sanar da dalibai da malaman Hausa game da wannan kafa.
ReplyDelete[…] Maguzantattun Karin Maganar Hausa […]
ReplyDeleteWannan abu akwai burgewa sosai amma mu dalibai ne da malamanmu zamu raya wannan kafa....
ReplyDeleteAmma ina Neman tallafi akan
Karin maganar da duka fandarewa ko suka bsabawa addinin musulunci guda 50....
Abu ubaida Allah ya kara jagora
Muna godiya Malam Taheer.
ReplyDeleteGame da karin magana, za ka yiya duba littafi mai suna K'AMUSUN KARINMAGANA na Farfesa Malumfashi da Nahuce. Insha Allahu za ka dace.
Mun gode.
Mun gode.
ReplyDeleteAllah ya biya.
ReplyDeletePost your comment or ask a question.