YAƘI DA BARA
Ta
Abu-Ubaida SANI,
Ph.D.
Department of
Languages and Cultures,
Federal University
Gusau, Zamfara, Nigeria
Email: abuubaidasani5@gmail.com | abu-ubaidallah@fugusau.edu.ng
ORCID: https://orcid.org/0000-0001-6447-4334 | WhatsApp: +2348133529736
Matashiya
Tuni bara da roƙo suka kasance tamkar
wani ɓangare
na al’adun Hausawa a sakamakon ƙaruwar Hausawa mabarata da ake samu. Ba a iya ƙasar Hausa ne Hausawa suke bara ba, har
sukan je wasu garuruwa na kusa da na nesa. Wannan al’amari ne da yake ɓata sunan Hausawa a idon abokan zamansu –
ko bayan ɗimbin
illoli da bara take tattare da su. Wannan waƙa ce da aka shirya domin
faɗakarwa ga waɗanda suka ɗauki bara (roƙo) a matsayin sana'a.
YAƘI DA BARA
Bismilla Ubangiji farko na ambace ka,
Sallu ala Mauhammadin manzo Ɗaha naka,
Alayensa na haɗa har da sahabu dukka,
Har mu ‘yan ku-ci-ku-ba-mun da muke ta
harka,
Yafe Al-Afuwu saɓon da mukai gareka.
Yau magana a kan bara ce ta azazzale ni,
Kai ne Al-Alimu kama mini don a ji ni,
Ra-ra-ra na zayyano harshe kar ya ja ni,
Mai roƙo da banbaɗa zan so duk ku ji ni,
Fatana mu tsira don gobe mu samu barka.
Mece ce bara tukum? Ya aka wagga sabga?
Roƙo ne da tambaya mai yi za ya
zaga,
A ba su abinci ko tufa ko naira su ƙirga,
Koko a ta da hannuwa ɗai in an ga hanga,
Sai su wuce hannu fayau babu batun sadakka.
Mene ne ka sa bara? Ya ci ku tambaye ni,
Ga jerin silar idan za ku ƙida ku bi
ni,
Akwai nakasa a fari zan yo ƙarin
bayani,
Kuturta ko kurumta da gurgunta ne tsani,
Sai a ɗale a luluƙa, roƙo za a afka.
Hausawa suna da camfi zan so ku ji shi,
Mai baiwa ko nakasa ko tawaya gareshi,
Allah ya yiwo shi ne yai roƙo a ba shi,
Idan kuwa ya ƙi yin hakan to hau za ta hau
shi,
Zai taɓe ya sabbace, kun ji fa wagga
hauka.
Camfin ne ya sa tagwaye suka zamma jari,
Uwar da ta haifi ‘yan tagwai to ta samu sirri,
Wai fa hana su saddaka na kawo tujari,
Ta zaga gari tana baran naira koko gari,
A ba ta gudun bala’i don wai kar ya auka.
Sila na bara na biyyu shi ne almajiranci,
Gudun hijira ƙidanya haɗa na huɗun maraici,
Akwai safara da son rai akwai tsantsar talauci,
Akwai rabuwar iyaye a aure ba mutunci,
Sai a rabe a farraƙe har ‘ya’ya su koka.
Akwai aure da haihuwar son rai ko jahilci,
An ƙi a tsara tsarin ƙwarai a cikin adalci,
Yara ƙanƙana a tura su bara fatauci,
Akwai har masu shara gidajen karuwanci,
Su ke tambaɗewa abin
tsoro da shakka.
Mun yi tara ƙidanmu kar
dai lamba ta kuɓce,
Akwai mutuwa ta zuciya su at cima kwance,
Ana gado na yin bara tamkar sanna’a ce,
Korar ɗa ya bar gida koko ɗiya ta macce,
Dukka sila na yin bara ne, dozin ƙidanka.
Manzo ya faɗi hadith zan yi tuni gare ku,
Mai tafiya ya yo ice don ya sayar garinku,
To darajarsa ta wuce masu barar cikinku,
Fuskar mai bara ƙiyama ko ta ga tasku,
Domin sai ƙashi ƙwarangwal ce babu tsoka.
Mai yi don ya yo kuɗi roƙon garwashi ne,
Kashedin ar-rasul faƙat roƙo dai haram ne,
Sai ga mutum uku kaɗai duk maganar hadith ne,
Ukun talakan cikinsu sai an samo mutane,
Sui shaidar haƙiƙanin ya zamto talakka.
Hausawa suna da haushi da abin takaici,
Sun ƙi biɗar halaliya sai roƙo da naci,
An murɗe wuyar hadith, aya an yi faci,
An yo fassara dadai son ran makiranci,
An farlanta yin bara an jera da zakka.
Manzo zai yi alfahar in ya ga al’umarsa,
Amma fajiri ina ranar haihuwarsa?
Ni dai in a nawa ne gwara a yo ɓarin sa,
Ko da ya fito waje gwara a karɓi ransa,
Ga shi muna ta girbin abin da mukai ta shuka.
Bahaushe na da ƙaulin da
shi ne yah haɗo shi,
Idan Allah ya tsaga baki a mutum fa to shi,
Ba ya hana shi ci da sha don shi ne ya yo shi,
Kan haka an taƙarƙare haiƙan babu
fashi,
Bahaushe na ta haihuwar masu bara da ɗauka.
Sun cika titunan ƙasar Hausa
fa jarraba ce,
Har Kudu ma suna zuwa, wannan fallasa ce,
Wasu a coci ma suke, wannan tambaɗa ce,
Wassu barin ƙasar suke kun san zauɗaka ce,
Shashashun cikinmu sun sa kimarmu sauka.
‘Yan Kudu na ta zolaya roƙon nan sila
ce,
“Malam” ko a ce “aboki” kalmar ba’a ce,
Ko “almajiri” kawai ba wani kauce-kauce,
Sui kora da fafarar Hausawa tsiyace,
Har tsalin zumagiya har da bugu da ɗirka.
Tsummokara jikinsu duk ba zarra na gata,
Ba wanka ba wanki ba yankan farata,
Sai ƙazuwa da ƙwarƙwata tsabagen ƙazanta,
Ba bayi matsugguni babu gida a kwanta,
Sai dai kame-kame nan kangwaye da bukka.
Akwai ma masu yin hayan yara don su goyo,
Don a ji tausayin na goyen sam babu wayo,
Ga yaro mitsittsili roƙo na ta
koyo,
In ya girma ya ƙware maitar ba ta ɓoyo,
Sai ya ɓuge ya
rankaya sawu ne ya taka.
Su ma yara ƙanƙana duk haka za su taso,
Ba ilmi ba magani ba wanka da soso,
Su mata a gun bara tabbas babu mai so,
Sai dai in a yo aro ai ɗani a kwanso,
Ga baiwa marar gata an maishe ta jaka.
Sun zama karnuka kawai sun koma kucakai,
Wasu suna da zarrafi sun faɗa wa son kai,
Sun hantse a tituna shan rana na sa kai,
Sun tattara dukiya ga su kamar musakai,
Har mota suke saya mai safara karauka.
Wassu suna bara suna ɗan taɓa ɗauke-ɗauke,
Wassu ana haɗi da su ƙwaya za a sauke,
Za su aje su adana har mai su ya ɗauke,
Wassu ko ‘yan ta’adda ne informer a sinke,
Za su naɗa su zagaya
sui sharhi a kanka.
Yanzu bara tana salo an sirka da ƙarya,
Za ka ga saurayi tasha ga tari na kaya,
Zai ce ya fito gari ya yi gamo a baya,
Yanzu yana biɗar na mota
ne ko ya karya,
In ka ba shi zagayewa zai yo ya bar ka.
Wassu suna zuwa masallatai ne su tashi,
Sui ƙaryar wutar bala’i ce wai ta tashi,
An musu gobara gidan sai toka da gaushi,
In ka nemi jin ƙwaƙwaf ka yi batun ka bi shi,
Zai zage ya ƙetare don ya guje ganinka.
Wassu a tituna suke ƙaryar
taimako ne,
Suna cike ramuka kamar dai ‘yan agaji ne,
Idan ba mai ganin su ko sai su yi gefe zaune,
Idan mota ko ta nufo za su nufo biɗa ne,
Sai ka cire ka ba su sunan sun taimake ka.
Waɗansu salonsu su takardu ne da kati,
Su ce ma babu lafiya sun zaka assibiti,
Wassu gidanka za su zo ko su tare a titi,
Ko a gida na sai da mai ko baki na kanti,
Take za su yanyame in mota ka faka.
In ko abinci kas saye yara suts tsare ka,
Sui maka ƙur na mujiya sakkat sun hana ka,
Mai masa da ‘yan bara ruuu za su ishe ka,
In ma ka yiwo biris ta iya tambayarka,
“Malam ko kana wa almajirrai
sadakka?”
In ka saya ka ba su nan to za su kasafta,
Sui yi gaba su ba ta masar ta haɗe abarta,
Ta ba su kuɗi su
rarraba saura ribatarta,
Hakka suke ta zagaye ya zama sanna’arta,
Ke ɗin har da su bara ɗai ne kunka taka.
Wanni ko gun siyasa a can ya baje kolinsa,
Can ne cinsa har da sha can ne sanna’arsa,
Shi aikinsa media yai ta baje guminsa,
Yai ƙarya ta cin amana don jam’iyarsa,
Allah wadanka ka zamo kaicon al’umarka.
Wassu a kan waya suke turowa da saƙo,
Ko Facebook ko WhatsApp sun maishe su ƙoƙo,
Har lamba na bankuna modern ne a roƙo,
Wassu kiran waya kawai za su yi don su miƙo,
Sun kwaso matsaltsalu sun jibge wurinka.
Kuttuna da ɗai kan cikakken saurayi ne,
Ba ya sana’a, bai nema, aiki nai zaman ne,
Kai ka boƙare kana tashin faɗuwa ne,
Sai ya taho da ɗai kamar neman har da shi ne,
In kuma ka hana shi to zai yi fushi gare ka.
Wanni ko kamfani ko matatar haihuwa ce,
Mata nai guda kaza ‘ya’yan runduna ce,
Kai ko ka bi sannu don matar ma guda ce,
Sai ya taho da ƙorafin matsaloli ya kwance,
Kai ka ce gidan akwai fafewa na ƙwanka.
Ni ban ƙi na
taimako ware tsiro da gyauro,
‘Yan ƙarya cikin bara su nika ƙi da horo,
Sun saka mai ya ƙamface dambun ya yi tsoro,
Su suka sa a yau har marayu ba su moro,
Su ke cin rabon faƙirai kafin a farka.
Mun dai samu mattsala saura mui correction,
Dole mu janye duk silar kawo confusion,
Ba sukar aƙida ba condemnation,
Mur riƙi gaskiya hadisai muy yo
adhesion,
Kar da mu bar batu na gyara mu ɓuge da suka.
Roƙon nan ya sa mu duk fuskantar
derision,
To mu haɗe mu sa ƙaimi haiƙan gun
repulsion,
Sannu a hankali batun roƙo zai
corrosion,
Sai mun ɗauki
decision mun samar da vision,
Za mu zamo a tsaftace sak birni na Makka.
Abin nan ba ya yi sai da hannun itta government,
Su samar ayyukan yi su kawo development,
A kakkawo training a kawo improvement,
Don mun san talauci shi ne duk rudiment,
Sai tsarmin jahilci idan shi ma ya sirka.
Aikin malamai kira su ke faɗɗakarwa,
Ga nan dai hanin hadisai sui fassarawa,
Sa ‘yan media suna babin barbazawa,
Sai aikin iyaye tarbiyya kulawa,
Killace ‘yan ɗiya gida kalace a girka.
‘Yan gudun hijira a al’uma dole a taimake su,
Bala’i ne ya far musu to mu ji tausayinsu,
Amma sai a rarrabe kar a shige cikinsu,
Mu ware gurragurbi nan masu kiran sunansu,
Za ka ga sun marairaye zamba ce gareka.
Kowa al’uma rawa nai yai rausayawa,
A bayar taimako marayu su ai kulawa,
Zakka in ta zo a yo adalcin rabawa,
A samu tsaro ya mamaye noma ai kulawa,
Sai an tara hannuwa za a iya ma jinka.
Sannu a hankali a sa doka mai hanawa,
Sai an yo a sannu kar ay yo murƙushewa,
Kar a hana su walwala ba zaɓin riƙewa,
Sai an samu adilai gwamnati mai iyawa,
Don an ba mu arziki sun ka zamo hankaka.
‘Yan himman cikinmu Razza’u ka tallafe su,
Masu barar cikinmu kawo shiriya gare su,
Raunanan cikinmu hore mana taimakonsu,
Mahukuntanmu Ar-Rashid gyaro zuciyarsu,
Kai ke ba da arziki mun roƙa gare ka.
Tamat na gode Rabbana nan na doshi boda,
Kai ne Al-Laɗifu kai ne
ka saka na ida,
Ramzi SHATAMAHA za ka iya ka ƙida,
Mai son wa ya yo ku ce mai Abu-Ubaida,
Roƙona gare ku fatan samun albarka.
August, 2026
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.