Jagora:
Alhaji Magaji Galadiman mutan
Maitsidau,
Kowag gaji bai saba ba,
Uban Shamaki dogo mai salati,
Uban Sarkin Fada kasko,
Uban Musa mai doki,
Uban Jarmai Muzammilu,
Wai ba horo ba duna,
Uban Abdullahi Kurata babban p.a,
Ba horo ba ɗan marayan zaki,
Ya biya ni na gode ma,
Naji daɗi iri-iri".
☝️☝️☝️☝️☝️Daga cikin tamburan mai girma Magayaƙin Kano, Malam Magaji Galadima Abdullahi na Makaɗa Shagari ɗan Makaɗa Adhama ɗan Makaɗa Dagajirau ne.
Makaɗa Dagajirau yayi tarayyar kiɗa da waƙa da
Galadiman Maitsidau Abdullahi Maikano dake masarautar Kano. A gidansa yake
sauka idan aka zo bikin sallah a birni kuma yana binsa da kiɗa da 'yan tauri a wajen
hawan sallah.
Bayan gushewarsu ɗansa Makaɗa Adhama ya ci gaba da
biyar Galadiman Maitsidau Muhammadu Lawan wato ɗan
Galadima Abdullahi Maikano bayan wafatinsu a halin yanzu sai jikan Makaɗa Dagajirau wato Shagari ɗan Makaɗa Adhama ya ɗauki maigirma Magayaƙin
Kano Malam Magaji Abdullahi ɗan
Galadiman Maitsidau Muhammadu Lawan wato jikan Galadima Abdullahi Maikano a
matsayin ubangida domin ɗorewar
taren data faru fiye da shekaru 100 da suka gabata.
Tun zamanin Sarkin Kano Muhammadu
Abbas ɗan Sarki
Abdullahi maje Karofi ɗan
Sarki Malam Ibrahim Dabo wanda ya yi sarauta daga shekarar 1903 zuwa 1919 ya ƙafa
wata ƙungiyar
'yan sintiri da ake kira 'Yan-bata- kulki dake sintiri a cikin birnin Kano don
taimakawa ' yan gadi wajen tsabtace birni daga ɓata-gari.
'Yan -bata-kulki akasari 'yan tauri ne da hatsabibai daga ko'ina a ƙasar
Kano, shi Dagajirau ne ke yi masu kiɗa
don ƙara
tsima su. Irin wannan tarayya tana raya al'adu da adabin Hausa.
Dattaku da adalci da karimci da
amana da kyautatawa daga gefen uwayen gida ke saka Makaɗa da Mawaƙa riƙon wannan igiya yayin da haƙuri da
ƙana'a
da juriya da biyayyar Makaɗa
da Mawaƙa
zuwa ga iyayen gidansu ke matsayin sinidarin tabbatar da wanzuwar irin wannan
zamantakewa.
A masarautar Maradun ta Jihar
Zamfara Makaɗa Usman Ɗankwanaga
Ɗankadu
da 'ya'yansa Makaɗa
Abdu Kurna da Alh. Musa Ɗanƙwairo da jikokinsa Daudu Garba da Ciroma Abubakar da kuma
kamakunnensa Alh. Muhammadu Ɗanjuma Muhammadu Musa(Ɗanƙwairo
na yanzu) sun fake wannan tare da Sarakunan Maradun tun daga Sarkin Ƙaya
Ibrahim I har zuwa ga Sarki Abubakar /Bubakar da Sarki Muhammadu Bello Tambari
da Sarki Ibrahim Maigandi II har zuwa ga mai martaba Sarkin Ƙaya
Alh. Garba Muhammad Tambari MFR na yanzu.
An samu irin haka a masarautar
Yauri ta Jihar Kebbi inda tun daga mai martaba Sarkin Yauri Abdullahi Jibrin
Abarshi ya zuwa ga mai martaba Sarki Tukur Abdullahi da Sarki Shu'aibu Yakubu
Abarshi har zuwa ga mai martaba Sarki Dakta Muhammad Zayyanu Abdullahi na yanzu
zuriyar Makaɗa Aliyu Ɗandawo
Shuni wato ɗansa Sani
Aliyu Ɗandawo
da jikansa Makaɗa Alh.
Ibrahim Sani Aliyu Ɗandawo dake jagorancin ƙungiyar kiɗa
ta wannan gida a halin yanzu yana ci gaba da yauƙaƙa wannan tare da ta wanzu shekaru masu
dama da suka wuce.
A taimaka muna da ire-iren wannan
tare da muke tunanin idan aka farfaɗo
da ita sabgar kiɗa da
kaɗe-kaɗe da waƙe-waƙen
gargajiya na Hausa da ta shiga wani mawuyacin hali na iya samun sa'ida.
Mun samu tsarabar waƙa da
wasu muhimman bayanai ne daga taskar maigirma Magayaƙin Kano, Malam Magaji
Galadima Abdullahi. Allah SWT ya ƙara lafiya da nisan kwana mai albarka,
amin.
A wannan hoto maigirma Magayaƙin
Kano Malam Magaji Galadima Abdullahi ne.
Daga taskar:
Hon. Ibrahim Muhammad (Ɗanmadamin
Birnin Magaji) Jihar Zamfara, Nijeriya.
09/08/2026.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.