𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum mallam, shekarata goma sha hudu da aure da mijina amma baya kyautatamin kullum cikin fada da mita da kananun magana yake daga ni har yarana idan muka ganshi fargaba mukeji ya sa mana tsoronshi a rai, yana mana mulkin zalinci ba soyayya ba kulawa ba kyautatawa ko rashin lafiya nake yi baya kula dani haka harzan warke baya zama damu idan ya fita wani lokacin sai dare ko mun yi bacci zai dawo, a haka a haka duk naji ya fita min a rai, idan nayi kokarin samunshi muyi sulhu haka zai mayar da abun abun fada da tashin hankali a saidai ya dauko abinda yawuce shekara da shekaru yayi ta fada, ahaka mallam sha'awan saduwa dashi duk ya fita min a rai saboda duk abinda yakem in bai da lokacina sai idan zai sadu dani ba magana mai dadi ba farinciki idan yagama kuma zai ci gaba da rashin mutuncin dayakemin kamar ban taba masa rana ba sai kuma idan wani bukatar saduwan yakawoshi, mallam saboda haka duk saduwan auren ya fita min a rai inata addua dai ba dare ba rana, mallam shin inada laifi idan nima naki yarda dashi lokacin dayazo saduwan saboda duk ya ciremin sha'awanshi a raina, kuma da mallam ba haka nakeba ko rigarsa nagani sai hankalina yatashi bare idan naganshi da kudina nake biya group group nake shiga don nakoyi yadda ake gamsar da miji, kuma inayi shekara da shekaru amma duk ya fitarmin a rai saboda kuntatawa da rashin kyautatawa ya sa ko shekara zanyi ba miji bazai dameni ba, mallam har hakan ya sa ina mishi mummunar addua don dagani har yaranshi ba wanda yakejin dadinshi, don Allah atayani da addua kuma abani shawara sannan amin posting a group. Ni macece meson soyayya da kulawa amma dole haka na hakura bawai don banaso ba saidan bansamuba karfi da yaji yake nuna bazaiyiba inyi duk abinda zanyi, amma shi bazan samu daga wajenshi ba.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuh.
A addinin Musulunci, mijin
da ke zaluntar iyalinsa, baya kula da su, kuma ya hana su hakkinsu na soyayya,
tausayi, da kulawa, yana da laifi. Ya wajaba ya gyara halinsa, domin Manzon
Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce mafi alherin mutane shi ne wanda ya fi
kyautata wa iyalinsa kuma ni ne mafi alherin ku ga iyalina. Mijin da ke
kyautata wa matarsa da 'ya'yansa ta hanyar ciyarwa, da tausasawa, da sakin
fuska yana samun babban lada kuma rayuwar aurensu tana dorewa cikin farin ciki.
Allah ya haramta zalunci ga
kansa da kuma tsakanin bayinsa. Mijin da ke cutar da matarsa ta hanyar duka,
zagi, hana ta hakkinta na ciyarwa, ko kuntata mata yana da babban zunubi kuma
zai fuskanci hukunci a duniya da lahira.
Dole ne miji ya kula da
matarsa idan tana rashin lafiya kuma ya bata magani ko abinci. Allah ya umarci
maza da su zauna da matansu lafiya da kuma daidaito. Manzon Allah (Sallallahu
Alaihi Wasallam) ya umarci maza su kula da matansu su kuma kyautata musu. Bai
halatta miji ya rika wulakanta matarsa, jifanta da miyagun kalamai, ko nuna
mata halin ko-in-kula ba. Musulunci ya gina zaman aure a kan soyayya, jinkai,
da kuma kyautata wa juna.
Annabi (Sallallahu Alaihi Wa
Sallam) kafin ya bar duniya, kafin Allah ya ɗauki
rayuwarsa wasiyar da yake bayarwa ga Al'umman duniya masu Mata shi ne: "ku
tausayawa Matayen ku, ku zauna da su cikin aminci da amana, ku kyautatawa
rayuwar su kada ku kuntata musu" kuma Manzon Allah (Sallallahu alaihi
Wasallam) yana cewa: "dukkanku masu kiwo ne. kuma za'a tambayi kowannenku
dangane da kiwon da aka bashi".
Sha'awar mace tana farawa ne
daga yadda aka gina zuciyarta da soyayya ta gaskiya, yadda ake kyautata mata,
da kuma yadda ake nuna mata ƙauna
da kulawa a aikace da kalamai masu dadi, kafin a je ga saduwar gado. Idan babu
magana ta gari kuma akwai cin mutunci, jiki ba zai taɓa
bayar da haɗin kai ba. Mace tana bukatar kulawa da
kalaman nuna kauna don ta ji tana sha'awar mijinta.
Idan miji yana neman matarsa
ne kawai lokacin da yake bukata, hakan yana sa mace ta ji ana amfani da ita ne
kawai, ba wai ana kaunarta ba. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya
karfafa maza su kasance masu wasa da nishadantar da matansu, ba wai kawai su
neme su lokacin biyan bukata ba.
Ba laifi ba ne a shari'ar
Musulunci mace ta ki yarda da bukatan mijinta na saduwa idan har yana wulakanta
ta, baya kulawa da ita, kuma baya kyautata mata, musamman ma idan yana amfani
da ita ne kawai lokacin da yake da bukata ba tare da bata hakkin rayuwa da
kauna ba. Wajibi ne akan miji ya kyautata mata, ya ciyar da ita, da kuma bata
kulawa ta gari akowane lokaci, ba kawai lokacin da yake son biyan bukata ba.
Mijin da baya sauke hakkin matarsa na rayuwa ta gari zai iya sa matarsa ta ji
babu dadi, kuma rashin ba shi hadin kai a irin wannan yanayi bai zama zunubi ba
a gare ta, domin yana tauye mata nata hakkin.
A muslunci, ba a son mutum
ya yi mummunan addu'a ko tsinuwa ga kowa, har da wanda ya zalunce shi, domin
addu'ar wanda aka zalunta a kan azzalumi karbabbiya ce. Yazo acikin hadisi cewa
duk sanda wani yayi addu'a akan zaluncin da akayi masa, to Mala'iku sukan dauki
wannan addu'ar akan giza-gizai, kuma Allah yakan ce masa "lallai sai na
taimakeka koda bayan wani lokaci ne". Kuma Manzon Allah (Sallallahu Alaihi
Wasallam) ya gaya wa Sahabbai (Allah ya yarda dasu) cewa : "ku kiyayi
addu'ar wanda aka zalunta. domin hakika babu wani abinda ke kangewa tsakaninta
da Allah". Mafi alkhairi shi ne neman shiriyar Allah maimakon la'ana.
Ki nemi lokaci mai kyau
lokacin da kuke cikin natsuwa (ba lokacin da kuke fada ba). Ki fada masa yadda
kike ji ta hanyar amfani da kalamai soyayya da girmamwa, ki Bayyana masa cewa
kina son shi kuma kina son kusancinsa, amma rashin kulawar da yake baki yana
kashe miki gwiwa.
Idan kika gano cewa magana
dashi kai-tsaye ba za ta yi amfani ba ko kuma zai juyo miki da fada, zaki iya
neman babban mutum da yake girmamawa a cikin danginsa ko naki don a zauna a
fada masa gaskiya cikin hikima.
Ki Kula Da Kanki Da Kwarin
Gwiwarki, Kada kiyi kasa a gwiwa wurin kula da tsaftarki, kyawunki, da farin
cikin zuciyarki. Wani lokaci canza dabi'unki da rashin damuwa da halayensa na
iya sa ya fara tunanin me ke faruwa, har ya dawo yana neman kulawarki. Zaman
aure yana bukatar hakuri da juriya, amma kuma yana bukatar mutunta juna da
soyayya don rayuwar aurenku ta samu dorewa cikin farin ciki.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.